Showing 279001 words to 282000 words out of 322641 words
Chapter 94 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
don basu damar shigowa
ummie dake murmushi tace
"fara dai gayama masu gidan abamu izini tukunna"
dasauri batool tajuya takoma falon ta sanardasu mummy
suma sunyi mammaki nan suka cemata tashigo dasu kowacce na qoqarin yafa mayafinta
da sallama ummie dake gaba tashigo Aysha abayanta
rungume juna sukayi da batool da Aysha cikin murnar ganin juna
ganin su Mussadiq na qoqarin shigowa yasa batool dan nutsuwa
kallonsu tayi, su biyun sanye da kaya iri daya baka ko iya banbancesu itama batool ta sumar kansu ta iya gane Deen aciki
kallo daya tayimashi tasan he's so nervous dubada yadda beson ko dago kai
habeeb ne ke bayansu wanda shima sanye yake cikin qananun kayanshi masu kyau
gabadaya ta gaidasu tana jan Aysha gefe don subasu wurin wucewa
amsawa sukayi saidai har lokacin Deen be dago ba ahaka suka shige falon
ganin hakan yasa suma shigowa Aysha nama batool rad'an ina zee itama tana bata amsa acikin rad'a cewa tana sama.
koda suka shigo falon sai suka iske duk sun zazzauna anata gaisawa hakan yasasu suma qarasowa suka zauna Aysha tashiga gaidasu ummy.
saida batool ta gaida ummie tasake gaidasu Deen sannan ta tashi tayi kitchen domin kawomasu abin motsa baki
Akan stool din kowacce kujera ta ajiye musu sannan takoma ta zauna kusada Aysha
cikin mutuntawa sosai da fara'a su ummy ke gaisawa Inda suma su Mussadiq suka gaishesu cikin girmamawa
shidai Deen duk Abinda akeyi yakasa sakin jiki kwata2 don ko dagowa beson yi, sosai yakejinshi atakure musanmman idan yanajin muryar mummy
tunanin cewa zee na cikin gidan nan ya hanashi sukuni ko kadan.
ummy takira Abbu Inda take sanardashi zuwan baqin nasu
ba'a jima ba kau saigasu Abbu da daddy suma sun shigo falon.
nan aka shiga sabuwar gaisuwa cikin farinciki da walwala
suma yan samarin suka shiga gaidasu cikin girmamawa sukuma suna amsawa cikin kulawa suna masu barka dasake saduwa
duk wannan abin da akeyi har lokacin Deen yakasa dagowa yayinda shikuma daddy yakasa janye idanunshi akanshi kwata2
anan ummie tashiga yimasu godiya sosai akan Kasancewarsu silar sake haduwarsu da Mujaheed dasuka dade da fidda rai dashi
anan tashiga basu labarin yadda rabuwarsu ta kasance cikin hawaye da yadda hakan yayi silar mahaifinsu kuma mijinta
kowa saida ya tausaya mata don sosai labarin ya ta6asu dukda sun sanshi dama
godiya taita yimusu har abin yaso yin yawa tana nuna tsantsar godiyarta agaresu hawaye a fuskarta
dakyar suka samu tayi shiru sunata rarrashinta da yimata,nuni da ta godewa allah donshi ya tsara komai a yadda yafaru dinnan suma ba wayonsu bane ko dabararsu
anan Kuma aka shiga fira wanda duk ta Kaka ce kowanne nakawo ra'ayinshi akanta Inda suka kasa tsayar da matsaya akan ko ita ta saceshi din kokuma tanada alaqa da 6acewarshi
anan aka buqaci Deen yabasu labarin iya zamansu daita
dukda halin dayake ciki na uneasiness haka yabasu labarin rayuwarshi tun tasowarshi daya bude idanu yasan Kaka
babu komai a labarin sai tsantsar kulawa da qauna da Kaka keyimashi
nan kansu yaqara kullewa suka rasa a wane matsayi zasusa Kaka
dole idan sunason wannan chakwakiyar ta warware su samo Kaka don ita kadai zata iya warware masu wannan sarqaqiyar
nan suka shiga shawarar yadda zasu samu Kaka
dafarko akace sukoma Nigeria suje su isketa amma firr ummie taqi yarda tace bazata ta6a barin Deen yaqara nesa daita ba saidai sutafi tare
haka sukaita shawarwari har daga baya suka samu mafita Inda Deen yabasu tabbacin Kaka zatazo nan Dubai dakanta
dasuka tambayi tayaya sai yace abar komai a hannunshi yasan yadda zaiyi.
ahaka suka cigaba da tattaunawar har zuwa wani lokaci
anan ummie tashiga tambayar ina zee
nan akace tana sama, sai ummy tasa su batool suje sutaho daita halan batasan da zuwansu bane.
tunda aka ambaci sunan zee Deen yaqara rasa yar nutsuwarshi
bugun zuciyarshi ce ta sauya yayinda wani feeling mai tsuma jiki ya mamayeshi
sauke kanshi yayi qasa ya cigaba da sauraron firar dasu ummie keyi sama sama yayinda duk hankalinshi da nutsuwarshi suka tattara sukayi hanyar dayaga su batool sukayi, dukda ba kallon wajen yake ba amma gabadaya hankalinshi na wajen.
ahankali bugun zuciyarshi tafara sauyawa tana yin doubling
ahankali yashiga murza taffukan hannunshi together kamar mai son yin maganin sanyin nan
sosai tsigar jikinshi ke tashi yanajin kamar ya dago amma yakasa dagowar
ahakan ya tsinkayi muryar da kunnuwanshi suka jima suna bege da marari, muryar da sai yanzu yasan iya adadin kewar dayaimata
"Ummie" yaji tafada cikin zazzaqar muryar da har yanzu beji mai irinta ba
cigaba dazuwa mashi muryar tayi cikin gaisawar dasuke da ummie
kasa riqe kanshi yayi daga qin dagowa
ahankali yafara dago oily eyes din nashi kamar wanda ake controlling da remote
daidai nan itama ta kallo wajen kamar tasani
caraff oily eyes dinshi ya sarqe da nata large pure white eyes din...✍?
*ga post din dare😆 nasan wasu harsun fidda rai🙁*
Ummin Fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*088*
Qirjinsu yabada damm lokacin da idanun nasu suka gauraya dajuna
ko seconds biyu batayi ba tana kallonshi ta janye idanunta ta maidasu akan ummie dake mata magana
murmushi tayi tadan sunkuyar dakai Jin yadda ummie keta mata godiya itama
cikin murmushi zee kecewa babu komai ai allah shine abin godiya
kasa janye idanu Deen yayi akan zee, gani yake kamar mafarkan daya sabayine kamar ba dagaske ita yake gani ba
komai nata nanan
her geogous smile, her melodious voice, her breathtaking beauty
sanye take cikin wata doguwar hijab harqasa milk colour, fuskarta babu makeup sosai amma she looks so cute
ahankali yakejin yadda zuciyarshi ke melting in emotions ga yadda zuciyarshi ke bugu sosai linkin yadda takeyi ada
A bangaren Mussadiq ma ita yake kallo dan murmushi na forming agefen bakinshi wanda duk kwakwarka baka iya gane yanayi saishi dakeyin abinshi
yadda zee ta basar ta hanyar avoiding qara kallon gefensu yabashi dariya, irin wannan dabi'un nata na Jin kai da class yasa tunfarko tafara burgeshi
ahankali yayi gyaran murya sannan yace
"hyy good afternoon"
ko bata juyo ba ta gane mai muryar kuma tasan daita yake amma saitayi kamar bata saniba don saima kallon Aysha tayi cikin murmushi tana mata magana
"yaya namiki magana ummie" inji Aysha tana nuna Mussadiq
da qarfi tayi maganar so kowa yaji hakan yasa zee juyawa ta kalli saitin data nuna
maimakon idanunta sufada akan Mussadiq din saisuka sake sauka Acikin na Deen da haryanzu ita yake kallo
saurin sake janye idanun tayi tana jin yadda zuciyarta taqara bugawa da qarfi
"hmm hyy" tafada ahankali batareda taqara kallon gefensu ba
"thanks so much for your effort, words can't express our gratitude to you, jazakillah biljannah" inji Mussadiq yana kallonta
"amin, thanks too" ta amsa batareda tasake kallon gefensu ba
saikuma ta tashi tsaye kamar wadda ke kan allura ta riqo hannun Aysha
"let's go upstairs" tafada tana janta
"gulma zakuje yi ko?" inji ummy cikin tsokana
dariya Kawai sukayi suka tashi su ukun sukayi hanyar sama suka haye.
ta qasan ido Deen yabisu da kallo harsuka haye saman
wani sad feeling yaji ya mamaye zuciyarshi
ahankali ya lumshe idanunshi ya bude yana jin wani daci daci a maqoshinshi
sama sama ya cigaba da sauraron firar su ummie jiyake kamar yatashi yafita ko yadanji sauqin Abinda yakeji a zuciyarshi idan yashaqi iskar waje
kamar Mussadiq yasan meke ranshi sai ji Deen yayi yana excusing kansu akan cewa zasu dan fita waje
jin sun amince yasa Deen saurin miqewa kamar dama akan qaya yake sauran ma suka miqe suka fice wajen atare
wajen qarafunan da aka qawata entrance din yanufa yana dafawa yayi inhaling iskar dake kad'awa mai sanyi sannan yafesar
qarasowa Mussadiq da habeeb dake bayanshi sukayi suma
shiru wajen ya dauka yayinda Deen yakafe harabar wajen da kallo da idanunshi dasuka sauya launi
abun da matuqar ciwo ace kuna under roof daya da wadda kake matuqar so da bege amma ko kalma daya takasa shiga tsakaninku
ga yadda yaga tanayi ma kamar batama ganeshi ba don ko kallon kirki batayi mashi ba, she looks so okay and calm kamar ma ganinshin be tunamata da komai ba
kodai dagasken tayi aure ta manta dashi?
tayiwu nan din gidansu mijinta ne, tayiwu Abbu da ummy iyayen mijinta ne, then waye mijin?
daidai nan sukaji anyi horn abakin gate
atare duk suka kalli saitin gate din daidai lokacin da shima maigadi yaruga don zuwa budewa
cigaba da kallon wajen sukayi har aka bude gate din
wata ash colour mota ta danno kai tashigo ciki
direct parking space tanufa tayi parking
kauda kai Mussadiq yayi yana dan ta6e baki don ko ba'a fada ba yasan ko waye
bude kofar akayi a bangaren driver aka fito sannan aka maida aka rufe
da kallo Deen yabi aymaan daya zagayo ta dayan side din motar ya bude backseat ya fiddo briefcase dinshi
maida kofar yayi yarufe ya kulle motar sannan yajuyo hannunshi daya riqeda briefcase dayan kuma rataye da farar lapcoat dinshi
hada idanu sukayi da Deen dake kallonshi har lokacin
Dan dakatawa aymaan yayi da tafiyar don beyi expecting ganinsu ba saikuma ya cigaba da tahowa yana janye idanunshi daga na Deen
Deen dai cigaba da kallonshi yayi har ya qaraso, babu irin tunanin dabaizo mashi ba arai akan aymaan
ganin ya kusan qarasowa yasashi dan janye idanu shima yana dan lumshesu yana Jin yadda zuciyarshi kemashi wani irin zafi
da sallama aymaan ya qaraso wajen yana Dan kallonsu
atare duk suka amsa suna dagowa suna kallonshi banda Mussadiq daya juyar dakai ma dukda shima ya amsa sallamar
"likita bokan turai" inji habeeb cikin washe baki
murmushi aymaan yayi yace
"kune agidan namu?"
"eh wlh barka da dawowa" inji habeeb yana Bashi hannu
musabaha sukayi aymaan na amsawa da barka dai
shima Deen danne zuciyarshi yayi yadanyi forming murmushi yabashi hannu
"welcome" yafada ahankali
"welcome too" aymaan yafada sunayin musabahan
"why are you here?" inji aymaan batareda yako kalli gefen Mussadiq ba bare su gaisa
"yanzu muka fito ai" inji Deen
kafin susake magana sukaji muryoyin su ummy zasu fito
duk atare suka juya daidai lokacin dasu ummie suka fito harda su zee suna fira cikin wasa da dariya
"A'a Dr, andawo?" inji ummie don ta shaidashi
murmushi yasaki sannan yadan matso yana gaidata cikin girmamawa
amsawa tayi cikin kulawa tana tambayarshi ya aiki
da alhamdulillah ya amsa yana tambayarta ya qarfin jiki
amsa mashi tayi da da sauqi sosai ko bega alama ba
cikin dariya yace eh yaga alamu ma ba alama bama kadai
duk dariya sukayi banda Deen da Mussadiq da abin bewani basu dariya ba
shidai Deen sai kallon aymaan yake akaikaice yakasa janye idanu akanshi
Kasancewar idanunshi na akanshi yasa yaga lokacin da aymaan ya dagawa zee gira daya itakuma tayi murmushi shyly tana kauda kai
shima murmushin yayi yana binta da wani kallo
sauke idanunshi Deen daga kansu yana jin zuciyarshi na yin jingim, jiyake kamar an doramashi qaton dutse akai
itadai Aysha bata ma yarda suka hada idanu da aymaan ba don sai kauda kai takeyi
tunda talura da yadda yake wani shasha mata qamshi yana hade haden rai idan yaganta ta yanke shawarar fita sabgarshi itama
sallama ummie tashiga yimasu bayan ta amshi address dinsu Ahmad akan suma zataje hargida tayimasu godiya, dama kuma already sunyi exchanging number akan zasu dinga kiran juna akai akai akan maganar Kaka
har wajen motarsu suka rakasu Inda anan ummie tasa su Mussadiq suka fiffidomasu kayan dasuka zomasu dasu
dafarko sunso qin amsa suna cewa yayi yawa gashi dama sun hado su aymaan da tilin kaya jiya
nacewar da ummie tayi yasa akan dole suka amsa suna masu godiya sosai
Nan sukayi sallama cikin aminci da fara'a kamar wadanda suka dade dasanin juna
itadai zee tuni takoma ciki don tunda suka tsaya jayayya akan kaya ta silale ta fece
suna nan har motar tasu ta tashi maigadi yabude masu gate suka fice
da taimakon su aymaan suka kwashi kayan dasu ummie suka kawo suma suka koma ciki
***
cigaba da kai kawo yake waya kare a kunnenshi, kallo daya zakamashi kasan cewa yana cikin damuwa sosai don sosai hakan ya bayyana a fuskarshi
haryanzu amsa daya ake bashi, lambobin dayake kira kwata2 basa shiga
Ajiyar zuciya ya sauke yana sauke wayar daga kunnenshi sannan yajuyo ya kalleta
tana nan Inda take buga uban tagumi, idanunta harsun gaji da zubar da hawaye
"innalillahi waina ilaihi rajiun.. meke faruwa ne haka? wlh haryanzu babu wayar kodaya acikinsu datake shiga" inji Alhaji Bashir cikin tsantsar damuwa
"innalillahi waina ilaihi rajiun, allahuma arjini fi musibati, wannan wane irin abu ne? kuma harda number abokin naka dayaje wajenshi din bata shiga?" inji mami dake zaune kusada Kaka cikin damuwa
"wlh harda ita, I don't know what's going on. dukkansu nambobinsu bata shiga" inji Alhaji cikin damuwa
qara fashewa da kuka Kaka tayi cikin dakussashiyar muryarta wadda tagaji da kuka
"dama saida raina yabani, saida naji banason tafiyar nan saida naji ajikina tafiyar nan ba alhairi bace, yanzu gashi ta tabbata
innalillahi waina ilaihi rajiun, yanzu ina zansakaina ni ma'u? ya zanyi da rayuwata? wlh bazan iya rayuwa babu kyakyawana akusadani ba, wlh mutuwa zanyi" saikuma tafashe da matsanancin kuka
Lailah dake kusada ita da damqe hannunta itama tana hawaye
tun shekaran jiya wancan suke cikin tashin hankali
kwata2 number Deen dana habeeb sunbar shiga gashi shekaran jiya yakamata sudawo amma haryanzu shiru
babu su babu alamunsu ga numbersu bata shiga
jawo Kaka mami tayi ajikinta tashiga bata baki tana kwantar mata da hankali amma yadda kasan qara zugata takeyi
"banida kowa saishi, shima beda kowa saini. tunda ya bude idanu duniya ni kadai yasani nashi, bayan ni besan kowa ba
bayada hayaniya, babu ruwanshi da kowa meyasa ake bibiyarshi da sharri?
dama ni ban yarda da wannan abokin nashi dayace zaima aiki ba, aiki ace harsai kabar qasarka kaje Inda bakasan uban kowa ba? ai daji ba alhairi bane
gashi beda lafiya, akasi kadan za'a samu ciwonshi na namonia (pneumonia) yatashi kuma idan yatashi dakyar yake sha kamar bazaiyi rai ba haka yakeyi
abu goma da ashirin duk suntaru sun hau kanshi ya akeson yayi da rayuwarshi?
yanzu haka muggai ne azzalumai sunsa yafito yazo qasarsu Inda babu yadda zaiyi dasu, yanzu yazanyi idan wani abu yasamu Kamal? yazanyi da rayuwata?"
duk cikin kuka sosai take wannan xancen, tsabar kukan datasha muryarta ma bata fita sosai don tun shekaran jiya take abu guda ko abinci bata iyaci saboda tashin hankali
"kiyi hqr Kaka insha allah babu Abinda zai faru dasu, ki kyautata masu zato na tabbata wani akasi akasamu qila amma insha allah zasu dawo cikin qoshin lafiya
Kuma karki manta baban yaron abokinane, tsohon abokinane damukayi primary da secondary dashi daga baya kuma aka rarrabu insha allah mundin yana taredashi babu Abinda zai faru dashi na cutarwa" inji Alhaji cikin son kwantar mata da hankali
"tsohon abokinka? tsohon aboki fa kace, waya san meya zama bayan rabuwarku? Kawai daga kunyi firamari da sakandiri atare shikenan saika yarda dashi kusani tura jikana wajenshi? wayasan meya zama bayan rabuwarku? ai muggayen mutane.sai daga baya suke zama mugaye bawai la'akari za'ayi da yarintarsu ba"
"yanzu dai insha allah daga nan zuwa gobe xan tabbatar nasamo mana information.ko yaya ne akansu, don allah ki.kwantar da hankalinki Kaka, jifa yadda kika koma ko abinci fa bakya ci sai aikin kuka. Balarabe yanzu babu Abinda yafi buqata wanda yafi addu'a, ki kwantar da hankalinki Kaka" inji Alhajin cikin rarrashi
"kiyi hqr Kaka mu cigaba da kyautata musu zato.insha allah zasu dawo garemu cikin qoshin lafiya, mu cigaba dayimasu addu'a insha allah zasu dawo garemu cikin aminci" inji mami
haka dai suka taru sunata rarrashin Kaka da kwantar mata da hankali
Lailah kau na gefe itama damuwa ce rubuce koina a fuskarta, bata jin tana iya jurewa idan wani abu yasamu Balaraben ta, fatanta allah ya kareshi aduk Inda yake ya maido masu shi lafiya.
***
Washegari su ummie sukaje gidansu Ahmad Inda su shigar dare ma sukayi musu don saida suka ma kirasu saboda dama sun amshi contact dinsu awajen su abbu
sosai su iyayen Ahmad sukaji dadin zuwan nasu Inda anan sukayiwa juna tarbar mutunci
godiya sosai ummie tashiga yimusu suma tana samasu albarka musanmman ma Ahmad
sosai suma suka nuna babu komai ai d'a nakowa ne suna kuma tayasu murnar sake saduwa
Ahmad kau fita dasu Deen yayi waje Inda suka samu wani tent sukayi zamansu suna fira
abin mammaki saigashi tasu tayi saurin zuwa daya da Mussadiq don nan da nan suka jiki da juna
kan kace me sunyi nisa a firarsu wanda mostly ta Abinda yashafi aikinsu ne wato Business
shidai Deen becika sakamasu baki ba don mostly besan akan me suke magana akai ba daga baya ma tashi yayi ya koma gefe ya tsaya yana bin harabar gidan da kallo yana feeling daddadan iskan dare dake kadawa
gabadaya daga jiya zuwa yau duk ya chanza yakoma kamar bashi ba
sosai damuwa ta bayyana a tattare dashi dukda iya bakin qoqarin dayakeyi na 6oyewa
yakasa mantawa da image din Zainab, zuciyarshi taqi bashi sukuni dukda yana tunanin da aure akanta kuma auren wannan likitan
yasan indai har tanada auren what he's doing was wrong don it's very wrong kadinga tunanin matar wani
saidai yarasa dalilin dayasa yakasa tankwara zuciyarshi akan haka don with every passing minute tunaninta qara addabarshi yake soyyayarta kuma qara qaruwa takeyi
hakan yasa duk yabi ya susuce yarasa Abinda kemashi dadi
ahakan har lokacin tafiyarsu tayi suka kamo hanyar gida
a hanya ummie taita tambayarshi meke damunshi don duk yadda yake qoqarin 6oye damuwarshi musanmman ma agabanta saida tagane yana cikin damuwa
murmushi Kawai yakeyi yace babu komai yagaji ne Kawai
haka ummie ta kyaleshi ba don ta yarda gajiyar bace saidai bata takura mashi ba suna isa gida ta kadasu part dinsu wai suje su kwanta tunda duk agajiye suke musanmman ma Deen din
koda suka shiga part din nasu duk shirin barci sukayi kowa yanemi lafiyar gado ya kwanta bayan sun.kashe wuta
Deen dai dama ba barci yakeji ba don haka kwance yake Kawai staring to dark space
ya dade sosai ahakan don dare yayi ma sosai don koina yayi tsit, kamar.daga sama yaji muryar Mussadiq nacewa
"she's not married"
shiru ya ratsa dakin nawani lokacin kafin wutar bedside lamp yakawo sanadiyar kunnawa da Deen yayi
"bakayi barci ba?" inji Deen yana kallon side din Mussadiq Kasancewar kowa dama da bed dinshi
sai alokacin Mussadiq yajuyo daga juyamashi bayan dayayi
"kaima ai bakayi ba" yabashi amsa
"me kace yanzu?" inji Deen
"nace batayi aure ba" Mussadiq yabashi amsa
shiru Deen yayi yakura mashi ido for sometimes sannan yace
"tayaya akayi kasani?"
"Ahmad ya gayamin, she's not married amma she will be soon idan kayi sake" yafada yana gyara kwanciyarshi
shiru Deen yasakeyi na wani lokaci
dagaske batada aure? kenan he still has another chance? amma meyasa yace zatayi soon idan yayi sake?
"meyasa kace hakan?" inji Deen
"saboda akwai masu harinta" Mussadiq yabashi amsa
"masu harinta? su waye?" inji Deen yana kallonshi beson ko dauke ido akanshi
"kai yanzu baka gane wannan annoying likitan sonta yake ba?"
"ni dafarko nayi tunanin shine mijin nata ai"
kya6e baki Mussadiq yayi
"Zaidai zama idan kayi sake, sonta yake na dade dasanin hakan kuma he can do anything to win her heart don haka kanada babban aiki agabanka"
shiru Deen yayi yana tunani
yes it's possible ace aymaan son