Showing 246001 words to 249000 words out of 322641 words
Chapter 83 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
da lagudar fuskar tana iya 6ata kwalliyar ma takoma wani abin daban hakan yasa ta miqe tsaye tana gyara rolling din veil dinta ta dauki turare taqara dan fesawa sannan ta kwashi wayoyinta tanufi hanyar fita tana qoqarin ganin ta saita bugun zuciyarta
***
qara wara manyan idanunta tayi in outmost shock zuciyarta na mugun bugu
kusanci sosai ke tsakaninsu don hannayenta data dafa qirjinshi dasu ya hana jikinsu hadewa waje daya
huramata iskar bakinshi mai qamshin mint yayi yana qara daga mata gira daya
"da ina zaki?" yafada cikin muryar rad'a
qoqarin tashi tafarayi tanajin yadda inner jikinta ke rawa
hanata tashin yayi ta hanyar zagaya hannunshi ta bayanta ya ruqota wanda hakan ba qaramin jan lantarkin jikinta yayi ba
agigice zee tace
"innalillahi, wh..what are you doing" tafada tana qoqarin tashi again
"am showing you how crazy I am, you called me psycho, don't you?" yafada still cikin rad'a yana kusanto fuskarshi ga tata
jabaya tayi tana qara tareshi da taffukan hannayenta dake kan qirjinshi
"m..mussadiq stop, wai meye haka? a..are you in your right sense?" tafada cikin rawar murya zuciyarta kamar zata faso qirjinta tafito
"no.. ni zarrare ne, koba haka kikace ba?"
"Mussadiq.."
"kince number Dr ya kamata na nema don mu gana shine nazo kibani"
"Mussadiq zanmaka ihu, I swear" tafada muryarta na rawa, sosai tsoro ya bayyana a fuskarta
wani guntun murmushi ya su6ucemashi sannan yaqara matso da fuskarshi dab da tata
"hakan ma zaifi qayyatarwa, azo aganmu ahaka" yafada still cikin rad'a qamshin bakinshi sai shigarmata hanci yake saboda kusancinsu
hankalin zee ne yaqara tashi, iya rudewa ta rude, ga yadda tunanin wani yazo yagansu ahakan yaqara hautsinamata yan ciki
dama haka Mussadiq yake, she know he's crazy amma batasan Abin nashi yakai har hakaba
"Mussadiq let me go.. this is wrong, you know it" tafada cikin muryarta data kasa daidaitawa
tunda take bata ta6a samun irin wannan kusancin da namiji ba
dukda ba bisashi tafado ba saidai suna daff sosai don taffukan hannunta data tare qirjinshi dasu ya hanata ida fadawa kanshi wanda shine kadai contact din jikinta da nashi sai kuma hannunshi dayasa ya tareta abaya don hanata tashi
ganin beda niyyar yin yadda tace din yasata dan rintse idanunta ta bude sannan cikin ahankali tace
"please.."
nanma shiru yayi sai kallo daya kafe fuskarta dashi
"you're not my muhharam Mussadiq, this is totally wrong, please let me go" tasake fada tanajin kamar ta fizge kanta saidai tasan any slight struggle zaisa taqare ajikinshi abinda Kuma bataso kenan
"sai kin maimaita Abinda kika fada ranar"
"Mussadiq.."
"nine zarrare ko?"
saurin girgiza kai tayi
"ni kika katsewa kira?"
"no, I.."
"maimaita Abinda kika fada aqarshe, mema kikace?"
"m..mussadiq wannan duk ya wuce.. I... kabarni natashi tukkuna please"
"yadda zaki gudu ko? answer me, ni kika katsewa kira? kinsan hakan meyake nufi agareni?"
tunda yafara magana take girgiza kai, ita kadai tasan yadda takeji
qara matso da fuskarshi daff tata yayi yana cewa
"speak, are you a lizard?"
qara girgiza kai tayi tana maida kanta baya
"m..mussadiq..."
"yes?"
"stop moving closer.. please"
"why?" yasake fada still moving closer
"al..alright, am.. am sorry" tafadi kalmar datasan ita kadai zata ceceta
ganin still bebar matso fuskar ba yasata sake cewa
"am sorry, ba gashi nafadi ba? please stop"
"you're sorry for what?" yafada still moving closer
"sorry for hanging up your call"
"and?"
"and.. and for calling you a psycho" tafada tana qara jabaya
"and?"
"and.. and for... for daring you"
"and?"
Dan squeezing fuskarta tayi cikin rashin fahimta
"I.. I think that's all"
"really? you thought so?" yafada yana daga gira daya
"am sorry for everything then, please let me go, this is totally wrong" tafada kamar zatayi kuka
shiru yayi yana sake kafeta da idanunshi dake lullu6e cikin glass din idonshi
itama sai samun kanta tayi da kafeshi da idanu kamar yau tafara ganinshi
sun dan jima ahakan idanunsu kafe da juna
motsa baki Mussadiq yayi zaiyi magana saidai kafin yayi zee ta rigasa
"Deen.." tafada ahankali cikin murya mai kama da rad'a
kallonta ya cigaba dayi bece komai ba
hawaye yaga sun taru a idanunta data kafeshi dasu babu kyaftawa
ahankali suka zubo suka gangaro kumatunta
mammaki ne ya kamashi ganin hawayen nata sunqi tsayawa sai gangarowa suke daga cikin idanunta dasuka fara chanza launi
hakan yasa ahankali ya janye hannunshi daya tareta dashi abaya saidai bata motsaba bare ta tashi din tana nan a yadda take still wet idanunta kafe dashi
jiyayi duk badadi don saiyayi tunanin shine silar hawayen nata
"are you ok?" yafada yana kai hannunshi fuskarta ya sharce hawayen kumatun damarta da yatsa
firgigit tayi lokacin da taji contact din yatsar a fuskarta sai kuma tayi saurin kallonshi kamar wadda ta farka daga barci sai kuma tayi saurin tashi tsaye
shima tashin yayi yana kallon yadda take share hawayen fuskarta da bayan hannunta
saurin duqawa tayi ta dauki jakkarta data fadi tun lokacin daya fizgota ta rataya idanunta aqasa
"Z... Ummie" ya kirata yana kallonta
bata kalleshi ba tazo zata wuce still kanta aqasa
shan gabanta yayi, ganin hakan yasa ta chanza hanya nan ma ya tare yana kallonta yanason suhada ido amma taqi dago fuskarta
"Ummie..."
"get out of my way please" ta katseshi cikin muryarta dake rawa sosai
"but why..."
kasa qarasawa yayi saboda dagowa datayi ta kalleshi da idanunta dasuka qarasa rinewa daidai kuma lokacin wani hawayen ya digo
cigaba da kallonshi tayi da idanun nata batareda ta iya fadin abinda takeson fadi ba
jikin Mussadiq ne yayi sanyi, tabbas ya hango wani abu cikin idanunta mai wuyar fassaruwa kuma kallo daya yaimata yagane she's emotionally hurted
ahankali ya kauce mata daga hanya still yana kallonta
bata jira komai ba tawuce dasauri tanufi kofa
juyawa yayi yana binta da kallo yana cire shade din idanunshi a lokaci guda harta fice daga library din.
dasauri tafito daga library din ta juya tabi wata hanya cikin gudu gudu sauri sauri
bata tsaya ba saida takai wani quiet wuri inda babu mutane
dagudu ta qarasa gindin wata bishiya ta durqushe wajen kukan datake riqewa tundaxu ya kufcemata ta toshe bakinta da taffukan hannayenta tacigaba dayi da dukkanin zuciyarta
❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️
tun daga nesa data hangoshi zuciyarta tasake sauya bugu
ahankali shauqi yafara mamaye zuciyarta harya tsuma dukkanin jikinta
ahankali ta cigaba da saukowa daga stairs din idanunta akanshi
zaune yake kan daya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun falon
sanye yake cikin wata dakkakiyar dark brown shadda wadda tafiddo farar fatarsh sosai
kanshi na sanye da hula zanna bukar wadda ta shiga da shaddar hannunshi sanye da tsaddadiyar agogon fata brown kaffafunshi kuma sanye suke da baqaqen socks.
zaune yake a kujerar dake facing kujerar mami fuskarshi dauke da qayyataccen murmushinnan nashi mai bayyana beauty point dinshi
agabanshi akwai Dan qaramin table na glass dake cikeda drinks da kayan ciye ciye wanda da alama ko ta6asu beyiba.
shagala tayi da kallonshi harta qaraso falon batasaniba saida muryar mami ta katseta daga lulawar datayi duniyar kallonshi
"kinga baqon August ko?" inji mami tana nuna Deen dake murmushi
murmushi Lailah tayi tace
"lallai kam mami, nima yanzu Afrah taje take gayamin, maraba da baqin August"
dagowa Deen yayi ya kalleta yadan hade girarenshi sai kuma ya sauke kanshi qasa murmushi still a fuskarshi
"shiyasa garin yau ya lumshe kamar za'ayi ruwa ashe dai da dalili" inji mami cikin tsokana
"aikaudai mami, but are you sure nan yazo direct? tayiwu fa 6atan hanya yayi don ni ban yarda wannan ziyarar tamuce ba" inji Lailah data zauna kujerar kusada ta mami
qara dagowa Deen da duk kunya ta hanashi saqat yayi ya kalli Lailah again da expression din 'ke ko?' a fuskarshi, itakuma tayi murmushi tana dan juya idanunta
"lallai kau, babu mammaki. to Mallam balarabe anya ziyarar nan tamuce koko dai gaskiya Lailah ke fada?"
hannu yakai yana dan shafa sumar kanshi cikin jin kunya yace
"mami Lailah kawai sotake ta hadamu"
"babu ruwana mami, ki tambayeshi yaushe rabonshi da gidannan" inji Lailah
"ina ruwanki to? ai nasan ayyukane sukayi mashi yawa shiyasa amma ai kowa yasan son mai son zumunci ne" inji mami cikin kare Deen
kallon juna Lailah da Deen sukayi Deen yayi wani murmushin gefen baki
Dan 6ata fuska Lailah tayi tace
"kai mami shine zaki bani gula?"
dariya mami tayi
"ai gani nayi kina neman yima dana sharri ne"
"d'an da bama wani jidake yake ba?" inji Lailah yana kumburi
"babu komai, ai tsakanin uwa da d'a sai Allah, babu mai shiga tsakaninmu"
qara kumbura fuska Lailah tayi tana kauda kai tace
"aike dama bakyason laifinshi"
yar dariya mami tayi tace
"ai baya laifi"
saikuma ta fuskanceshi
"ya aiki? komai lfy ko?"
Deen da murmushi yaqi barin fuskarshi yace
"Alhamdullilah mami, komai na tafiya daidai"
"masha Allah, Allah ya taimaka ya cigaba da budawa"
"Amin ya Allah mami" ya amsa cikin girmamawa
"ya wajensu Kaka? kwana biyu haduwa tayi wuya"
"suna lfy, tacema a gaidaku"
"muna amsawa, insha allah zan shigo wajenta ma kwanannan"
"to allah ya amince mami"
duk hirar dasuke idanun Lailah na kanshi tana cikeda burgewa tana jin kamar ta hadiyeshi don so
miqewa mami tayi tana cewa
"ina zuwa bari nadubo wancan sarkin 6anar, yanzu haka tanacan tanayi dama Idan kaji shiru babu wulginta to gwara ka bincika"
murmushi kawai Deen yayi
"ayimin magana Idan katashi tafiya"
"to insha Allah, a sauko lfy"
ahaka mami tatafi tabarsu su biyu a falon
sadda kai Lailah tayi tafara wasa da yatsunta nervously
dama Idan suna wuri daya su biyu kadai haka takeji, duk saitaji ta takura
jin shiru yasa tadan dago ta saci kallonshi sai taga hankalinshi ma nakan wayar hannunshi
sauke idanun tayi tanadan murmushi sannan taqara dagowa tace
"bakasha komai ba yaya"
dagowa yayi daga kan wayar ya kalleta sai kuma ya kalli kayan gabanshi yace
"hmmm nasha ruwa ai, wannan tullin kayan ina zani dasu? am full"
tasan gaskiya yake fada don Deen baya yima abinci kawaici Idan yanaso ci yake
"ok, ya aikin? hope yanzu ayyuka sundan lafa" tafada cikin son janshi da fira don tasan Idan tayi shiru saidai suyi zaman kurame don ta,lura kamar he's not good at fira, shirunshi yafi surutunshi
"Alhamdullilah, da sauqi gaskiya sosai. pressure din yarage"
"to Allah ya taimaka, more more grace to your elbow"
murmushi yayi yace
"Amin Amin, kefa? ya school?"
"school Alhamdullilah, munata fama ga exam nata gabatowa"
"to Allah yabada sa'a, adai cigaba da dagewa"
"insha Allah yaya"
haka suka cigaba da firarsu sama sama har suna haka abba yashigo.
sosai abba yaji dadin ganinshi dukda dama yasan da zuwanshi, cikin girmamawa Deen ya gaidashi yana amsar handshake din da abba yake miqomashi a kunyace
inda sabo yaci ace Deen yasaba da hakan don hakan nacikin al'adar abba miqama mutum hannu suyi musabaha duk banbancin shekarunsu kau
abba irin mutanen nan ne masu faran faran ga raha da dariya
nan ya zauna suka shiga labari wanda duk yashafi aikin Deen
a yanayin dasuke firar zaka hango tsantsar qaunar da abba keyima Deen shikuma Deen zaka hango tsantsar girmamawa da biyyaya dayakema abban.
can kuma suka tashi abba da Deen suka fita waje suka bar Lailah a falon
parking space suka nufa inda Abba yanunama Deen sabuwar motarshi daya saya kwana uku daya wuce wadda ke lullu6e cikin rigar motar
da taimakon Deen suka yaye lullu6in motar.
danqareriyar motace yar yayi mai mugun kyau, sosai Deen yayima Abba allah yasanya alhairi sannan yashiga duba mashi lafiyar motar kamar yadda Abba ya buqata don ganin ko tanada wani fault daya kamata agyara kafin afara hawanta
Lailah ce ta tashi daga inda take zaune taqarasa jikin Windows din falon tadan yaye labulen wajen tana leqensu
Deen ne tagani gaban motar ya dage murfin gabanta ya sunkuya yana dubata
tattare hannuwan rigarshi dayayi yaba farar fatar hannunshi bayyana mai cikeda kwanttatun gargasa
lumshe idanu tayi ahankali tasake budewa akanshi, tarasa meyasa komai Deen yayi saiyayi mugun yimashi kyau.
cigaba da kallonsu tayi har yagama yan gyare gyaren dayake, Abba ya zagaya yashiga motar Deen na gaban motar still harya tadata shikuma yaqara sunkuyawa yana duba engine motar
sun dan dade ahakan kafin abban yafito bayan yakashe motar shikuma Deen ya maida murfin gaban motar ya rufe alamun sungama Abinda sukeyi
sake lullu6e motar sukayi sannan sukazo suka wuce suka kama hanyar part din abban.
Ajiyar zuciya Lailah tasauke tana sakin labulen, sosai take tausayama kanta na fadawa son maso wanin datayi, fatanta dai Allah yabata mafita akan wannan matsalar tata yakuma sassauta mata.
sai bayan sallar isha'i Abba da Deen suka sake shigowa main house din don Deen yayi bankwana dasu mami.
basu dade ba suka fita da Abba da Deen da Afrah data liqemashi suka rakashi har wajen motarshi
ko anan ma sundan qara dadewa suna fira sannan Deen yashiga motar bayan sunyi sallama ya tada motar yajata.
bin motar da kallo Lailah dake leqensu ta windown dakinta tayi harta fice.
sauke wata nannauyar Ajiyar zuciya tayi sannan tasaki labulen takoma ta jingina da bango tana Lumshe idanunta.
💚💚💚💚💚💚💚💚💚💚
Tun bayan rabuwar zee da Mussadiq bata qara walwala ba, haka ta qarasa ranar cikin qunci da rashin kuzari
sosai batool ta damu da hakan kuma tambayar duniyarnan tayimata akan meke damunta amma taqi gayamata saidai tace mata babu komai
dole ta haqura ta kyaleta saidai tasan akwai abinda ke damunta kuma tafi alaqanta hakan da qila mikin soyayyarta ne yatashi don dama haka take wasu lokacin, duk yadda takeson 6oye damuwarta tayi pretending she's ok wani lokacin kasawa, wani lokacin kawai sai kaga mood dinta yachanza takoma very depressed.
murda handle din kofar akayi tawaje aka turo kofar
batool ce tashigo dakin ta tsaya daga bakin kofar tana kallon zee
haryanzu zaune take inda tabarta rungume da pillow ta kafe wuri guda da ido
Ajiyar zuciya batool ta sauke sannan ta qarasa shigowa cikin tana sakin murmushi cikin son wartsakar daita
fadawa tayi kan gadon itama gefen zee tana dariya wanda hakan yadawo da zee daga duniyar tunanin data shiga tajuyo tana kallonta
"albishirinki" inji batool happily
dauke kanta xee tayi daga kallonta don kwata2 bata cikin mood din wasa, kamar bazatayi magana ba can kuma tace
"goro"
murmushi batool tayi tace
"to yarinya Akhie tafiya zaiyi, guess where?"
Dan kallonta zee tayi saikuma tasake kauda kai, da batool tasan yadda batason ko magana ce dabatazo tana takura mata ba amma sanin wacece batool din yasata sanin amsamata din kawai shine kwanciyar hankalinta
"where?" ta tambaya tana dan yatsine fuska cikin qosawa
"Nigeria!" batool tabata amsa cikin murna
saurin juyowa Zainab tayi ta kalli batool din
"Nigeria?.."✍?
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*076*
*THE TRIP*
"Are you serious?" inji zee tana kallon batool cikin mammaki
"wlh yanzu naji suna labarin da ummy, gobe ma zasu tafi zasubi flight din 12noon"
shiru zee tayi tana kallonta, kawai saita tsinci kanta dajin wani irin kewar kasar tata.
bata ta6a tunanin zatayi missing Nigeria nan kusa ba amma yanzu dataji wannan zancen saitaji tayi missing dinta sosai, tayi missing qasarta da mutanen ciki, jitayi dama daita za'ayi tafiyar amma kuma anya zuwan bazai famamata tsohon mikinta na zuciya ba? kodayake anan dinma ba tsira tayiba, tagudo nan don mance past dinta tayi moving on amma seems it's not easy don kullum past dinta cikin hunting dinta yake
kauda kanta tayi daga kallon batool din tace
"me zaije yi acan to?"
"asalin tafiyar batashi bace, Ahmad wani business trip zaikaishi can shine shima yace zayaje don yarabu dazuwa gashi dama kwanannan he's less busy"
"kenan tareda Ahmad zasu tafi?"
"yeah... did you want to go too?" inji batool tana quramata idanu
wani kallo zee tayi mata sai ta kauda kai
"never!" tafada tana hade fuska
murmushi batool tayi
"nayi tunanin kina kewan can ne"
"banayi" tabata amsa tana komawa ta jingina da frame din gadon
murmushi tasake yi tace
"A'a dole kiyi missing Nigeria, gida gidane ko don mahaifanki dake can"
"ai yanzun ma kamar tare muke don kullum muna waya kuma Idan naso ganinsu ma zan gansu ta video call so bana wani missing dinta"
murmushi kawai batool tayi bata qara cewa komai ba saidai talura da yadda mood din zee yaqara chanzawa wanda ta tabbata harda zancen tafiyar tasake dagulamata mood din
A daren ranar barci rabi da rabi zee tayi, sosai tunanin tafiyarsu Aymaan ya tsayamata arai yakuma tadomata tsumin kewar qasarta da mutanen cikinta.
washegari sukuku ta tashi, jiki babu kwari tahau daily chores dinsu da shirin makaranta.
suna zaune a dining suna breakfast Aymaan ya sauko daga sama shima yayi joining dinsu.
gaidashi batool da zee sukayi ya amsa cikin kulawa da barkwanci kamar yadda yasaba sannan shima ya gaida ummy
batool ce tayi serving dinshi sannan ta koma ta zauna tacigaba dacin abincinta
jawo abincin yayi gabanshi yafara ci saidai rabin hankalinshi nakan zee daketa tsakurar abincin sama sama
Dan murmushi yayi sannan yadauki mug din shayinshi dake tururi yadan kur6a ya ajiye yasake kallon zee
"ke yar Nigeria, hope kinsan yau zankaiwa qasarku ziyara?"
dagowa zee tayi ta kalleshi sai tadanyi murmushi
"hmmm jiya nakejin labari, Allah ya tsare hanya"
Dan daga gira daya yayi yace
"hakama zakice? nayi tunanin liqewa zakiyi kice kema kina zuwa"
Dan ta6e baki tayi tace
"saidai nace Allah yakiyaye hanya"
dariya batool tayi tace
"hmmm haka zakice ai, yarinya tazo qasar turai taji dadi ta manta da qauyenshi" taqara fashewa da dariya Aymaan na tayata
"kekau kullum tana cin dajaja🍗ta larabawa tana shan ni'imttaciyar weather mu ba dole ta manta ba?" inji Aymaan
kumbura fuska zee tayi tana makamasu wani kallo
"wane ni'imttaciyar weather? ai wlh Nigeria tafi nan weather mai ni'ima. kuda nan da rana tsabar zafi kamar ana gasa mutum a oven? a qasarnan Idan kayi walwala da zirga zirga cikin kwanciyar hankali to darene, ahakan kuma kukeda weather mai kyau?" tafada tana harararsu
"ahaka kuma kike qara haske kina fresh, dakike can kauyen naku ko rabin kyan yanzu baki kaiba dukda ni'imttaciyar weather taku" inji batool
"wake haske? ai kuma kunsan nafi kyau danake qasarmu, anan banda tsabar rana da zafi me akeyi, badon ina kaffa kaffa da kaina ba da yanzu nazama duna qila sai an haska da touchlight za'a dinga ganin fuskata dakyau"
dariya duk sukayi harda ummy dake aikin sauraronsu
"aimu ranarmu fari takesawa ba baqi ba ko kin ta6a ganin balarabe baqi? koma akwaisu yan kadanne, mafi yawancinmu fararene" inji Aymaan
"Allah mai iko, yanzu nan kuma jinku kuke ku larabawa ne ko?" inji ummy da sai yanzu tasa baki
dariya zee tayi
"karfin hali kenan, dadai ba'a san asalin balbela ba"
kumbura fuska batool tayi tace
"yo Idan ba larabawa bane ba su wanene?"
"ato, tayani tambaya" inji Aymaan
"cikkakun larabawa nemu" inji batool
"fararen ma kuwa" Aymaan yabata amsa
dariya sosai zee keyi don sosai suka bata dariya
"A'a gwarama kayi shiru da bakinka Aymaan, Idan ana maganar farare kabar zazzaqewa don.kunya zakasha" inji ummy dake taya zee dariya
Dan 6ata rai Aymaan yayi yace
"to ni ba farin bane? wai batool ni ba fari bane?"
Dan kallonshi batool tayi saikuma tafashe da dariya
"wlh tlh Akhie kai baqine"
ta qarashe tana saurin miqewa daga kan kujerarta don dama kusadashi take
sakin bakinshi Aymaan yayi yana kallonta itakuma takoma bayansu ummy dake dariya tana dariyar itama
"kutt... nizakiba kunya muna team daya? lallai kin qoshi" yafada yana kwafa ya sake daukar mug din shayinshi
"yo ai gaskiya ne Akhie, kasan ni bana qarya" inji batool tana dariya
kada kai kawai Aymaan yayi bece mata komai ba ya cigaba dacin abincinshi
kujerar kusada ummy batool taja ta zauna taqi