Showing 144001 words to 147000 words out of 322641 words
Chapter 49 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
tace
"scary mouse, har kaji tsoro ko?"
Kallonta yasakeyi ya danyi murmushi sai kuma ya qara dauke kai
"tunanin me kakeyi harna qaraso baka jini ba?"
Girgiza kai yayi batareda ya kalleta ba bece komai ba
"yaushe ka iso school?
Juyowa yayi ya kalleta again, ahankali ya bude baki yace
"dazu" a takaice
Tsayawa itama tayi tana kallonshi don sosai kallonshi yabata mammaki
Babu wannan fara'ar babu murmushi babu sakewa dukda fuskar ba adaure take ba but look dinshi is very formal.
"ya dai?" tafada tana kallonshi cikin ayar tambaya
kauda idanunshi yayi daga kanta yana cewa
"daidai"
"what's wrong?" tasake tambaya
Juyowa yayi yasake kallonta, kallon da yasa hanjinta dan kadawa don kallon yana dauke da ma'anoni daban daban
"babu, wani abu kika gani?" ya Tambaya yana cigaba da yimata irin kallon
Shiru tayi da farko saikuma tace
"kamar you're not alright"
Wani slight murmushi yayi sannan ya dauke kanshi, shima kamar bazaiyi magana ba sai yace
"am alright, kawai na gano wani abu ne"
"Wani abu? Wane abu?"
Yan tsakuwa ya tsinta a gabanshi qwara biyu ya tilla daya can nesa
"abinda ake 6oyemin" yafada yana tilla dayan ma
Shiru tayi tana kallonshi kawai takasa cewa komai
Qara tsinto daya yayi ya riqe yana kafeshi da idanu kamar mai karanta wani abu jikinshi sai kuma ya danyi murmushi
"yanzu nasan komai, na daina lalube" yafada yana tillashi shima
Jikin zee ne yadanyi sanyi kamar bazata iya cewa komai ba sai kuma tace
"wai meke faruwa ne Deen? Are you ok?"
Juyowa yayi ya kalleta da idanunshi dasuka fara kadawa
"nayi kama da wanda ke ok? Am not"
"then.. What's wrong? Sai magana kake marassa ma'ana aguna, meke faruwa ne?"
"kin fini sani Zainab, kinsan komai and that's what hurts me more, 6oyemin dakikayi"
Kallon idanunshi datake yasa nata ma kadawa tanajin yadda zuciyarta ke bugawa sosai
"mena 6oyemaka?" tafada cikin rawar murya
"da ace baki sani ba da bazan ji komai wajen gayamiki ba Amma kinsani Zainab, kinsani.
Kuma barina a duhun da kikayi yafi komai yimin ciwo"
Hawaye ne suka taru a idanunta
"waya gayamaka?"
Dan murmushi yayi mai ciwo tareda kauda kai
"sanin Hakan beda muhinmmancin"
"don Allah ka gayamin, please" tafada tana qoqarin danne hawayenta
"it doesn't matter Zainab, bayada wani fa'ida" yafada yana qara kauda kanshi yana jin zuciyarshi na zafi sosai
Sauke idanunta tayi qasa Hakan yaba hawayenta damar digowa kan skirt dinta
"nayi Hakan ne don karka shiga damuwa, nayi tunanin zan iya solving abin ne ni kadai" tafada ahankali batareda ta dago ba
"amma ai abin nima ya shafeni, nima inada right din sanin kome ke faruwa Koda abin zai bugarmin da zuciya" yafada shima batareda ya juyo ya kalleta ba
Ahankali ta tsane idanunta sannan ta dago ta kalleshi
"am sorry, kamar yadda nafada dazu nayi Hakan ne don karka shiga damuwa"
Shima juyowa yayi ya kalleta
"ni idan ban shiga damuwa ba shi wanda kika bari da broken heart ya zaiyi da rayuwarshi?"
Kallon rashin fahimta tayi mashi
"wa kenan?"
Murmushin takaici yayi
"da kinsani da kinbar pretending saboda nariga nasan komai, everything"
"pretending kuma? Ni bansan abinda kake magana akai ba"
"really? Kenan kin manta da wanda aka ajiye maganarku dashi tare?"
"mene? Aka ajiye maganar me?" tafada in confusion
"maganar aurenku, kina sonshi, keda kanki kika kawoshi wajen dad dinki aka kuma ajiye magana akanku, ko shima kin manta" yafada zuciyarshi na quna
"what? This is crazy! Yaushe aka badani bansaniba?
Murmushin takaici kawai yayi ya kauda kai
"Tambayarka nakeyi Deen, waya gayamaka haka?"
"wanda bazai ta6a yimiki qarya ba, so is better kibar pretending" yafada cikin qunar zuciya
"Daddy?"
Juyowa yayi ya kalleta da idanunshi da haryanzu basu washe ba saikuma ya kauda kai
Dafe goshi zee tayi kawai tayi shiru
Saikuma ta dago ta kalleshi
"dame dame ya gayamaka?"
"dama akwai wasu abubbuwan da be gayamin ba?" yafada cikin qaryewar zuciya yana kallonta kamar zaiyi kuka
Jin tayi shiru batace komai ba Saima kallonshi datake itama yasa yace
"don Allah ki gayamin, zanfi son inji daga bakinki bawai daga wani wajeba, qila zafin bazai kai yadda zanji ba idan nayi discovering Hakan a bakin wani"
Sosai yabata tausayi Hakan yasa wasu hawayen sake taruwa a idanunta
"dagaske ne kina sonshi kuma an tsaida maganar ku? Yaushe ne Hakan ya faru? Kafin muhadu ko kafin mufara soyayya ko bayan Hakan? Don Allah ki bani wadannan amsoshin ko zan samu rintsawa yau"
Kauda kai tayi tana dauke hawayenta dasuka kusan gangarowa
"ba Gaskiya bane, tunda nake ban ta6a soyayya ba sai akanka kuma bazan ta6a sharing soyayyar ka da wani ba"
Dukda be yarda ba Amma kuma yaji sanyi, yaji zafin zuciyarshi ta dan ragu
"amma ai bazai yimiki qarya ba"
"zai iya komai don ya rabamu"
Kallonta yayi cikin tashin hankali
"ya rabamu, dama yasan da maganar mu"
Dagowa tayi ta kalleshi
"yasani, sosai ma bama shikadai ba, harda mummy"
Shiru yayi yana kallonta da mammaki
_*shiyasa nazo wajen ka, please ka jawo ra'ayinta akan Hakan tunda naji ance kai abokinta ne, kana iya abinda ya gagaremu ka kuma samata ido kaga ko wani ke zugata don ni nafi tunanin Hakan*_
Girgiza kai Deen yayi bayan ya gama tuno wadannan kalaman na daddy
"anya Zainab daddy yasani kuwa? I don’t think so" yafada yana girgiza kai
Dan murmushi tayi sannan tace
"meya fadamaka? Ka gayamin"
Shiru yayi kamar bazai gayamata ba sai kuma ya sauke Ajiyar zuciya ya shiga labarta mata yadda sukayi da daddy jiya daddadare
Dan murmushi zee tayi mai ciwo sannan tace
"kasan abinda yayi?"
Girgiza kai Deen yayi ahankali batareda yace komai ba
"warning dinka yayi indirectly akan ka rabu dani"
Tsayawa yayi kawai yana kallonta yana jujjuya maganar ta
"Deen daddy beson tarayyarmu, duk hanyar danasan zanbi na fahimtar dashi nabi amma yaqi fahimta ta, I tried and am still trying amma banganin alamun nasara, bansan ya zanyi ba kuma" tafada qara tsane idanunta
"naqi fada maka ne don banaso hankalinka yatashi, a ganina komai zai zama daidai kafin ka ankara, bansan zaije yasameka ba"
"don Allah ki fadamin abinda ke faruwa, komai.
Karki ragemin komai, don Allah" inji Deen
Shiru tayi hawaye na cigaba da sauko mata batareda tace komai ba
"Zainab ki tuna wannan abin mu biyu ya shafa, be kamata ace daya na cikin duhu ba, don Allah ki taimaka ki gayamin" yafada pleadingly
Cije lower lip dinta tadanyi sannan tafara bashi labarin duk abinda yafaru, daga zuwan Asaad har zuwa rashin amincewar daddy akan za6inta da dalilin haka, tiryan tiryan tabashi labarin komai har zuwa yanzu dasuke zaune
Shiru wajen ya dauka na wani lokaci
_*ka nusar daita sosai, idan ma kaga alamun zugata akeyi let me know, sai na tabbatar na koyawa munafukin hankali don na tsani munafurci kana gani na nan, duk yadda muke da mutum daya munafurceni to wlh nagama dashi kuma zamu sanya kafar wando daya ne dani dashi*_
_*ta yiwu wani ko wata ke zugata yana dorata a keken 6era da nufin kaita yabaro*_
Ajiyar zuciya Deen ya sauke, sai yanzu duk ya gane inda magangganun daddy suka dosa
Tabbas warning ne, warning yake mashi indirectly amma shi yakasa ganewa, to dama tayaya zai gane bayan besan komai ba gameda abinda yake faruwa?
Babu makawa shine daddy ke nufi da yana zugata yana huremata kunne yana so yakaita ya baro.
"Deen kar Hakan ya dameka, wannan abin duk yayisu ne don be fahimceka ba, amma ina ji ajikina watarana zai fahimta, very soon"
Dagowa yayi ya kalleta
"Zainab daddy yanada Gaskiya, yafimu hangen nesa tunda gashi ya hango abinda duk bamu hango ba, Ya hango future dinmu.
Zainab akwai banbanci sosai a yanayin rayuwar da taki, ke kinsaba da akwai, kin saba da wadata a kodayaushe Yayinda ni a nawa bangaren ba Haka bane, mu abu biyu muka saba dashi, samu da rashi"
"Deen kaima kasani, ni kai nakeso ba abinda ka mallaka ba ko zaka mallaka, kaine farinciki na, farinciki yafi gold and sliver"
"Zainab, abin saukin fada gareshi a baki Amma wuya a experience, ina sonki zee, soyayyar da babu sirki ko kadan aciki, ba don komai naki ba Zainab kuma ina iyayin komai don na faranta miki amma Tambayar anan shine zaki samu farinciki a duniya ta? Duniyar da babu bushasha babu ababen more rayuwa kamar wanda kika taso aciki? Zaki iya zama a irin gidan danake zama? Zaki iya cin irin cimarmu, zaki iya shan ruwanmu? Zaki iyasa irin suturarmu? Zaki iya?"
"Zan iya, kuma fa mutane ne kuma kuna rayuwa da duk abubbuwan daka lissafomani naku cikin farinciki.
Rayuwa a kango tareda kai kamar rayuwa ne acikin mansion mai cikeda kayan more rayuwa
Rayuwa batareda kai ba a mansion kamar rayuwane acikin kango Deen.
Ina sonka a yadda kake kuma zan iyayin komai a dalilin son ka, zan ci cimarku zansha ruwanku nakuma saka suturarku don wata rana ba kasancewa zanyi babu ci babu sha Saidai ni nazama cima ga wasu hallitun, namana yazama abincin wasu qannanun dabbobin, suturata kuma daya ce ta Gaskiya wannan farin kyallen, so why zance bazan iya Hakan ba Tun a duniya, idan ban iya yiba a duniya zanyi don dole idan na mutu"
Kallonta yakeyi yana jin qaunarta na hudamashi koina na zuciyarshi
"nidai kawai sonake kayi min alqawari cewa baxaka ta6a barina ba no matter what, kowanne abu yanada qalubalenshi, wannan yana daga cikin qalubalen soyayyar mu kuma zamu tsallake da taimakon juna"
"Zainab bazan ta6a barinki ba duk rintsi, zan jajirce a soyayyarki babu gudu babu ja da baya, insha allah zamu tsallake wannan qalubalen dama duk wanda zaizo a gaba dukda bama fatan Hakan"
Bude hannu tayi ta miqo mashi tana kallonshi
"promise me, promise you'll never break my heart"
Kallon hannun nata yayi sannan shima ya dora nashi hannun asama suka damqe najuna
Shima yana kallonta cikin ido yace
"I promised, I promised I'll never break your heart, never!"... ✍️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:38 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*048*
*THE PROMISE 2*
Sun dade suna tattauna yadda zasu 6illowa al'amarin, da yadda zasu samu shawo kan dukkan muhinmman mutanen da zasu buqaci amincewarsu a wannan tafiyar tasu.
Sai a sannan zee ta yarda da wannan karin maganar ta bature na
*a problem shared is a problem solved*
Sai gashi abin yayi juye yazama mai sauqi agaresu, ita datake 6oyewa don karya shiga damuwa sai gashi saninshi yakawo masu mafita
Basu tashi school din ba sai wajajen 3pm kuma kamar yadda yasaba shi ya rakota mota yakuma bude mata kofa tashiga.
Yana jin idanun bala akanshi yana kuma lura da kallon dayake binshi dashi amma ya share don he's ready for everything.
Yana tsaye yana kallon motar yana daga mata hannu har suka fice daga school din.
Ajiyar zuciya ya sauke yana jin wani qwarin gwiwa a zuciyarshi, yes he'll fight for his love, insha allah bazai gaza ba.
Shima fita yayi ya samu abin hawa yahau shima ya kama hanyar unguwarsu.
***
Da sallama yashigo gidan hannunshi riqe da cazbaha, forehead dinshi kuma da alamar qasa alamun daga sallah yake
Kaka dake zaune a tsakar gida bisa tabarma saboda zafin da akeyi ta amsa sallamar shi
Qarasowa yayi ya cire takalminshi shima ya zauna gefen kaka yana sauke Ajiyar zuciya
"ya dai?" inji kaka
"na gaji" yafada yana yatsine fuska
"kamar wanda yayi wani aiki?"
Murmushi kawai yayi bece komai ba
Shiru Wurin ya dauka sai kuma ya matso gaban kaka yana tayata tsintar waken datakeyi
"Kaka?"
Dagowa tayi ta kalleshi
"na'am"
Sai kuma yayi shiru yarasa ta ina zai fara
"ya kuma kayi shiru? Wani abu?" inji kaka tana kallonshi cikin kulawa
Murmushi yayi saikuma ya rufe fuskarshi da taffukan hannunshi
"Tofa? Meye kuma haka kakeyi kamar wata amaryar qauye?"
Dariya Deen yayi yana cewa
"kai kaka"
Itama dariyar tayi tace
"ai Gaskiya ne, kana wani rufe fuska kamar gaban surukarka"
Murmushi yayi yace
"kika sani ko gwada yadda zanyi agaban surukar tawa na keyi?"
Dariya kaka tayi
"kuma fa, to ai sai kabari kafara yin surukar sannan"
Murmushi yasakeyi
"Kika sani ko nayi din"
"Me din?"
"surukar"
Wani kallo tayimashi ta cigaba da abin take tana cewa
"ahakan?"
Gyara zama yayi cikin zumudi yace
"Allah kaka"
"Allah me?"
Sai kuma ya sake rufe fuskarshi
"nayi maki suruka"
Tsayawa tayi tana kallonshi babu kyaftawa
Jin shiru yasa yadan leqo a tsakankanin yatsun dake fuskarshi
Janye hannun yayi daga fuska ya kalleta
"bakice komai ba"
"yo aini ban gane ma inda ka dosa ba" tafada still tana kallonshi
Yar Dariya yayi sannan yace
"to kawo kunnenki kiji"
Da sauri kau ta miqa tana murmushi
Rada yashiga yimata a kunne sai naga idanun kaka sun qara budewa
"iyee! Wai dagaske!" tafada unbelievably
Sake rufe fuska yayi yana Dariya
Tashi tayi babu shiri tana rangada gud'a
"Ayiririririririririririririririririiiiiii! Kai amma allah na gode maka, kace me?" tafada cikin tsananin farinciki
"kai kaka Kiyi ahankali kar ajimu a waje"
"a jimu a wajen, Ayiririririririririririririririririiiiiii!! Wannan ai abin son kowa yajine, abin alhairi? Kai amma allah na gode maka, iyee! Kai dole ma nayi sujjadar Godiya ga allah "
Sai tayi qasa ta kai goshinta qasa
Deen dai kallonta yake kawai fuskarshi beaming with smile
Saida ta dago sannan ta cigaba
"Allah ya tabbatar da alhairi kyakyawana, kyakyawana zaiyi aure, kyakyawana yasamu wacce yakeso, kyakyawana ya girma, ashe da rabon zanga bikinka kyakyawana, da rabon qila zanga 'ya'yanka" Sai kuma ta fashe da kuka tana rufe fuskarta da ha6ar zaninta
Dariya Deen yayi
"kai kaka, kuka kuma?"
Dagowa tayi ta kalleshi cikin kukan tace
"dole nayi kuka, dole ne 😭"
Dariya yasake yi don shi Dariya ma ta bashi
Saida tayi mai isarta sannan ta koma ta zauna ta fuskanceshi dakyau tana maida tray din waken dasuke gyarawa baya tace
"to yanzu gayamin wacece surukar tawa? Wace yar albarkar ce mai sa'ar kyakyawan sardidin jikan nawa"
Dariya yaqara yi zuciyarshi qall
"kai kaka"
"eh mana, ai duk macen datayi sa'ar samunka to tagama dace a duniya saikuma ta nemi lahira, ba cika baki ba jikana namiji ne daya tamkar dubu, ga kyawun hali ga kyawun fuska
Kamalele kamala, kamaladini mai kamala takoina, fari mai farin aniya!
Gayamin dan sardidin kyakyawana Wace santaleliyar tayi sa'ar duniya wajen za6enka?"
Dariya Deen keyi sosai tunda tafara maganar don yana jin dadi idan kaka na mashi kirari
"wannan kirarin duk nikadai kaka?"
"ai ka cancanci fin haka dan kyakyawana, Gayamin wacece?"
"ai kinma santa kaka?"
"to? Ba mammaki kau amma dai gwara ka fadamin nasan ko ainahin wacece"
Murmushi Deen yayi
"Aminiyarki ce kaka"
"Aminiyata kuma?" tafada cikin rashin fahimta
"eh, Zainab"
"Zainab.. Zainab.. Zainab" tafada cikin son tunano mai sunan
"kai kaka Gaskiya kinfara tsufa wannan mantuwa haka? To Zainab yar makarantarmu dinnan, diyar mummy wadanda muka zauna asibiti dasu"
Wara idanu kaka tayi
"wacece? Kana nufin wannan Zainab din?" tafada tana waro idanu
Murmushi yasake yi
"Ashe kin gano? To ita"
Ahankali fara'ar kaka tafara ragewa a fuskarta mammaki ya maye gurbin murnar
Ganin wannan chanjin yasa shima fara'arshi ragewa
"yadai kaka?"
"bakada hankali ne? Wace yarinya kake nufi? Wannan diyar masu kudin?" ta tambaya still a mammakince
"eh kaka ita din"
"a wane duniyar mahaukatan Hakan zai yiwu? Ko kai bakasan kosu waye ba?"
Murmushi yayi yace
"Kaka nasan kosu waye mana, ai ba wannan ne abin dubawa ba hallarcin Hakan za'a duba"
Sakato tayi tana kallonshi
"to don kai kana sonta cemaka akayi zata soka ne?"
Murmushi Deen yaqara yi sannan ya matso kusa ya kama hannayen kaka ya riqe
"mezai hana taso ni kaka? Maganar ma damuke yanzu su daddy da mummy duk sunsan da zancen"
Sakin baki kaka tayi tana kallonshi kamar yau tafara ganinshi tama kasa cewa komai
Sakin hannunta daya yayi yadanyi waving a fuskarta
"kinyi shiru kaka"
"dole inyi shiru kyakyawana, ka tabbatar da abinda kake cewa kuwa"
"wlh kau kaka na tabbatar, wlh duk sunsan da maganar" yafada cikin zumudi
"ikon allah" inji kaka cikin mammaki saikuma taji kaso sittin na cikin murnarta yabi iska
Qara ruqo hannayenta Deen yayi sosai yace
"to kaka ya naga baki murna kuma?"
"ai kyakyawana abin ne yazo min wani iri, anya kau baka debo da zafi ba?"
Qara damqe hannunta yayi
"haba kaka, komai mai yiwuwa ne muddin allah be haramta ba"
"hakane, amma sai inga kamar yarinyar tafi qarfin ka, bakaga daga gidan data fitoba? Ya zakayi daita?"
Dan murmushi yayi
"kamar ya yaya zanyi daita kaka?"
"Ato ai dole nace haka, yarinya tasaba da akwai, ga cima mai rai da lafiya kullum cikin wadata take ya zakayi daita idan ka aureta? Wai ita ma tace maka ta amince dakai ko kuwa?"
"eh kaka, nima tana sona kuma ta amince ta zauna dani akowanne hali, tana sona sosai tsakani da allah"
Shiru kaka tasake yi sai kuma tace
"to iyayenta fa? Sun amince suma?"
"eh mana kaka, duk sun amince, duk sun yarda" Yafada yana murmushi yana kallonta yanason yaga fara'arta ta dazu tadawo
"ikon allah, to allah yaza6a Mafi alhairi, allah ya tabbatar da alhairi" tafada incheerfully
"to amma kaka yanaga bakya murna irin na dazu?" yafada yana 6ata fuska
"ina murna mana, ina murna sosai, kawai dai ina fargabane kar muna zaman zamanmu mujawoma kanmu matsala" tafada tana jawo tray din waken ta cigaba da tsinta
"insha allah kaka babu wata matsala, ki tayamu da addu'a kawai" yafada shima yana saka hannu a tsintar
"to allah ya tabbatar da alhairi, ai addu'a muna yimuku kullum kuma zamu cigaba dayi"
"yauwa kaka ta" yafada suna cigaba da tsintar yana cigaba dayi mata firar zee
Itadai sauraronshi kawai take amma kwata2 hankalinta yaqi kwanciya da za6in nashi, ba don batayi mata ba sai don fargabar faruwar abinda bata shirya mashi ba kuma bata fatan ya lokacin ya riskesu nan kusa har abada.
*ZEE*
A bangaren zee kuwa sai bayan dinner taje tasamu mummy har daki don yanzu don dole mummy tazama makusanciyarta saboda ra'ayinsu dayazo daya.
Anan ne tasamu mummyn ta zauna ta fadamata duk yadda sukayi da Deen da safe dakuma yadda daddy yaje wajenshi jiya.
Ajiyar zuciya mummy ta sauke sannan ta kalli zee tace
"Zainab, Gaskiya wannan maganar tawuce duk yadda kike tunani, ni aganina gwara kawai ku haqura da juna saboda Gaskiya daddy bada wasa ya dauki maganar nan ba"
Gaban zee ne yafadi
"mummy... Na haqura dashi kikace?" tafada cikin rawar murya
"qwarai Zainab saboda Gaskiya wannan al'amarin ba qaramin al'amari bane, dukda daddy be fahimci wasu abubbuwan ba shima ta Wani bangaren yanada Gaskiyarshi akan wannan al'amarin don idan kika tsaya kika natsu kika duba zakiga duk wannan abin dayakeyi duk saboda ke yake yinsu, he's making sure