Showing 105001 words to 108000 words out of 322641 words
Chapter 36 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
tayi ta kalli mummy taga itama ita take kallo
"ki daga mana" inji mummy ganin wayar takusan tsinkewa
Kamar dama umarnin mummyn take jira saita dauki wayar ta daga kiran ta karata a kunne batareda tace komai ba
"Assalamu alaiki..."
Luu... Tayi baya baya ta jingina da kujerar datake akai kamar marar lakka tana lumshe idanu ta bude daidai lokacin da muryar tashi ta daki dodon kunnenta... ✍️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:36 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*037*
_jiya nayi mistake, *Ruma* cikin qaramar hukumar *BATSARI* take ba *6atagarawa* ba. Afuwan👏_
"Hello?"
Muryarshi taqara ratsa dodon kunnenta dama zuciyarta baki daya
Ahankali ta bude lumssasun idanunta ta saukesu akan na mummy dake kallonta itama
Saurin zabura tayi zaune don ita harga allah ma manta a inda take zaune
"hello" tafada tana miqewa tsaye
"excuse me mummy" tafada tana wucewa hanyar stairs da sauri
Mummy ba tace komai ba sai Binta datayi da idanu
"hello?" Deen yaqara cewa a karo na uku
"hy" zee ta amsa daidai tashiga daki ta maido kofa ta rufe
Sautin murmushin shi taji wanda ba qaramin tasiri yayi a gareta ba
"aslm alaiki"
Zamewa tayi ta zauna gefen gadonta tana shaqar numfashi ta fesar ahankali tana jin yadda 6acin ran data wuni dashi na fecewa ahankali yana bin iska
"wslm.."
Sai shiru ya biyo baya
Jin shirun na neman yin yawa yasata cewa
"yes? Who’s this?"
Sautin murmushin shi taqara ji sannan taji yace
"Kamal ne"
Itama murmushin tayi amma marar sauti tace
"Kamal?" tafadi sunan cikin wani salo da Saida Deen yakoma ya jingina da bangon dakinshi ya lumshe idanu
Jiyayi tasake cewa
"wane Kamal din?"
Murmushi yayi wanda tajishi sarai yace
"like seriously baki gane muryata ba? Deen ne fa"
Murmushi tayi cikin zuciyarta tace
'ko cikin muryoyi dubu naji muryarka saina tantanceta"
A zahiri kuma tace
"Oops! Deen? Dama naji muryar sounds familiar ashe kaine?"
Murmushi yasakeyi yace
"eh nine, good afternoon"
"afternoon, how you? Ina kakata?"
"lfy lau, kakarki na nan lfy lau ina mummy na?"
"mummy tana dakinta"
Murmushi taji yasake yi sai jitayi dama tana ganinshi taga smiling face din
"just call to say hello"
Murmushi itama tayi mai sauti tace
"thank you so much, how's weekend?"
"weekend alhamdullilah, zaki zo school on monday?"
"why not?" tafada tana jawo pillow tana rungumewa a qirji
"ok saimun hadu monday din" inji Deen a dayan bangaren
Ba haka tasoba don ita nan gyara zaman susha firarsu tayi amma ya ta iya?
"ok allah ya kaimu" tafada ahankali
"bye ki gaida min mummy"
"zataji nima ka gaida kaka"
"ok bye"
"bye"
Kittt... Taji an katse wayar
Lumshe idanu tayi ta Janye wayar daga kunnenta ahankali tana sauke wani nannauyan numfashi
Wani kayattacen murmushi ya su6uce mata tayi wani juyi a kan gadon wanda yakaita tsakiyar gadon ta kwanta rigingine still pillon a qirjinta
Number daya kirata dashi ta shiga kallo fuskarta dauke da murmushi
Latsa wajen adding contact tayi tayi saving din number shi da
_*D❤️*_
Sannan ta maida wayar ta rungume a qirji ta maida manyan idanunta ta rufe.
***
"kyakyawa na! Kyakyawa na!!"
Kiran da kaka keyi mashi yasashi ajiye wayar ya tashi ya fito
"kakata?" yafada yana qarasawa kitchen din datake
"maza ga abincinka nan ka dauka ka cinye ka kawo na qara maka"tafada tana nuna mashi kwanon abincin
Waro idanu yayi yace
"aqara kuma? Kaka wannan ai yayi yawa"
Dan harararshi tayi tace
"kuma saika cinyeshi ba, maza dauka bari na shinfida mana tabarma waje" tafada tana fita daga kitchen din
Tabarma ta fiddo ta shinfida daidai Deen yafito da abincinshi dana kaka
Zama sukayi kowa yaja abincinshi gabanshi sukayi bismillah suka fara ci
Can kaka ta dago tace
"yau za'a Saida wayar nan ko?"
Dago idanu Deen yayi ya kalleta sannan ya kada kai kawai
"yauwa ai gwara ayi a saidata ko mun samu jari, jiya kusan raba dare nayi ina tunanin yadda zamuyi dasu harna samu na yanke shawara
Idan aka samu kudinnan zan qara jarin kokon nan don dama sau dayawa ba isa yake ba kafin takwas ya kare azo kuma aita nema babu, kaga saimu qara yadda zamu dinga samu da dan kwari ko?"
Kada kai Deen dake aikin sauraronta yayi alamun gamsuwa
"Sai kuma wata shawarar dana yanke, mezai hana nafara siyarda dambu?"
Dagowa Deen yayi ya kalleta
"Dambu kuma kaka?"
"eh dambu, kaga da hantsi wajajen 12 haka zuwa azahar zanyi kuma naga babu masu yi anan unguwar sai inga kamar za'a samu alhairi, koko?"
"to kaka muda bamu ga kudin ba tukkuna"
"ai zamu gani ko? Ba yau za'a siyar daita ba?"
"eh"
"to? Ina wannan lissafin ne yadda komai zai qara zo mana da sauqi, kaga yanzu ba aiki kuke samu ba can wajen aikinku sai wannan yar sana'ar tawa ta koko ita ke dan taimaka mana ga kudin makarantarka don ma aski yazo gaban goshi kaga ya kamata mu qara himma ko kuwa?"
Deen dake sauraronta Tundazu ya kada kai ahankali zuciyarshi fall tunani kala2
Yasan tanada Gaskiya don yanzu sunfi raja'a akan abinda ake samu a sana'ar ta na koko da qosai don ba aiki suke samu ba sosai yanzu yawanci yan gyare gyare ne da kudinsu basu taka kara suka karya ba, ga kudin makaranta
Gaskiya so samu a siyarda wayar don zata taimaka sosai amma kuma bejin yana iyawa bawai don yana kwadayin riqeta ba don gayu ko wani abu, A'a kawai jiyake bazai iya siyarda kyautar da akayi mashi ba, kyautar kuma ta zee
"yauwa kayi da jiki ka gama kaga idan ka fita siyan geron gobe sai ku wuce kasuwar tsaitsayen ku sayar"
Da to ya amsa mata ya cigaba da cin abincin cikin sanyi, zuciyarshi fall tunani
Atare suka gama cin abincin ya kwashe kwanikan yakai kitchen din yadawo ya xauna kusada kaka dake qilga kudin dazata bashi yayi sayayyar
Saida tagama sannan ta bashi ya amsa ya tashi ya shiga daki ya dauki wayar yafito yayi mata saiya dawo ita kuma tabishi da adawo lfy
Koda yafito hanyar gidansu salmanu yayi Saidai kafin ya qarasa yaci karo da qannen salmanun nan yake Tambayar shi ina salmanun sai yace bayanan yafita
Hakan yayi ma Deen dadi sosai sai kawai yayi tafiyarshi kasuwa don yiwa kaka sayayya
Koda yadawo da batun wayar ta tareshi nan ya gayamata ai be samu salmanun ba shiyasa basuje ba
Bataji dadi ba Amma saita haqura akan ai akwai gobe, sai aje siyarwa goben
Deen kawai jinta yake amma bayajin zai iya Hakan don he valued the phone kamar yadda yake value mai ita
Da daddare bayan sun fito sallar isha'i Deen ya tari salmanu yayi convincing dinshi akan Koda kaka tayimashi maganar siyarda waya yasan abinda zai gayamata
Dayake salman dan maqocinsu ne kuma sunzo tsararraki da Deen kuma ba laifi suna mutunci sosai Hakan yasa ya amince bayan yagama tsokanarshi akan to ya tanaji kudin dazai biyashi na qaryar da zaiyi don buhari ya hana aikin banza
Shidai Deen Dariya kawai yayi sukayi musabaha ya wuto gida
Washegari ma haka yaita raina ma kaka hankali akan bega salmanu ba can dai taje gidan da kanta tabada sallahun idan salmanu yadawo yazo tana nemanshi
Dayake shima yasan kiran ko na menene be tashi zuwa ba sai bayan isha'i, sanin cewa babu halin zuwa lokacin saita cemashi yatafi yadawo gobe da marece zai raka Deen kasuwa
Da to kawai ya amsa ya tashi yayi tafiyar shi.
A bangaren zee kau yau ma haka taita jiran kiran Deen Saidai bata qwalaffa rai ba irinna shekaranjiya Saidai har dare babu kira babu alamun shi
Bata wani damuba don tasan gobe zasu Hade school Hakan yasata kwanciyarta hankali kwance wani barci mai shegen dadi yayi gaba daita
*MONDAY*
Tafiya take ahankali cikin tafiyarta data zame mata jiki
Bïñ harabar school din take da kallo ganin yadda yacika sosai yau don dama kowa wannan monday din ne harinshi
Qara gyara zaman gyallenta da iska ya saukoshi daga kafada tayi tana cigaba da tafiyarta
"Zainab..."
Taji an kirata daga baya wanda ko bata juyaba tasan mai kiran
Yitayi kamar batajiba ta cigaba da tafiyarta tana murmushi slightly
"Hey! Zainab.." taqara jin muryarshi na qara kusantota
Wani murmushin tasake saki tana dan daga gira daya sama batareda ta tsayaba
"Zainabbb!" taji a kusa kusa da ita da alama yana gab da ita
Sai a lokacin tafara slowing down ta juyo ahankali cikin son ganin wa ke kiranta
Deen din ne, sanye cikin baqin wandon jeans sai farar t-shirt mai zanen baqi a gaba, as usual sumarshi a dan tuje take dan akwai zirin dama ya biyo mashi ta fuska
Ganin shine yasata tsayawa tana kallon yadda yake ida qarasowa yana dan yatsine fuska
"my goodness Zainab, are you deaf?" yafada yana sauke numfashin saurin dayayi
Dan daga gira daya tayi cikin alamun tambaya shikuma daidai ya qaraso
"tun daga bakin gate nake kiranki amma bakiji, are you sure Kunnuwanta lafiya lau suke?"
Harararshi tadanyi suka cigaba da tafiya tace
"kokuma kaine za'ayi ma wannan Tambayar ba? Are you sure maqoshinka lfy lau yake? Dama tayaya zani jika da wannan voice din naka?"
"Allah da qarfi nake kiranki, cewa nake Zainab! Zainab!! But unknown to me ashe kurma ce"
Juyowa tayi tayimashi mugun kallo shikuma yadan matsa gefe yana Dariya
"Allah, gashi energy dina ya qare Wurin shouting"
"dama kanada energy din ne? Lazy bone" tafada tana dan Harararshi
"O'O! Am not lazy"
"O'O! You are" ta kwaikwayeshi
Kafin wani yasake magana a cikinsu sukaji daga bayansu ance
"hey! Ku biyunnan kuzo"
Atare suka juya daidai wanda ya kirasu din shima ya kallesu sai kuma ya dauke kai yana cigaba da Fiddo abubbuwan dayake fiddowa a booth din motarshi daya wuto da ita ciki sosai yadda kayan zasuyi dadin kaiwa office.
Kallon juna Deen da zee sukayi saikuma suka qarasa wajenshi kamar yadda yace
Deen ne cikin ladabi yafara cewa
"Good morning sir"
Amsawa mr ibrahim yayi batareda ya dagoba sai sannan itama zee ta gaidashi itama ya amsa mata batareda ya kalleta ba
Suna nan tsaye a bayanshi har yagama fiddo kwalayen daga booth sannan ya rufe ya juyo ya fuskancesu
"help me with these" yafada yana nuna masu kwalayen
"ok sir" inji Deen yana wucewa don daukar daya
Itama zee wucewa tayi Wurin qaramin cikinsu ta dauka sai jitayi ashe babu nauyi ma da alamu takardune ciki ko littatafai
"ga key, ka bude kushiga dasu ciki saiku dawo mu ida kwashewa" inji mr ibrahim yana miqama Deen key din office din
Amsa yayi sannan suka jera da zee suka wuce don kaiwa
Saida sukayi nisa sannan Deen cikin muryar rada yace
"mutuminki"
Kallonshi tayi tana dan Harararshi tace
"Amebo" itama cikin rada
Murmushi mai sauti yayi yace
"eh din"
Ajiye nashi kwalin yayi bayan sun qarasa ya bude office din zee tashige sannan shima yadawo ya dauki kwalin shima yashiga
Ajiyewa duk sukayi a qasa sannan suka fito yasake rufe kofar sannan sukayo hanyar dawowa
"guess ya haqura" inji Deen yanzu ma cikin rada dukda basuma shawo kwanar da zasu hangi mr ibrahim din ba
Daga kafadu zee tayi tace
"may be, maybe not"
"gashi nan ya kiramu"
"ai besan mune ba, bakaga reaction dinshi ba dayayi realizing nice"
"ni ban gani ba"
"dama ya xa'ayi ka gani da wadannan small small eyes din naka kamar na cinnaka🐜"
Dan 6ata rai yayi yace
"kekuma da naki big big eyes kamar na kwado🐸"
Dan wara idanun tayi
"nidin?"
"exactly"
Yitayi kamar zatazo wajenshi yayi saurin matsawa yana Dariya
Kwafa tayi tana murmushi suka shawo kwanar da zasu dinga hango mr ibrahim suka hangoshi tsaye yana magana da wani lecturern shima
Cikin rada zee tace
"yaushe kake ganin ya kamata na sake samunshi? Now?"
"No not Now, kibari zamuyi magana but not Now" yafada daidai sun qaraso wajensu mr ibrahim din
Gaida dayan lecturern sukayi sannan suka sake daukar kwali guda guda ya rage saura daya sukayo gaba
Kafin ma ya bude kofa sukaga shima mr ibrahim yataho da kwalin qarshe
Kafin ya qaraso har sun shiga sun ajiye yana isowa shima ya shigo ya ajiye yayi masu Godiya sannan ya sallamesu suka fito
"yanzu ina zaki?" inji Deen
"Sabon department dinmu ofcourse"
"kinje copying timetable?"
"No kaifa?"
"nima yanzu zanije"
"ok muje, Hakan ma yakamata nafara ko?"
"nima haka nagani"
Daga nan sai suka sha kwana suka kama hanyar inda ake liqa timetable suna tafe suna fira gwanin sha'awa
Tare sukayi copying din timetable din anan suka ga ashe duk basuda class yanzu
Zee sai 12pm saikuma na 2:30pm shikuma yanada na 1pm shima da 2:30pm.
Ganin Hakan yasa suka wuce library don a lokacin duka qarfe 10 da yan mintuna
Anan sukayi zamansu sunata fira har lokacin shiga lecture din zee yayi ta tashi tabarshi anan
Ganin Hakan yasashi daukar wani Littafi yana karantawa to wine time away, lokacin shigarshi class nayi shima ya tashi ya fice ya nufi sabon department dinsu
Zee tarigashi fitowa Hakan yasa tawuce cafteria ta siyamusu snacks ta dawo library din
Bata dade ba sai gashi shima yayi joining dinta
Tare sukaci abinda ta siyo din suna duba lecture din da suka dauka yau
Sai wajajen 2pm suka tashi suka nufi masjid gabadaya shi yayi bangaren maza ita tayi na mata
Koda suka fito classes dinsu duk suka wuce don duk sunada lecture a daidai lokacin
A kusan tare suka fito inda a lokacin har Motarsu zee ta qaraso
As usual sallama sukayi don Deen cewa yayi akwai abinda zaiyi ba yanzu zai tafi ba
Bata damuba itama sukayi sallama tashige mota bala yaja suka fice tanajin kanta cikin nishadi marar musaltawa
Haka ranaku sukaita tafiya masu, kodayaushe zaka gansu a school atare Saidai idan daya ya shiga class yabar daya, sosai wata iriyar shaquwa datafi tada tasake shiga tsakaninsu Agefe daya kuma wutar soyayyar Deen tana cigaba da balbala a zuciyar zee
Yanzu yana dan kiranta don wani sa'in yana kiranta sau daya a rana wani sa'in kuma sai bayan kwana biyu yake kiranta, itama tana dan kiran shi amma ba sosai ba kuma yasha bata kaka su gaisa ta waya
Duk yadda takejin soyayyar shi a zuciyarta tana iya bakin qoqarinta na dannewa tayi acting normal musanmman ma a gaban shi dukda wani sa'in Dakyar take iya controlling din emotion dinta
Sosai soyayyar shi ke qara hauhawa a duk kowacce daqiqa a zuciyarta abin har tsoro yake bata don wani sa'in har kuka take tana fargabar kar allah ya jarabceta ta wannan fannin don tasan ba qaramar wuya zatasha ba
A gida ma mummy tayi noticing chanji sosai daga gareta
Don yanzu kusan kodayaushe indai tana gida to batada Wurin zama kamar garden, can zataje ta xauna shiru ko ta buga tagumi tana kallon waje guda tana murmushi kamar ta6a66a
Wani sa'in ko a dining suke haka kawai sai takama murmushi tun abin na ba mummy mammaki har abin yafara damunta
A bangaren Deen kau haryanzu be furta soyayyar shi ga zee ba Saidai yana bata kulawar dake sata tantamar anya babu sonta a ranshi kuwa?
Saidai kuma data tuna waye Deen da abinda yake iyawa sai ta bar wannan tunanin don ba qaramin aikinshi bane ace duk kulawar nan babu sonta ko daya a ranshi kawai abota ce
Yanzu haka satinsu uku da komawa school, komai yana tafiya masu daidai a karatunsu musanmman ma zee don sosai Deen ke warware mata abubbuwan dasuka shigemata
Gashi sun shirya da mr ibrahim don taje ta sameshi personally tabashi hqr dukda Saida Deen yasha fama kafin ta yarda taje don sau uku ana saka rana sai ranar tazo taji bata iya zuwa daga qarshe dai Dakyar ya iya convincing dinta taje sai gashi mr ibrahim din ne gwasaleta ba kamar yadda take gudu yayi accepting apology dinta yakuma yimata nasiha
Hakan ba qaramin dadi yayi mata ba don jitayi kamar anyi lifting wani abu mai nauyi daga saman qirjinta
***
Yau friday, dawowarta daga makaranta kenan tashigo falon tana sallama qasa qasa tana jan qaffafu irin a gajiye dinnan Saidai wanda tayi tozali dashi yasata warwarewa nan take
"Aunty Feenah!!!" tafada cikin wara idanu sannan ta nufi Feenah da gudu ta fada jikinta tana dariyar murna
Itama Feenah riqeta tayi cikin Dariya tana cewa
"ji yar rainin hankali zata qaryani, ni abokiyar wasarki ce?"
Mummy dake gefe zaune tace
"hmm ai indan wannan ce kadan ma kika gani"
Dagowa zee tayi still tana Dariya tace
"wai dama yau zakizo shine baki gayamin ba? Gaskiya banji dadi ba" tafada tana so6ara baki
"to idan ma gayamiki wani abu zaki yimin? Kema ba daga sama ba naga kin fado gidanmu ba?"
"oh ramawa kikayi kenan?"
"qwarai kuwa"
Dariya tayi tace
"babu komai ai, tsakanin uwa da 'ya sai allah, ina kayan ki nashigar miki dasu ciki dukda ni ba'a shigarmin da nau ba"
Yi Feenah tayi kamar zata maketa tayi saurin miqewa ta nufi stairs tana Dariya
Kwafa Feenah tayi tana cewa
"zanyi maganinki ai tunda naga kin maisheni kakarki"
"ai kunfi kusa, dama zani ce ta tarda muje don kaff babu abinda tabari a halin ki" inji mummy
"kai yaya, wlh nafi Zainab hankali" inji Feenah tana turo baki
"kindai fita" mummy ta amsa tana Dariya
*10:30pm*
Sake dagowa tayi daga wayarta datake danne danne daita ta sake kallon Aunty Feenah data juya mata baya tana waya cikin yin qasa da murya sosai don ko zee dake kwance kusada ita bata jin abinda take cewa
Sai jitayi ta bata sha'awa har itama tana hasaso kanta tana waya da Deen dinta
Tunawa tayi da yadda suke waya, sunyi gudun tsiya suyi 5mins suna waya amma Tundazu take duban agogo awon Aunty Feenah daya da kusan rabi suna waya
_ko me suke cewa?_ abinda ta tambayi kanta kenan saikuma ta ta6e baki ta cigaba da danne dannenta
Saida Feenah taqara daukar 15mins kafin suyi sallama da saurayin nata ta juyo ta kalli zee datayi nisa a wayarta tana downloading wata waqar hamisu breaker
Fizge wayar Feenah tayi tana cewa
"dawa ake charting?"
Tashi zee tayi zaune da sauri tana cewa
"wayyo Aunty dan allah karki datsemin yakusan Shigowa"
Jada baya Feenah tayi tana Dariya ganin tana qoqarin amsa ta daga wayar sama tana dubawa
"Yadda kunne yaji? Menene wannan?" inji Feenah tana yatsine fuska
"Wata sabuwar waqar hamisu breaker ne, naga gajeriyar video dinta a status dazu sai naji ta burgeni shiyasa nake downloading"
"mtcheew! Ni dalla amsa, namayi tunanin dashi kike charting"
Amsa tayi tana Dariya
"da wa?"
"bansaniba yar rainin sense"
Dariya zee taqara yi
"wai Deen? Bana tunanin yana charting"
"why?"
Daga kafadu zee tayi
"qila ra'ayi"
Ta6e baki