Showing 228001 words to 231000 words out of 322641 words
Chapter 77 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
tsaye bakin kofa yana kallonta
Jitayi kamar ta saki ledar don rikicewa don sosai kallon dayake binta dashi ya rikitata
Ahankali ya dauke idanunshi akanta ya cigaba da warware hannun longsleeve din shirt dinshi wanda ya nannade wajen alwalla sannan yazo ya ra6ata ya wuce.
Sake tamke idanunta tayi cikin wani yanayi tanajin yadda zuciyarta ke bugawa har lokacin
Innallilahi, what's all these?
Ta dade sosai anan din batareda ta iya sake motsawa ba sai kuma tunanin kar yadawo ya taddata wajen yasa ta cira kafarta Dakyar ta wuce ciki
Tana shiga daki batool na fitowa daga bayi
Tsayawa sukayi suna kallon juna
Can batool ta qaraso ciki tana cewa
"Sai yanzu yabarki kika taho?"
Ajiyar zuciya zee ta sauke ta qaraso batareda ta amsa ba ta zauna gefen gado
"ya akayi kuma?" inji batool
"batool, yaya Aymaan fa ya ganmu" tafada tana kallonta
"nagani nima, am scared like hell, tunda nasamu nashigo ban ganshi ba na hauro sama da gudu, wlh haryanzu gabana faduwa yake" inji batool
"hmm naki mai sauqi ne batool, yanzu muka Hade dashi aqasa.. Kai damn this guy!" tafada tana dafe kai
"Menene kuma?" inji batool tana kallonta
"ashe mance ledar da ummie tabamu nayi a motar don 6acin rai, shine yazo yaba maigadi yakawo min, daidai na amsa ina juyowa muka sake ido hudu da yaya Aymaan kuma na tabbata yaji lokacin da maigadi ke cewa gashi inji wannan mutumin"
Wara idanu batool tayi
"what if yayi tunanin shiya baki?"
"abinda nake gudu kenan, dama tun farko banso zuwa gidan nan ba yanzu ga irinta, yanzu da wane ido zan sake kallonshi? Mutumin dayasa aka tsaremu dani dashi few weeks ago yagani taredani a mota harda saqon leda, kai" tafada cikin takaici
"Gaskiya kam abin beyi ba yanzu yaya zamuyi?" inji batool
Saurin juyowa zee tayi tana facing dinta
"don Allah idan yadawo kije ki fadamashi duk abinda yafaru, ki gayamashi muma bada son ranmu muka shiga motar ba, I just can't bear it idan ya cigaba da yimin wannan kallon"
Wara idanu batool tayi
"wa? Ni? Ca6 bakisan yaya Aymaan ba, Kodan kinga Koda yaushe yana washe baki? To wlh idan bude miki dayan shafinshi bayada kyau, ko giyar wake nasha bazan fara tunkararshi ba yanzu don qaramin aikinshi ne ya hurgadoni waje"
Sake dafe kai zee tayi, ita ba komai tafi jiba sai kar ya yimata wata fassarar kar girmanta dayake gani ya zube"
"amma karki damu, ta inda aka hau tanan za'a sauka kawai ummy zamu gayamawa ta gayamashi, nasan zai fahimta" inji batool
Dagowa tayi ta kalleshi
"dagaske?"
"sosai ma, zata fahimtar dashi"
Dukda Hakan ba taji dadi ba, kawai tuna irin kallon dayayi mata dazu takeyi ranta na qara jagulewa
Ranar kasa fitowa ayi dinner da ita tayi Duk kuwa yadda batool tayi tayi daita ta fito
Kawai jitake bazata iya sake hada ido da Aymaan ba, kunyarshi takeji sosai.
Kamar yadda batool tace ma zee Hakan akayi, Ummu batool suka samu sukayi ma bayanin komai harda ganinsu da mussadiq da Aymaan yayi suka kuma roqeta ta sanar dashi
Dariya Kawai ummy tayi tace shikenan zata gayamashi
Basu saniba ko ta gayamashi din don Aymaan beyi musu maganar ba kwata2, tun zee na noqe noqenta harta ware itama don wanda takeyi don shi bema damuba harkar gabanshi kawai yake kuma ko a fuska be ta6a nunamasu ba Saima cigaba da mu'amalantarsu dayayi kamar yadda yasaba.
Saidai a bangaren Aymaan abin na nan a ranshi tun lokacin daya faru.
Shi kanshi be iya musalta yadda yaji ranar da yaga zee agaban mota tareda wani, wanin ma mussadiq
Dakyar ya iya shiga da motarshi yayi parking yafito ya wuce cikin gida yana jin kamar zuciyarshi zatayi exploding at any moment
Babu tunanin da zuciyarshi bata kawo mashi ba akan ganinsu dayah
Be ta6a sanin yanada kishi har haka ba sai ranar
Dakyar yasamu yayi alwalla yafito don lokacin sai kiraye kirayen sallar magrib akeyi
Saukowa yayi daga stairs din ahankali still yana jin yadda zuciyarshi tayi mashi jingim
Saidai me? Yana bude kofa yasakai zai fito yaga maigadi yana bata shopping bag wai gashi abata inji wannan gayen
Ga mammakinshi kuma saita amsa tana Godiya
Jiyayi kamar an makamashi guduma akai a lokacin
Jiyayi kamar zuciyarshi zata fashe a lokacin
Cikin qarfin hali yazo ya ra6ata ya wuce batareda yasake kallonta ba yana jin kamar akan gajimare yake tafiya ba qasa ba
Be dawo ba sai bayan isha'i, kuma Koda ya haye sama yashige dakinshi Be qara saukowa ba don baya buqatar sake ganinta a lokacin don shikadai yasan yadda zuciyarshi ke mashi
Washegari ne bayan yadawo daga aiki ummy ta iskeshi har daki inda anan ta gayamashi duk abinda yafaru
Yaji dadi jin zarginshi be tabbata ba Amma dukda Hakan abin bebar yimashi zafi ba, duk lokacin daya tuna Da image din zee da mussadiq agaban mota sai ranshi ya 6aci, he can't help but notice yadda sukayi matching dajuna sosai.
*BAYAN KWANA UKU*
Tafe suke suna hira jefi jefi kowanne da littafi kare a goshin shi saboda ranar da ake qwalawa
"kai wlh garinnan badai zafi ba, ina ganin weather din Nigeria is harsh ashe tanan tafi?" inji zee
"hmm kema kya gani shiyasa idan zafi yashigo har wani baqi na musanmman kakeyi, fararen sukoma baqaqe baqaqen kuma su qara extra runewa" inji batool
"Ca6 amma kuna qoqari, yanzu idan azumi yazo fa ya zakuyi?"
"ji wata tambaya, daga azumin zamuyi saboda ana zafi? Dole muyi ko muci ubanmu"
Dariya zee tayi tace
"wa zaici ubanku?"
"Yana can yana jira da sanda, gwara ka taimaki kanka duk wuya kayi" inji batool
"hmm Gaskiya bana jin ina iya azumi a qasar nan, kutt! Yanzu fa zafin yafara Shigowa ina ga cikin azumi lokacin ana tsakiyar zafi?"
"aikau wlh babu inda zaki, sai kin dandana kema, kutt! Aikau wlh karma kifara, azumi sai kin yishi anan kiji ingayamiki"
"Sai ki hanani tafiya to idan kina iyawa" inji zee tana Harararta
"tsaf ko, allah ya kaimu lokacin kiga ikon allah"
Da haka suka qarasa food canteen din school din suka shiga
Akwai yan mutane ciki inda Mafi yawanci abin sakawa aciki yazo nema wasu kuma fekewa sukayi ma hot ranar waje
A cikin wajen akwai tebura da kujerun zama
Kowanne table zagaye yake da kujeru uku.
Batool ce ta nufi wani table dake daga gefe taje taja daya daga cikin kujerun dake zagaye dashi ta zauna
Yayinda itakuma zee tawuce siyomasu abinda sukeso
Ruwa da drinks masu sanyi ta siyo masu tareda peanuts
Dawowa tayi ta iske batool na waya
"ok ganinan, nima yanzu nashigo canteen, ok ganinan zuwa"
Zama zee tayi
"keda wa?"
"nida farhana, wai inzo anfara submitting wannan assignment din"
"amma saimun gama sannan ko?" inji zee
"Sai mun gama me? Dole naje nabada yanzu ga lecturern ba mutunci ya isheshi ba" tafada tana tashi tsaye
"to yanzu zaki dawo ko?"
"eh mana, kawai badawa zanyi indawo" tafada tana wucewa
Maida hankalinta tayi kan abubbuwan gabanta ta bude ruwa ta zuba a dan kofin robar da ake siyarwa tareda ruwan, ta zuba aciki takai baki tafara sipping tana lumshe idanu jin sanyin ruwan na ratsa mata bushashen maqoshinta.
Bata ajiye kofin ba Saida taga bayan ruwan sannan ta sauke cup din tana Ajiyar zuciya
Jitayi kamar ana kallonta Hakan yasata bude idanunta dake lumshe tunda tafara shan ruwan
Jada baya tayi babu shiri cikin tsoro a sanadin abinda idanunta sukaci karo dashi
Razanar datayi yasa kingin ruwan da basu ida wucewa ba kwareta tashiga tari babu kakkautawa
Dago idanunshi dake cikin spec sa6anin shade daya saba qwamawa yayi ya kalleta
Ganin dagaske take tarin yasashi saukar da qafar dayayi crossing yana kallonta
"hey, are you ok?"
Cigaba da tarin tayi hannunta dade da baki idanunta har sunyi ja
Hakan yasashi saurin sake daukar kofin gabanta ya zuba wasu ruwan yakai mata saitin baki
Kasancewar a lokacin babu abinda take buqata kamar abinda zai tsayar mata da tarin yasa babu musu itama ta matso jikin table din daya raba tsakiyarsu ya kafamata kofin a baki tashiga shan ruwan
Saida tadan sha dayawa sannan ta kauda kai Hakan yasashi shima Janye kofin daga bakinta
Ahankali take sauke numfashin tarin datayi
Hanki fari qall taga ya miqo mata, batace komai ba ta amsa tashiga goge gefe da gefen bakinta daya 6aci da ruwa
Tana cikin gogewa kamar ance ta kalli bakin kofar Shigowa Wurin, sai idanunta sukayi mata mummunan gani.
Dammm qirjinta ya buga lokacin ta hangi Aymaan tareda batool tsaye bakin kofar sun kafamata idanu
Batasan lokacin da ta saki hanki din hannunta ba Cikin tsananin kidima
Ganin yanayinta dakuma kafe waje guda da idon dayayi yasa shima mussadiq kallon inda nan shima idanunshi suka gano mashi Aymaan da haryanzu ke tsaye kamar statue a inda yake idanunshi sunyi wani irin mugun kadawa
Dan daga girarenshi mussadiq yayi ya ta6e baki sannan yakoma yasake balancing a kujera
Ahankali Aymaan yashiga Takowa wajensu still idanunshi akansu babu ko kyaftawa
Zee jitayi kamar tajita ta 6ace daga wajen, sosai yanayin Aymaan ya razanata don tunda tasanshi bata ta6a ganinshi cikin irin wannan yanayin ba.
Qarasowa wajen yayi ahankali shima yaja dayar kujerar data rage ya zauna
Sauke idanunta zee tayi tana jin yadda jikinta ke rawa innerly
Jawo peanuts din gaban zee yayi batareda ya kalleta ba ya bude seal din yashiga dauka da daddaya yana sakawa a baki yana tauna ahankali
. Wurin ne yayi shiru, very tensed ga zee data kasa Dagowa har lokacin Yayinda mussadiq ko ajikinshi danna wayarshi ma yake hankali kwance
Can ya dago daga danna wayar dayake ya kalli zee directly wanda idanunta ke a qasa har lokacin
"so what did you say baby? Wancan din yayi miki ko a chanza wani?"
Dagowa zee tayi a mammakince tana kallon mussadiq dake kallonta shima
Baby? Wacece baby?
"bakice komai ba dear" yafada softly yana mata wani kallon qasan ido irinna masu jin barci
Cikin tsananin mammaki take kallonshi sai kuma ta kalli Aymaan dake taunar peanuts din bakinshi
Shima mussadiq kallon Aymaan din yayi saiya daga gira data
"oh! Nagane.. Nagane. Shikenan zamuyi waya, I'll take my leave yafada yana maida wayarshi a aljihu ignoring kallon shock din da zee ke mashi yafara qoqarin tashi
"ina zaka bayan baka gama ba?" inji Aymaan batareda ya kalleshi ba
Dakatawa mussadiq yayi daga tashin dayayi niyyar yi don dama abinda yake so kenan, ya tanka
Maida kallonshi Aymaan yayi akan zee da har lokacin takasa ko motsi
"ki bashi amsar shi mana _*baby*" yafada yana kallonta, kallon dake dada Kada yan cikin ta
Girgiza kai tafara tana qoqarin lalubo voice dinta dataji tarasa nan take mussadiq ya katse ta
"karka damu, maganar tsakanina da ita ne, zamu qarashe a waya"
Dagowa Aymaan yayi a karo na farko tunda ya zauna ya kalleshi straight in the eye
"who are you? How dare you?" yafada in a low dangerous voice
Murmushin gefen baki mussadiq yayi yace
"wanne kake son na amsa daga ciki?"
"kanada wani irin qarfin hali, an ta6a fadamaka Hakan?" inji Aymaan yana kallonshi eye-in-eye
Qara Sakin shegen smirk dinshi yayi
"kanada abin ban Dariya, an ta6a fadamaka Hakan?" yafada shima yana kallonshi eye-in-eye
Murmushin dayafi kama dana takaici Aymaan yayi yace
"A'a, amma ba abin mammaki bane idan ka fadi Hakan don abinda zaiba mahaukaci Dariya ba lallai bane yaba kingin normal people ba"
"Careful now, don’t let your brains go to your head?"
Katse shi Aymaan yayi da
" Brains aren’t everything. In fact, in your case they’re nothing"
Dan murmushi mussadiq yayi yace
"you know what? Nasha wannan tunanin, I don’t know what makes you so stupid, but it really works"
" I’d explain it to you, but your brain would explode" inji Aymaan
Sunkuyowa mussadiq yayi gaban Aymaan wanda Hakan yaqara basu kusanci
"you know what? Anyone who told you to be yourself simply couldn't have given you worse advice.. So be yourself" ya miqe tsaye
Shima miqewa Aymaan yayi
"I do heed to advice, but if I Said advice.. I mean advice given By a sane being"
"sane or insane.. I don’t care, all I know is am advising you to stop sticking your nose into my business.. For your own Good"
Zai wuce Aymaan ya sha gabanshi
"and where did you think you're going? Am not done with you yet" inji Aymaan da kallo daya zakamashi kasan bala'i ke cin zuciyarshi
"yaya Aymaan..." batool data qaraso Tundazu tafara fadi Saidai kallon daya watsa mata yasata kasa idawa
Maida kallonshi yayi akan mussadiq dake kallonshi sheqeqe
"ba'a taka ko baki bakin gonata, meya kaika ra6arta?" inji Aymaan yana kallon mussadiq da bloodshot eyes dinshi, kallo daya zakamashi kasan baya cikin hayyacinshi, fushi ya fiddashi daga hayyacinshi kamar yadda yasaba yima masu haquri da aka kai bango
Yar Dariya mussadiq yayi
"yaushe ka chanza sana'a? Koma yaushe ne am sorry to say anci baya Sosai, From Likita to manomi"
"abin bazai ida baka mammaki ba sai na chanza daga manomin zuwa mafed'i"
"Yaya Aymaan, don Allah ka saurareni.. Please" inji zee da duk take a tsorace da yanayin kowannensu
Be kalleta ba ya cigaba da cewa
"answer me, wani tsautsayi yasaka ra6ar gonata?!" Yafada cikin qaraji
"yaya Aymaan please.. Look kallonmu akeyi" inji batool cikin tsananin tsoro
"ra6a? To ka jira, nan bada dadewa ba zan shige cikinta tsamo tsam.."
Naushin da Aymaan yakai mashi ya katse shi yayi saurin tarewa da hannu
Girgiza mashi kai mussadiq yashiga yi yana murmushi
"karka soma.."
Bangajeshi Aymaan yayi da dukkan qarfinshi wanda Hakan yasa yayi taga taga zaya fadi sai kuma yaci nasarar tsaida kanshi
Dagowa yayi ya kalleshi a fusace
"alright.. You'll get it"
Nufoshi yayi shima Aymaan ya Nufoshi suka cakumi juna
Kan kace me fada ya kaure aka shiga musayar blows🤜🏻🤛🏻
Wajen ne ya rikice don dama tunda suka fara hankalin kowa yadawo kansu.
Bugun juna sukeyi with all their strength kowanne na qoqarin huce haushin dan uwanshi daya dade danqare a zuciyarshi
Sosai jikin zee ke rawa, hannayenta rufe da baki hawaye na rige rigen gangarowa a fuskarta.
Dakyar mazan food canteen din suka samu suka 6an6aresu daga jikin juna kowannensu da irin ciwon dayaji a wajen dan uwanshi
Aymaan dayafi zuciya aka shiga qoqarin fitar dashi daga canteen din yana fizgewa yana zagin mussadiq da shima ake riqe dashi cikin canteen din
Dakyar aka samu aka fiddashi daga canteen din su zee na biye dashi suna hawaye
Fizgewa yayi daga riqonsu a fusace yana dakamasu tsawa akan su sakeshi
Sakinshi sukayi suna son ganin ko komawa zaiyi saiya juya ya nufi motarshi hannunshi daya dafe da kai
Saurin maramashi baya zee tayi
"yaya.. Yaya Aymaan please listen to me"
Ko kallonta beyi ba ya cigaba da tafiyarshi harya kai Wurin motarshi ya bude kofar
Riqe kofar itama tayi cikin kuka
"Aymaan ka saurareni mana.. You're going nowhere in this condition!"
Juyowa yayi ya kalleta da rinnanun idanunshi
"as if you care " yafada ahankali
" whatever yaya, just listen, I..."
Katseta yayi ta hanyar daga mata hannu sannan kuma ya Hade taffukanshi waje guda 👏
"spare me that.. Please"
Ya ida bude kofar yashige
"Akhie.." batool tafara
Jawo murfin kofar yayi ya rufe da qarfi sannan yaja motar da mugun qarfi yabar wajen
Bïñ motar sukayi da kallo devastated.
***
Tunda ya hau titi yake tsula wani uban gudu kamar mai gasar tsere, babu ruwanshi da bin dokokin hanya kawai kutsawa yake yana driving yadda yaga dama
Saida yayi nisa sosai sannan yasamu wuri ya gangara gefen titi yayi parking ya dora kanshi bisa sterring yana sauke numfashi ahankali
Ya dade ahakan sannan ya dago kanshi ya jingina da kujerar bayanshi
Tunawa yayi da yadda komai yafaru.
Hanya ce ta biyo dashi hanyar school dinsu, sai yaji babu abinda yakeson gani kamar ita saiya yanke shawarar shiga school din
Yana parking a inda ake parking yafito ya shiga makarantar
Harya fara shawarar ta ina zai fara nemansu sai kamar wasa ya hango batool tana ta sauri
Sunanta yakira da qarfi Hakan yasa ta tsaya tajuyo ta kalleshi
Wara idanunta tayi saita Nufoshi shima ya nufeta suka Hade a hanya
"ina zaki?" injishi
"Wani assignment zanyi sauri nabada"
"ina Zainab?"
"Tana food canteen, tarema muke assignment kawai zan bada nakoma"
"ok muje na rakaki sai Mukuma canteen din"
Tare suka je department din nasu tayi submitting sannan suka juyo suka dawo suka kama hanyar canteen din
Qarasawa bakin kofar wajen sukayi suka shiga
Idanunshi ne ya sauka a kansu suka yimashi mugun gani
Wannan marar mutuncin ne ya sunkuyo yana bata ruwa abaki tana sha
Saida tagama sha sannan ya ciro hanki yabata tana goge bakinta dashi
Mutuwar tsaye yayi Yayinda yaji komai na kwance mashi, zuciyarshi ta tasomishi har wuya yanajin kamar zata biyo ta baki ta fito waje and daga nan yayi loosing control har duk abinda yafaru yafaru
Haryanzu kuma be daina jin radadin da zuciyarshi ke mashi ba
Lumshe idanunshi yayi yafara ambaton allah a zuciyarshi har yasamu tadan yimashi sauki
Bude rinnanun idanunshi yayi yana furzar da huci sannan ya sunkuya ya dauki gorar ruwa wanda yasaba ajiyewa a gaban mota ya 6alle murfin ya kafa kai dukda ba wani sanyi garesu ba ya ida tuttula sauran a kanshi sannan ya qara Sakin nannauyan Ajiyar zuciya
Lalubo wayarshi yayi cikin aljihu ya Fiddota
Number Ahmad yashiga nema Saidai kafin ya ganota kira ya shigo wayar
*Ahmad* yaga yana yawo a screen din wayar
Wani numfashin yasake saukewa sannan ya daga kiran ya kara a kunne
"kana ina?" inji Ahmad ta cikin wayar
"ina nan" Aymaan ya amsa a taqaice
"to kayi maza kazo Aymaan I have a huge surprise for you please"
"Menene?" inji Aymaan moody
"kawai kazo please, its urgent, ina office idan kuma baxaka iya zuwa ba ka fadamin inda kake zanzo"
Jin seriousness din Muryarshi yasashi fara wondering meke faruwa
"ok, ganinan" yafada yana katse kiranshi
Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya sake tada motar yahau kan titi yaja wannan karon cikin normal speed
A parking space yayima motarshi matsugguni sannan ya fito daga cikinta ya rufe
Kallon harabar kamfanin su Ahmad din yayi sannan ya sake furzar da huci yafara tafiya yanufi ciki not minding yadda kayan jikinshi sukayi squeesing sukayi kaca kaca ga ruwan daya sheqawa kanshi dazu a mota, yadai koma gashinan dai kamar sabon kamu
Direct elevator yashiga ya danna floor din da office din