Showing 285001 words to 288000 words out of 322641 words

Chapter 96 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4324

komai, duk Abinda yafaru shine sila



yanzun ma saida yagaji da tsayuwa sannan yawuce wurin tent din daya zauna dazu yaciro waya don kiran Mussadiq.





------




shiru motar ta dauka kamar babu kowa ciki

tunda suka kamo hanya babu wanda yace uffan acikinsu

can batool ta sauke Ajiyar zuciya tadan saci kallon zee dake kallon waje ta window sannan tasake maida kallonta ga titi

"gaskiya Zainab Abinda kika yima gayen nan baki kyauta ba" inji batool


banza zee tayi ta kyaleta

"ko babu komai shi musulmi ne, yayi miki sallama kobazaki yimashi magana ba,atleast answer the salaam amma yayimiki,sallama ko kallonshi bakiyi ba"

Ajiyar zuciya zee tayi tana rolling idanunta
"wai batool meye damuwanki ne? ina ruwanki dana amsa sallamarshi ko ban amsa ba? what if na amsa acikin zuciyata? please batool kibar shiga wannan maganar idan ba sokike mu sa6a ba"

"Zainab ni gaskiya nake fadamiki, kome mutumin nan yayi miki be kamata kiyimashi wulaqanci ba, agaban fa mutane kikayi ignoring dinshi yana binki yana begging dinki amma ko kallo, haba?"

"ni nace ya tareni agaban mutane? duk Abinda nayimashi shiyaja, he even have guts dahar zai tareni, mema zai gayamin idan na saurareshi?"

"ki saurareshi tukunna mana, bakisan me yazo dashi ba, bakisan me zaice maki ba"

"kuma banason sani ok? please and please kifita harkata akan wannan batun batool, banason musamu misunderstanding akan hakan"


Ajiyar zuciya batool ta sauke ta cigaba da tuqinta batareda tasake tankawa zee ba


itama zee maida hankalinta tayi akan window ahaka har suka isa gida.



Washegari ma kamar jiya tana fitowa daga class bayan daukar wani lecture sai cin karo tayi dashi daga dan nesa da class dinsu


dauke kai tayi kamar bata ganshi ba tanufi hanyar fita daga wajen

binta shima yashiga yi yana mata magana da magiyar ta saurareshi not minding who and who is watching


kamar jiya ko kulashi batayi ba ta cigaba da tafiya tama rasa inda zata nufa


daga qarshe tayi hanyar class dinsu batool luckily anata suna ajin ana jiran lecturer yashigo hakan yasa itama fadawa class din tawuce wurin zaman batool ta xauna kusada ita

"kekuma fa? daga ina?"

Ajiyar zuciya zee tadan sauke
"class" ta amsa ataqaice

"to dakika shigo nan bakiga lecture zamuyi ba"

"babu damuwa, I'll take part too"


batool zatayi magana lecturer yashigo hakan yasa suka nutsu



lecture din ya daukesu almost an hour kafin sugama Inda duk Abinda akeyi hankalin zee ba wajen yake ba yayi nisa


bayan lecturer yafita students suma suka fara fita

tattare books dinta batool tayi tajuyo ta kalli zee taga hankalinta ma baya kusa kwata2

girgiza kafadarta tayi wanda hakan yasata yin firgigit ta kalleta

"lafiyar ki kuwa? tunanin me kike?"

Ajiyar zuciya zee tasauke sannan tahau waige waigen class din

"wai har angama lecture din?"

"A'a ke za'a jira, nidai tashi am hungry nasama ma cikina wani abu" inji batool tana miqewa


tashi itama tayi aqasan zuciyarta tana fatan karsu ga Deen idan sunfita

kallon agogonta tayi

awa daya kenan tasan yagaji yatafi ma

da wannan tunanin tafita


saidai me tana fita ta hangoshi qarqashin wata bishiya dake daga opposite din class din jingine ya zubama kofar ido


ganinta yasashi miqewa daga jinginar da yayi yana sakarmata murmushi


saurin kauda kai tayi ta sake rungume books dinta tawani hada rai tazo tawuce


nufota yayi hakan yasa tayi hanyar fita wajen da sauri

"Zainab... wait" yafada yana binta shima da Dan sauri


binsu da kallo batool tayi harsuka fita daga wajen sannan ta girgiza kai itama tafito tayi hanyar cafteria


cigaba da bin zee Deen yayi yana mata magana amma ko kallonshi batayi ba

tarasa Inda zata dosa kuma don zai iya binta duk Inda taje gashi suda wani lecture sai nan da 30mins


data gaji da bin dayake mata saita juyo afusace tana makamashi wani mugun kallo


ganin hakan yasa shima dakatawa yana kallonta

"meye damuwanka danine? wai who are you ma?" tafada afusace

"Zainab..."

"tambayarka nayi waye kai?"

"Kamal ne.. Kamal dinki"

wani kallo tayimashi

"Kamal din wa? as far as am concern banta6a sanin mai irin sunan nan ba"

"Zainab nasan kina tsananin fushi dani amma don allah ki saurareni even if sau daya ne please... nasan nasaki a qunci dayawa..."


"qunci? dawa dawa kasa a qunci? look at me up and down nayimaka kama damai wata damuwa?"


rasa Abinda zaice yayi don kwata2 she's not helping matters

"Zainab..."

"am Happy bakaga haka ba? ko bakaga alama ba? banada wata damuwa daidai da qwayar zarra, quncin me kake magana akai to?"


"Zainab..."

"look sunana yafita daga bakinka don ba'ayishi don kazo kana cikamun kunnena dashi ba, as far as am concern I don't know you, ban ta6a ganinka ba so please kabar bina kamar wadda kabaiwa Ajiyar kidney dinka, I have nothing to do with you ok? spare me please"

tana kaiwa nan ta juya

"Zainab! Zainab!!"


ina harta wuce


furzar da zazzafan huci yayi yana riqe waist dinshi

"this is serious" yafada ahankali



Ataqaice haka Deen yaita bibiyar zee a school cikin son ganin ta tausaya ko sau dayane ta saurareshi amma a banza don kwata2 qara botsarewa takeyi every passing minute


wani lokacin haka zaita binta yana mata magana taqi tankamashi yadda kasan da gini yake wani lokacin kuma tafada mashi baqa


saidai duk Abinda take mashi baya sarewa haka yake lallashin zuciyarshi yana cigaba da binta yana baiwa kanshi kwarin gwiwar cewa watarana zata saurareshi


kullum haka zaizo ya wuni a school din yana binta batareda gajiyawa ba

kwata2 baya damuwa da irin wulaqancin da zee kemashi don yasan he deserve it tunda shine sila

wannan karon yayi determine bazai sareba kamar yadda yasaba abaya, he's determine to show zee how far he can fight for her love


batool dai abin bayamata dadi kwata2

ita Deen bala'in tausayi yake bata musanmman idan taga yabiyo zee tana ignoring dinshi

akwai lokacin da taje tasameshi tace mashi ya kyaleta tunda bata saurararshi yabata space atleast qila tasauko amma saiyace mata karta damu shi Abinda takemashi baya damunshi cos he know he deserve it

haka dai ta kyalesu dole ta zubamasu ido

Mussadiq ma a 6angarenshi yana sane da duk Abinda ke faruwa saidai ya kyaleshi yana son gani how far he can go and he was amazed as how Deen yaqiyin ko gexau daga qudurinshi na shawo kan zee


Deen fa yakoma zee's chewing gum, duk Inda tayi yana biye saidai idan tana a class

tun tana mashi masifa harta kyaleshi takoma bata tankamashi ko shekara zaiyi yana zuba

sosai wannan taurin kan na Deen yabata mammaki

tasanshi very timid da saurin sarewa but this time around labarin na neman chanzawa

abubbuwan datake mashi ya isa ya haqura ya kyaleta koda itace autar mata amma ita gani tayima ko ajikinshi kamar ma bashi take mawa ba

haryanzu taqi bashi damar explaining kanshi shima kuma haryanzu beda niyyar haqura

wani lokacin cikin mutane zaita binta babu Abinda ya dameshi saidai ita taitajin kamar ta nutse

tagaji, tagaji sosai da wannan nacin na Deen hakan yasa watarana daya biyota yana mata magana tayi wata hanya

binta yayi yana cigaba dayimata magana har sukaxo wani wuri da babu mutane

juyowa tayi tana kallonshi hannaye riqeda kugu hakan yasa shima tsayawa yana kallonta


shiru yabiyo bayan haka suna kallon kallo

"gayamin me kakeso, mezanyi maka kabar bina kamar snail and it's shell?" ta tambaya a qule

murmushi keson kufcema Deen amma yayi saurin hadiyewa

"inason ki saurareni ne please"

"ok ina sauraronka meya faru?" tafada cikin qosawa

rasa ta ina zaifara yayi

"you have 2mins" tafada tana kallonshi

"Zainab it's about Abinda yafaru atsakaninmu ne, Don allah kiyi hqr ki gafarceni, nasan ban cancanci yafiyarki ba amma Don allah ki yafemin..."

"na yafemaka, shikenan?" ta katseshi da hakan


Dan buda idanunshi yayi

"d..dagaske?"

"dagaske, yanzu zan iya tafiya?"


cikin jindadin yafiyar datayi mashi yace
"oh thank you, nagode nagode sosai Zainab"

"it ok, now I'll get.going karka qara bibiyata kuma" tafada zata wuce


saurin tare gabanta yayi yace
"No please Zainab"

"meye kuma?!" tafada afusace

"O'O! please don't shout" yafada pleadingly


harara ta gallamashi jin ya ambaci sararshi

"Zainab I know Abinda zance yana iya 6ata miki rai amma kiyi hqr, please mukoma kamar da please, Zainab I still love you, wlh haryanzu my heart beats for you please.."

"how dare you?" tafada ahankali idanuwanta na kadawa

shiru yayi ganin reaction dinta

"how dare you say that to me?"

"Zainab am sorry but.. that's the pure truth, I love you Zainab, ban ta6a daina sonki ba kullum soyayyarki banda qara hauhawa babu Abinda takeyi a zuciyata"

"qarfin halinka ashe yawuce yadda na musalta?" tafada tana kallonshi sosai kamar da mammaki

"kiyi hqr zee, amma this is the truth... I love you... I still love you, I never stop loving you and I'll never stop"


Dan murmushi zee tayi
"wane irin love kake magana akai don ya kasu kashi kashi"

"true love zee, inamaki soyayya ta gaskiya"


"soyayya ta gaskiya, irin wanda kesa agudu abar heart breaking letter?"

lumshe idanu Deen yayi zuciyarshi na zafi

"Zainab..."

"ko irin wanda kesa a karya alqawari?"


"Zainab kiyi hqr"

"ni tambayarka nayi bacewa nayi kabani haquri ba" tafada hawaye na taruwa a idanunta

"wacce daga ciki kake nufi?"

"Zainab... nasan na yaudareki nakuma ci amanarki amma..." saikuma yarasa Abinda zaice


"yes? amma me?" tafada tana kallonshi hawayen idanunta na barazanar zuba


to her greatest surprise saitaga yafara yin qasa before she knew it yana kan knees dinshi

wara idanu tayi tareda kyafkyaftasu akanshi

"amma kiyi hqr zee, kiyi hqr... banida hujjar dazan kare kaina kona wanke kaina illa nabaki hqr"

"Deen meye haka kakeyi?" tafada tana dan jabaya

"kiyi hqr zee"


"ka tashi" tafada hawayenta nazubowa

"No zee, I can lay for you ma, nidai Kawai ki yafemin"

ganin zaiyi laying din yasata cikin tsawa tace
"stop!"

ganin be saurareta yasata qarasowa gabanshi dasauri itama ta zube a gwiwowinta tana tareshi

"I said stop!" tafada tana turashi baya

"nacemaka kayimin kneeling ko kayimin laying ne?" tafada cikin kuka

"I don't know what to do again Zainab" yafada idanunshi na kadawa sosai

"ni nace kaimin wani abu? you always make me cry, Ka qware wajen sani kuka, kanajin dadi kaga ina kuka ko?" tafada cikin kuka sosai

girgiza kai Deen yayi yana matsowa kusada ita

"A'a wlh, Zainab aduk duniya,babu Abinda na tsana sama da kukanki, I hate seeing you cry"

"amma kuma kake sani? duk wadancan daka sakani be isheka ba saika qara sani?" tafada cikin kuka sosai dama qiris take jira

"Zainab kiyi hqr, please forgive me, bansan yadda akayi nima nake saki kuka ba, I swear it's again my wish"

"against your wish? katafi kabarni Deen, shima against your wish ne?"

sunkuyar dakanshi yayi daidai da digar hawayenshi

"nasoka da dukkan zuciyata Deen, nabaka amana na yarda dakai na damqamaka amanar zuciyata as a whole amma kai mekayi? you broke it into pieces and throw it back at me!"

runtse idanunshi Deen yayi gam zuciyarshi na mugun zafi

"katafi kabarni Deen alokacin danafi buqatarka, ka kunyatani, you betrayed my trust for you!"

"am..sorry" yafada cikin rawar murya sosai


"katafi without even looking back for once, katafi kabarni without caring wane hali zan shiga... sau daya ko,sau daya,baka ta6a waiwayena ba"

rufe fuskarshi Deen yayi da taffukanshi zuciyarshi na wani irin zafi

"kuma shine yanzu zakace kana sona kuma? are you this cruel?" tafada tana kallonshi da jajjayen wet eyes dinshi

ahankali Deen ya janye taffukanshi daga fuskarshi datayi ja ga hawaye a cheeks dinshi

"Zainab nasan nasaki a qunci da baqinciki, nasan nayi breaking heart dinki amma wlh bada son raina bane nayi hakan kuma nima na azabtu don tun bayan rabuwarmu dake ban qara farinciki ba.."

"shiyasa har kayi moving on harka zama wani a duniya? while nikuma inanan nakasa gaba nakasa baya"

Dan lumshe idanu Deen yayi yabude yace
"Zainab duk Abinda nazama aduniya kece sila, kece silar sanina a duniyar nan da'akayi"

"katafi kabarni Deen batareda tunanin kadawo kaga halin daka barni,acikiba ko sau daya"

"Zainab nadawo, wlh nadawo... nakasa jure zama babu ke wlh adaddafe nayi three weeks nadawo amma...amma aka tareni da mummunan labarin daya girgiza zuciyata akace min wai...wai kinyi aure kinbar qasar"

dagowa zee tayi tana kallonshi da rinnanun idanunta

"ni?" tafada ahankali

"eh zee, fadin halin dana shiga aciki a lokacin baxai misaltuba, kusan haukacewa nayi, zee nayi kuka, nayi nadama nayi danasani kuma ina kanyi, wlh tun bayan rabuwarmu basake farinciki ba rayuwata bata sake tafiya daidai ba"

shiru Kawai Zainab tayi tana kallon yadda yake magana yana hawaye kallo daya zakamashi kasan da dukkan gaskiyarshi yake magana

"Zainab ki saurareni yau zan fadamiki komai, zan fadamiki silar komai"


shiru zee tayi tana kallonshi nawani lokaci sannan tace
"ina sauraronka"....✍?





*naso mugama Deen kafin babban sallah amma allah be yarda ba, anyimana haihuwa najiki sosai so baxan dinga samun damar posting ba don haka anan zan tsaya harsai bayan sallah idan allah yakai ranmu, allah yanunamana wucewarta lafiya🤲🏻*





Ummin Fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:45 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*










*091*






*Barka da sallah to you all, fatan anyi sallah cikin qoshin lfy, allah ya maimaita mana🤲🏻*









"it all started ranar damuke waya dake daddy dinki yayi banging in

naji komai.. naji duk fadan da daddy yayimiki da kalamanshi akan soyayyarmu..."






_*FLASHBACK*_



_"wato ke bakyajin magana ko? duk abinda nake gayamaki ta kunnen dama yake shiga yafita ta haggu ko? dama bakida hankali bansaniba?"_

_"ina nunamiki hanya kina rufe ido! kinje kina biyewa wancan dan iskan yaron ya huremaki kunne ya bushe maki idanu bakya ganin kowa da mutunci ko? eh!!"_

_"kullum kinacan banda qara liqemashi babu abinda kikeyi ko? and itama good for nothing uwarki babu abinda takeyi sai goyon bayanki ko?"_


cikin kuka sosai yajiyo muryar zee nacewa

_"don allah daddy kayi hqr wlh ina sonsh..."_


cikin ihu sosai yaji daddy ya katseta da

_"will you shut that your dirty mouth up! are you stupid! ina yimaki magana kina min zancen banza zancen wofi?!"_

_"harni zaki fadawa soyayya? ni zaki fadawa kina sonshi! soyayyar banza soyayyar wofi! soyayyar dakike mashi yakai wacce nakemaki koko soyayyar dayake miki takai wacce nakemaki? wato ni kuka maida shashasha ashe? ni inacan ina haukana ku kunacan kuna abinda kukaga dama babu abinda ya dameku.. am disappointed in you Zainab, very disappointed"_


kitt... Deen ya katse kiran don jiyayi bazai iya cigaba da saurare ba


sosai jikinshi yayi sanyi musanmman idan yatuno sautin kukan zee dayake jiyowa qasa qasa

tashi yayi daga kishingiden dayake kan katifarshi ya zauna ya jingina da bango


sosai zuciyarshi ta quntata ga wani d'aci d'acin dayakeji a maqoshinshi

haka ya zauna shiru na wani lokaci ya kafe wuri guda da ido


besan iya lokacin daya dauka ba ahakan sai jiyayi haske ya dallomashi fuska sanadin yaye labulen dakinshi da akayi

dagowa yayi ya kalli kofar yaga kakace

"wai kyakyawana kwana biyun nan meke 6oyeka a daki? saikazo kashige kayi shiru kamar wata amaryar qauye, badai bakajin dadi bane kake 6oyemin?" inji kaka tana qarasowa

gyara zamanshi yayi yana kokarin gyara yanayin fuskarshi

"A'a kaka Kawai nagaji ne shiyasa nashigo nadan kwanta"

"Ka kwanta? kwanciyar lafiya yanzu bayan la'asar? maza tashi to kaje can shagon Abba ka qaromana barkono don naga wancan be isa kaga zaka dan warware ma idan kadanyi tafiya amma idan ka kwanta yanzu ai kasan abinda zaka jawowa kanka" tafada tana kwance ha6ar zanenta

"to" ya fada yana qoqarin tashi


kudin tabashi tana fadamashi abubbuwan dazai siyo sannan tarakoshi har tsakar gida saida taga fitarshi sannan takoma


ahankali yake tafiya a layin nasu hannayenshi zube a aljihunshi kanshi asunkuye

idan ka kalleshi saikayi tunanin tafiyar qasaita yakeyi yayinda kwata2 ba haka bane damuwar dake ranshi ma ta isheshi


shagon Abba din yaje inda ya iske jira sosai hakan yasa yanemi wuri a dan bencin dake waje ya zauna don jiran jama'ar su rage


harde hannayenshi yayi a qirji ya kafe waje guda da ido ya lula duniyar tunani


besan adadin lokacin daya dauka ba ahakan sai jiyayi an dan girgizamashi kafada

saurin dagowa yayi ya kalli mai girgizamashi kafadar sai yaga ashe Abban ne

"yadai kyakyawan kaka? kaxo ka zauna nan shiru tundazu sai magana nakemaka bakaji, halan dai ba magana kaje ka janyowa kaka ba" inji Abba cikin tsokana don shima tsarar Deen ne don ko zai girmeshi baxai bashi shekaru masu yawa ba


murmushi Kawai Deen yayi yace
"siyayya nazoyi naga shagon acike shiyasa nace bari najira"

"waya gayamaka ana komawa gefe azauna ajira shago yarage? sai kaga wadanda suka zo daga bayanka ma,sun rigaka tafiya, irin haka ai magana zakayi saina baka ma batareda kajira ba tunda duk yarane masu sayayyar amma kazo ka zauna anan salan kaja kaka taji shiru tafito ta tattaro yan unguwa zuwa shagona nemanka" ya qarashe cikin tsokana

murmushi Deen yasakeyi sannan yace
"barkono zaka bani da maggi"


"na nawa?" inji Abba yana,komawa shagon da yanzu babu kowa ciki Deen na biye dashi


saida Deen yagama siyayyarshi tsaf sannan yabiya yajuyo yakamo hanyar gida


daga nesa ya hangi wata dalleliyar mota kofar gidansu

ahankali yake tafiya idanunshi akan motar yana wondering ta wanene

be gama zancen zucinshi ba yaga anfito daga gidansu

gabanshi ne yafadi lokacin da sukayi ido hudu da daddy

wani matsiyacin kallo daddyn ya jefeshi dashi sannan yayi gaba fuuu mutumin dake taredashi na maramashi baya yana yi yana waigen Deen dayayi tsaye yakasa qarasowa


wannan motar yaga sun nufa sun bubbude kofoffin gidan gaba sun shiga sannan aka tada motar suka bar wajen atsiyace


bin motar Deen yayi da kallo harta bar layin

gabanshi ne yacigaba da faduwa

meya kawo daddy gidansu?

tunawa yayi da magangganunshi na dazu dayaji ta waya hakan yasa zuciyarshi taqara tsinkewa

koma me yakawoshi ya tabbata ba alhairi bane duba da matsiyacin kallon daya jefeshi dashi

ahankali kamar marar lakka yaja qafaffunshi yanufi kofar gidan nasu cikin fargabar abinda zai tarar aciki


da sallama yashiga ciki amma shiru hakan yasashi ida qarasawa cikin gidan inda ya hango kaka zaune kan sabuwar tabarmarta ta buga tagumi kanta a sunkuye


ahankali yasakeyin sallama yana qarasowa yana kallon kakar tashi wadda harlokacin bata dagoba bare ta amsa sallamar tashi

saida ya qara kusantota sannan ya lura da dami damin kudadden dake gabanta yan dari biyar biyar sunkai wajen wrapper biyar hakan yasashi dan wara idanu yana kallonsu shima

"kaka?" yafada yana qarasowa

"kaka meye wadannan?" yafada yana kallon kudadden

sai a lokacin kaka tadago ta kalleshi

"idanuwanka sunfara ciwone? kudaddene, kudadden daka siyar da mutuncinmu akai"

kallon rashin fahimta Deen yayimata
"bangane ba kaka"

"tayaya za'ayi kagane Kamal? tayaya? bayan baka dauki maganata abakin komai ba baka yarda da,hangen danake maka ba" tafada cikin qunar zuciya

"kaka..."

"Tunfarko saida nagayamaka yarinyarnan ba sa'arka bace, tafi qarfinka amma ka nunamin kafini sanin abinda duniya keciki, to gashinan... gashinan ubanta yazo har gida ya taddani har nan yayimin wankin babban bargo babu abinda ya manta be gayaminba, ga Kuma kudi nan ya ajiye yace akyalemashi yarshi yariga yayimata miji, yanzu Kamal abinda zakamin kenan? ina zaman zamana? ina rayuwata cikin rufin asiri da kwanciyar hankali zakaje kasiyomin tashin hankali da kudinka? da mutunci na da komai wadannan mutanen sukazo sukayimin tass suka zubemin wadannan tsinnanun kudadden niga matsiyaciya? yayi maka kyau" ta qarashe tana miqewa tsaye tana share hawayenta


tunda tafara yaji kamar an zaremashi dukkanin lakka ajiki yakasa koda kwakwarar motsi

nuna kudadden kaka tayi cikin muryar kuka tace
"gasunan ka kwashesu don dama kai suka kawomawa, sunce dama abinda kakeso,kenan ba diyarsu ba


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login