Showing 147001 words to 150000 words out of 322641 words

Chapter 50 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4306

kar ayi abinda baza'azo ana regretting nan gaba ba.

Shi aure babban al'amari ne idan babu sanyawar albarka daga daya daga cikin iyayen both macen da namijin abin na iya juyewa yazama something else don haka Kiyi hqr kiyita addu'a idan kamal dinne mafi alhairi a wurinki to allah ya ganar da daddy idan kuma bashi bane allah ya za6a maki Mafi alhairi, insha allah zaki samu mai sonki sosai wanda zai Mafi kamal din sonki"

Tashin hankali!!


Kuka zee tafashe dashi sai gata on her knees

"Mummy please, karki ce haka. Ke kadai ce last hope dina please karki karaya, karki karya min gwiwa please.
Wlh Deen shine Mafi alhairi gareni please don't say that"


Sakin baki mummy tayi ganin yadda ta rude lokaci guda

"meye haka Zainab?" tafada a mammakince

"mummy don Allah karki bar bayana, please... We can do it, we can convince daddy, don Allah karki ce na haqura da Deen, bazan iya ba" saikuma ta zauna ta Hade kanta da gwiwa ta cigaba dayin kuka, idan mummy ta bar bayanta ya zatayi? She's her last hope.


"haba Zainab, saboda namiji zaki zauna kina irin wannan abin kina kuka? Inji dai bake ke forcing kanki agareshi ba?"

Dagowa zee tayi fuska sha6e2 da hawaye

"mummy wlh A'a, shima yana sona, bani ke cusa kaina ba, he loves me more than I do to him"

"then sai Kiyi hqr ki tsaya kiga yadda allah zaiyi daku, idan da rabon ku mallaki junanku zakuyi Hakan idan kuma babu babu yadda kuka iya dole ku hqr da juna.

Shi musulmin qwarai da tawakkali aka sanshi da kuma daukar qaddara"


Kasa cewa komai tayi sai cigaba da sobbing datayi

"kije ki cigaba da addu'ar za6i na alhairi don kuka won't change anything da yanayi da mutane da dama bazaki gansu da damuwar komai ba.

So is better ki riqe du'as don shikadai zai taimakeki nima zan tayaki kuma zan sake yimashi magana nima bawai na karaya bane kawai dai sonake na fahimtar dake ba kowanne abu da ka qwallafawa rai kake samu ba, kinji ko?"


Kada kai kawai tayi ahankali cikin matsar hawaye

"Good, yanzu tashi ki tafi and wipe your tears don basuda amfani, what matters most is du'a"

Qara Kada mata kai tayi sannan tashare hawayenta ta tashi tana jin kamar jiri zai kwasheta


"Don't worry kinji zan sake mashi magana insha allah zai fahimta" tafada cikin son qara kwantar mata da hankali

Qara kadamata kai zee tayi sannan tayi mata sallama ta fita

Binta da kallo mummy tayi cikin tausayawa saikuma ta girgiza kai ahankali ta cigaba da abinda takeyi.



Tana shiga dakin tayi wajen gadonta da gudu ta fada akai.


Sauran kukan da bata ida a dakin Mummy ba ta cigaba dayi

Jitayi kamar ta riga ta rasa Deen din ma

Wannan wane irin abu ne? Ko kadan bata ta6a kawoma ranta zata samu matsala irin wannan a soyayyarsu ba


Tariga ta dogara da maganar daddy na bazai mata dole ba duk wanda takawo zai kar6a hannu bibbiyu, bata ta6a tunanin banda talaka ba ko dayake ita kanta idan aka gayamata zata so talaka a lokacin qaryatawa zatayi, kawai lokaci daya ta makance a soyayyarshi makantar da bata tunanin zata ta6a bude ido nan kusa.


Aunty Feenah ce tafado mata arai, sotake ta kirata ta gayamata komai ko zataji sauqin abinda takeji ko kuma tabata shawarwaru kamar yadda tasaba

Amma saita tuna basama qasar, tun bayan wata daya da auren suka shilla honeymoon gashi batada number ta tacan kuma Koda tanada ita bekamata ta kirata ba a irin wannan lokacin ba, be kamata ta takura masu ba Suna tsaka da cin amarcinsu.


Ringing din wayarta ya katse ta daga tunane tunanen datakeyi

Wani sanyi taji a zuciyarta tun kafin ma ta duba mai kiran.

Ganin zata tsinke yasata saurin dauka ta daga kiran ta kara phone din a kunne bayan tayi iya qoqarinta na gyara yanayin ta don batason ya fuskanci halin datake ciki ko kadan batason ta saremashi gwiwa shima.


Saida suka gaisa sannan Deen cikin zumudi yashiga gayama zee yadda sukayi da kaka da amincewarta 💯 harda qarin maggi da gishiri a labarin don yaqara bada armashi.


Nan take zee taji duk damuwar ta ta yaye itama tashiga murna


Sun dade suna firarsu kamar basuda wani problem a rayuwa sannan suka rabu dakyar ba don sun so ba sai don barcin daya addabi idanun kowannensu


Sallama sukayiwa juna akan sai gobe idan sun hade a makaranta sannan suka katse kiran kowanne zuciyarshi wasai


Babu dadewa duk barci ya kwashesu mai cike da mafarkan juna






Kingin ranakun dasuka biyo baya sunzo very smoothly for the two lovers


Kwata2 sun manta da damuwarsu sun dauki damuwarsu sun ajiyeta a gefe sun cigaba da gudanar da soyayyarsu tsabtataciyar cikin salo na burgewa da ban sha'awa.


Soyayya suke bugawa wacce tafi ma tada, irin soyayyar nan mai tsayawa a rai kamar zane akan dutse wanda baya ta6a goguwa.


Basuda damuwar komai idan ma suna da ita to qila sun manta da ita don kwata2 basama kawota a jadawalinsu sam, rayuwarsu sukeyi kamar dama subiyu ke a duniyar basa tunawa da komai da kowa.



A bangaren iyayen kau abin dai babu yabo ba fallasa za'ace, haryanzu daddy shiru yayima biris da zancen Haka ma mummy bata qara tada zancen ba

Kaka ma ba laifi amma bawai ida Sakin jiki tayiba da wannan relationship din nasu ba don haryanzu hankalinta be ida kwanciya dashi ba

Taso ace Deen yasamo daidai shi ko don kaucewa matsala anan gaba, matsalar da basusan iyakar ta ba Amma ganin yadda Deen ya saki jikinshi dakuma yadda yake nuna tsananin qauna akan Hakan yasata 6oye damuwar ta ta cigaba da binsu da addu'ar za6i na alhairi.



Everything was going smoothly kwatsam wata rana zee na Kwance daki waya a kunnenta taji an banko kofa anshigo a fusace.


Saurin juyowa tayi cikin mammaki sai ganin daddy tayi kamar an jefoshi dakin sai suraci yake.


Saurin tashi zaune tayi zumbur batareda tama tuna Da katse kiran dasukeyi ba.


"daddy?" tafada ahankali tana kallonshi da kuma mummy datake bayanshi daga bakin kofa


Da yatsa daddy ya nuna zee

"wato ke bakya jin magana ko? Duk abinda nake gayamaki ta kunnen dama yake shiga yafita na haggu ko?

Dama bakida hankali bansaniba?! Ina nunamaki hanya kina rufe ido!

Kinje kina biyewa wancan dan iskan yaron ya huremaki kunne ya bushe maki idanu bakya ganin kowa da mutunci ko?!! Eh!

Kullum kinacan banda qara liqemashi babu abinda kikeyi ko? And itama Good for nothing uwarki babu abinda takeyi sai goyon bayan ki ko?!!"


Sosai zee ke kuka ganin yadda daddy ya burkuce mata sai tsawa yake mata abinda be ta6a ba

"daddy don Allah kayi hqr wlh ina sonsh.."

"will you shut that your dirty mouth up! Are you stupid! Ina maki magana kina yimin zancen banza zancen wofi!!"


Yadda ya hayyayaqomata kamar zai maketa yasata saurin yin baya ta zauna kan gado tana shigewa jikin frame din gadon tana wani irin kuka cike da tashin hankali.


"harni zaki fadawa soyayya?! Ni zaki fadawa kina sonshi! Soyayyar banza soyayyar wofi?! Soyayyar dakike mashi yakai wacce nake maki ne! Soyayyar da yake maki takai kwatar wanda nake miki?!
Wato ni kuka maida shashasha ma ashe, ni inacan ina haukana ku kunacan kuna abinda kuka ga dama babu abinda ya dameku"


"am disappointed in you Zainab, very disappointed.

A tunanina Koda ban kawo maki hujjar komai ba na hanaki kula wannan yaron haka kawai zaki rabu dashi ko don farincikina kamar yadda nasha sadauqarda farincikina saboda naki.

Amma da hujjata da komai kuma duk abinda nakeyi akanki nakeyi don kar rayuwarki ta tagayyara amma shine zaki debo qasa ki 6ullamin a idanu, kin mance da soyayyar danake miki kin manta da qaunar danake miki kin fita harkata duk saboda wannan kwadayayyan yaron, duk saboda dadin bakin dayayi miki ko!!"

Kada kai yayi yana murmushin takaici
"to wlh bazai yiwuba, zan dauki mataki, mummuna kuwa akanshi, tunda nabishi ta girma da arziqi bejiba, I'll have to show him my true colour, don haka daga yau karki qara fita daga gidannan kije koina, ko school na hana, zanyi maganinku ne wlh, shashashan banza!!"

Yana kaiwa nan ya kada babbar rigarshi ya fice daga dakin kamar zai tashi sama itama mummy ba don tayi saurin matsawa ba da yayi gaba daita.


Bin bayanshi mummy tayi da kallo harya fita yamaido masu kofar da qarfi.

Maida kallonta tayi kan zee dake takure akan gadon haryanzu tanata kuka kamar zata shide


Ajiyar zuciya ta sauke cikin rashin sanin abin yi sannan itama ta nufi kofa ta bude ta fita


Qara fashewa da wani kukan tayi tana Hade kanta da gwiwa, sosai takejin wani zafi na ratsa kowanne lungu da saqon zuciyarta tana jin yadda take fidda hucin zafi.


Zamewa tayi ta kwanta tana cigaba da kukan da tasan shi zai sata jin sauqin abinda takeji a zuciyarta.



Bata san iya tsawon lokacin data dauka ahaka ba sai jitayi anfara kiraye kirayen sallar magrib


Dakyar tasamu ta tashi tayi alwala ta gabatar da sallar

Tana nan zaune aka fara kiraye kirayen isha'i nan ma ta tashi ta kawota tayi addu'o'i sosai akan allah yakawo masu mafita sannan ta tashi ta koma kan gado ta kwanta tana jin yadda kanta ke saramata.


Duk yadda taso yin barci kasawa tayi don kwata2 barcin ya qauracewa idanunta ga wani irin ciwo da kanta ke mata na kukan datasha.


Wayarta ta laluba ta kunna sai taga duration din wayar dasukayi da Deen ke samar screen din wayar.


Lissafi tayi da lokacin dasuke wayar da lokacin da daddy yashigo saita ga ashe ma bata katse kiran ba bayan shigowarshi, Saida aka qara 10mins kafin kiran ya tsinke wanda cikin dayan biyu ne, ko shi ya katse ko kuma kudinta ne suka qare, idan haka ne that means yaji duk yadda sukayi da daddy?


Rasa mai bata amsar tayi sai kawai ta dannama number shi kira Saidai tun kafin aje ko ina taji ana cewa number datake kira bata shiga

Qara bugawa tayi bayan wancan ya katse nan ma amsa daya ce, the number is not reachable.

Kashe wayar gabadaya tayi ta tura qarqashin pillow ta koma ta kwanta tana cigaba da kukan zuci.

Wannan wane irin abu ne da maimakon yaci baya sai qara cigaba yake?


She can't believe yau ita daddy ya tsaya yayi ma tass haka, kuma ta tabbata da ta tsaya jayyaya dashi babu abinda zai hana ya wanka mata mari saboda yanayinshi kawai ya nuna yakai maqurar qurewa a 6acin ranshi

Sosai fadanshi da barazanar shi na daukan mummunan mataki akan Deen ya tsaya mata arai, Hakan yasa bata wani samu isashen barci ba a ranar duk rabi da rabi tayi kuma marassa dadi.



Washegari ta tashi da zazza6i, yau lahadi babu school gashi ta tashi da menstrual cramps wanda ke nuna alamun zata samu menstrual flow dinta a kowanne lokaci.


Bayan ta samu tayi sallar asuba dakyar takoma kan gado ta kwanta ba don tana jin barci ba sai don she's too weak har a lokacin.


Ta dade ahaka lamo kan gado can taji an bude kofar dakinta an shigo.

Batasan ko wanene ba kuma bata bude idanu ba don ganin waye


Jitayi anzo bakin gadon ta kuma ji alamun zama bisa bedside locker din wajen

Dumin hannu taji a wuyanta Hakan yasa ta sauke Ajiyar zuciya ta bude gajiyayyun idanunta tana kallon mummy dake ta6a wuyanta

"Are you sick?" inji mummy tana qara feeling temperature dinta


Lumshe idanu kawai zee tayi batareda tace komai ba


"tashi muje kici abinci kisha magani"

Yamutsa fuska tayi zatayi magana mummy ta girgiza mata kai alamun karta fara saikuma taqara cewa
"tashi mutafi"


Babu yadda ta iya haka ta tashi dakyar tanajin kamar taita kuka.

Saida tafara yin brush sannan ta dawo ta zauna don daga baya ma sama aka kawomata abincin.


Ta danci da dan yawa bisa takurawar mummy sannan tabata maggunguna tasha harda na period dinta saboda ta mata complain din ciwon cikin.


Saida ta shanyesu duka sannan takoma ta kwanta tana jin yadda kanta har lokacin ke harbawa


Bata dade da kwanciyar ba barcin da bata samu yiba tun jiya ya dauketa.




Lokacin da ta tashi har menstrual flow dinta yazo Hakan yasa ta tashi ta shige toilet don babu laifi tadan ji qarfi qarfin jikinta tayi wanka tayi packaging kanta sosai sannan ta dawo ta zauna gefen gado.


Wayarta dake kashe tun jiya ta lalubo ta kunnata tashiga call log taqara buga number shi Saidai this time around sai sukace tana switch off.

Komawa tayi ta jingina da frame din gadon ta lumshe idanu tana jin daci a ranta, this is the toughest time in her life.


Aranar ko kofar dakinta bata fita ba abinci Saidai a biyo ta dashi daki kuma dole taci don mummy ke tsareta sai taci.


Har dare number Deen bata shiga abinda be ta6a faruwa ba hakan yasa taji hankalinta yaqi kwanciya babu abinda ke fadomata arai sai kalmar daddy na saiya dauki mataki akai mummuna, Hakan ba qaramin samata fargaba yakeba a zuciya




A daddafe dai tasamu gari ya waye.

Tunda wuri tayi shiri don babban burinta shine taje ta ganshi a school ta tabbatar da lafiyarshi don jiya dashi ta kwana a ranta

Saidai me Koda ta sauko saita nemi bala ta rasa Koda ta tambayi security sai cewa yayi be isoba har lokacin


Komawa cikin gida tayi ta zauna a falo tashiga neman number bala amma bata shiga, tafi awa nan tana zaman jira amma shiru gashi ita bata iya driving ba.


Ganin abin na neman zama rainin hankali sai ta tashi ta sake fita da niyyar samun adaidaita kawai tayi tafiyarta

Saidai me firr security yaqi bude mata gidan wai daddy yabashi umarnin kar yabari ta fita.


Sosai abin ya quleta Hakan yasa tashiga zazzaga mashi bala'i akan ya bude mata gidan tafita gidan na ubanshi ne?

Saidai dik masifarta da hayaniyarta ko gezau securityn beyiba dama ta dameshi saiya shige dan dakinshi ya rufo kofa.


Juyawa itama zee tayi tashiga cikin tana kuka sosai, Direct dakin Mummy ta nufa taje ta tardata tana yan lissafe lissafenta


Fadawa tayi jikinta tana kuka sosai tana roqonta tazo tasa security ya bude mata gida


Ajiyar zuciya mummy tayi tace
"Zainab, bakiji abinda daddyn naki yace bane? Cewa yayi bazaki qara fita daga gidan nan ba Koda kuwa school zaki, Kiyi hqr kawai harya sauko"


Kuka zee ta cigaba dayi
"mummy am scared, tun shekaranjiya number Deen bata shiga, kar ace daddy yayi mashi wani abin"


"babu abinda zaiyi mashi insha allah, kawai shawarar dazan baki yanzu itace kibar batun Deen for now, muddin kinason zaman lfy don daddynki ya dauki abin da zafi fiyeda tunaninki"


Da wannan kalmar zee ta tashi ta koma dakinta ta kwanta ta tattakure waje daya kamar marainiya.


Tun daga ranar farinciki ya kaura a rayuwar Zainab, tun tana attempting fita daga gidan ana hanata har ta haqura ta bar ma fitowa kwata2 daga dakinta.

Kullum yini take cikin dakinta tana kuka babu abinda yafi daga mata hankali kamar jin Deen shiru har lokacin, yanzu sati daya kenan da faruwar Hakan amma haryanzu number shi is switch off, sosai Hakan ke daga mata hankali.


Cikin wannan kwanakin sai gashi tayi wata ramar dole, sai acikin kwanakin taqara tabbatar da bazata iya rayuwa batare dashi ba don ita kadai tasan yadda takeji a yan kwanakinnan da bata sanyashi a ido ba kuma bataji muryashi ba.



Ana haka ranar data cika kwana goma da faruwar komai tana zaune waya a hannunta ta lalubo number Deen ta tsaya ta kuramata idanu kawai tana kallo

Kamar da wasa ta dannama number kira batareda sa ran zata shiga ba

Kamar a mafarki kawai sai taji tafara ringing


Wara idanunta tayi cikin mammaki bugun zuciyarta na qara gudu


Saidai harta tsinke ba'a daga ba


Hannu na rawa taqara bugawa tana miqewa tana jin kamar zuciyarta zata tsinke saboda bugawar datake


Saida ta jera kira uku, ata hudun ne taji an daga


Kasa cewa komai tayi sai rarraba idanun datake zuciyarta na mugun gudu

"Zainab..." cool voice dinshi ta ratsa kunnenta


Rufe bakinta tayi da tafin hannunta takoma ta zauna bisa gadon da6as


"Hello? Zainab?" tasake jin Muryarshi nacewa Hakan


Hawayene suka shiga taruwa a idanunta still takasa cewa komai
"Zainab is this you? Please say something"

Lumshe idanu tayi tana ba hawayen idanunta damar gangarowa

"Deeen..." Sai kuma tashiga yin sheshekan kukan da batasan yazo mata ba


"Zainab, are you crying? Please kibari kinji? Kar zuciyata ta buga, am ok kinji" taji yafada shima a cikin wani irin murya mai matuqar rauni


"Deen ina ka shiga? Nakusan mutuwa saboda fargaba, meya faru da wayarka?" tafada cikin kuka


"am ok zee, babu abinda yasameta kawai babu charge ne" yafada cikin son kwantar mata da hankali

Girgiza kai tayi
"No Deen, you're not ok, gayamin meya faru me daddy yayi maka"


"babu komai Zainab, babu abinda yayi min, I love you and I'll never back off, no matter w..."

Sai kuma taji shiru


"hello? Hello! Deen! Kana jina?" tafada tana sake miqewa hankali tashe


"eh yana jinki, mallama me kuma kike nema da jika na? Me kuma yasaki nemanshi?"


Baki na rawa zee tace
"k.. Kaka?"


"eh nice, kaka ce. Nagode ma allah da kika gane Hakan, meye kuma kike nemanshi bayan duk abinda kukai mashi? Eh!"

Kasa cewa komai tayi sai bakinta dake rawa amma takasa furta komai

"to ahir dinki wlh, karki qara kiran yarona a waya, kifita harkar shi wlh don shima yariga ya gama dake dama ai qarfin hali ne irin nashi banda Hakan ai ke ba kalar matar dazai aura bace.."


Muryar Deen taji daka can baya yana kiran sunan kaka

Muryar kaka taji tana cigaba da cewa
"menene? Menene kake hanani magana? Kabari nayi mata wonin

Kina jina? Wlh ki fita harkar jikana kina jina ko? Mu ba kowan kowa bane bamuda wadanda zasu tsaya mana idan kika jefamu a chakwakiya, muna zamanmu ne cikin rufin asirinmu da wadatar zuciya, muna zamanmu cikin farinciki don Allah karki tarwatsa mana shi, don Allah ki kyalemin yaro kije kema allah ya hada ki daidai ku masu kudi muma haka, mun gode


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login