Showing 291001 words to 294000 words out of 322641 words
Chapter 98 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
rana za'ayi ba hakan besashi doqin ranar ba don gani yake wannan Introduction din sharen fage ne na mallakar zee tunda koba komai za'a tsaida magana ne akansu yadda koma wani yazo daga baya yana sonta akwai maganarshi akanta
sosai cikin yan kwanakinnan Deen yadage da buga buga duk don yasamu yatara kudin daza'akai Introduction din hakan yasa shima yabar zuwa school din akan da anyi Introduction din saisuyi resuming school din gabadaya dashi da zee
besan ya tsarin abin yakeba amma yasan ba'a zuwa hannu biyu neman aure
wannan busyn daya shiga yasa beda lokacin lurada halin da kaka tashiga ciki
*TWO DAYS TO THE INTRODUCTION*
Zaune kaka take tsakar gida kan tabarma ta miqe kaffafunta ta hardesu tana kalkadawa ahankali
kallo daya zakamata kasan cewa she's very disturbed
kafe hanyar shigowa gidan tayi da ido kamar mai jiran 6illowar wani yayinda saqe saqe da dama keta kai kawo a kwanyarta
da sallama Deen yashigo gidan wanda hakan yayi daidai da saukewar naunauyan ajiyar zuciya daga kaka
murmushi yasakar mata lokacin daya hangota yaqaraso ciki hannunshi riqeda yar baqar leda
cigaba da kallonshi kaka tayi batareda ya motsa ba harya qaraso ya zauna gefenta yana washh yana yatsine fuska alamun gajiya
"wlh kaka nagaji, jikina ciwo" yafada yana qara yatsine.fuska
jin shiru yasa yadago ya kalleta yaga itama shi take kallo
"kaka?" yafada ahankali yana kallonta
hakan yasata kauda kai wadda hakan yaba kwallar idanunta damar digowa
ganin digar hawayen yasa hankalin Deen tashi nan take yanemi gajiyar tashi yarasa
"subhanllilah, kaka menene? meya faru" yafada yana kamo hannunta zai juyo fuskarta don tabbatar da abinda yagani amma taqi bari
"kaka don allah menene?" yafada yana qara qoqarin leqa fuskarta
fizge hannunta dake cikin nashi tayi tarufe fuskarta da tafukkan hannu tareda fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya
gaban Deen yayi mummunan faduwa ganin dagaske kuka take hakan yasashi saurin rarrafowa gabanta ya kama hannayenta zai janye daga fuskarta amma taqi bari
"innalillahi, kaka wai meya faru? don allah kiyi magana" yafada cikin tashin hankali
qin maganar tayi saima qara volume din kukanta datayi wanda hakan ba qaramin daga hankalin Deen yayi ba don jiyayi kamar shima yasa kukan
"kaka don girman allah ki gayamin meke faruwa, don allah kiyi shiru ki gayamin, don allah" yafada kamar zaiyi kuka don har idanunshi sunfara chanza launi
nan ma batace komai ba sai kukan data cigaba dayi wanda yakeji har cikin ranshi
"kaka don allah ki gayamin, don allah kibar kukan nan zuciyata zata buga" yafada muryarshi na dan rawa rawa
sai a lokacin tadago ta kalleshi fuska sha6e sha6e da hawaye
"Kamal nima zuciyata zata buga, zasu rabamu, xan rasa raina. zamu rabu na har abada"
"innalillahi waina ilahi rajiun, rabuwa kuma? haba kaka meyasa kike fadin wannan mummunan kalmar? don allah kibar fadin haka"
"Kamal kaine komai nawa, baxan iya rayuwa babu kai ba baxan juri nisa dakai ba, mutuwa zanyi" taqarashe cikin fashewa da kuka sosai
hawayene suka taru a idanunshi shima
"kaka don allah kibar fadin haka, babu wanda zai rabamu, nima bazan iya rayuwa babu ke ba..."
"to idan hakane mu gudu Kamal.. mubar nan wajen, mubar garinnan don allah" ta katseshi dasauri kamar zautatta
tsayawa Deen yayi yana kallonta for a moment kafin yace
"mugudu? kamar ya mugudu?"
"mubar nan Kamal, nidai hankalina be kwanta da nan ba kuma, ina tsoron kar arabamu ina tsoro Kamal" tafada cikin yanayin tsoron
"wazai rabamu kaka? waye zai rabamu" inji Deen in confusion
"nidai mubar nan Kawai... tashi kagani, taso" tafada tana miqewa tsaye tana jan hannun Deen da kanshi yayi mugun kullewa
tashi shima yayi tajashi har dakinta yana biye daita suka shiga
"kagani? na tattara komai tafiya Kawai yarage, Kawai mutafi don allah"
tsayawa yayi yana bin jakunkunan kayansu dake tsakiyar dakin da kallo Speechless, yama rasa meke faruwa
"da daddare saimu tafi Kawai yadda babu wanda zai ganmu ko?" inji kaka da hawayenta yaqi tsayawa ga jikinta har lokacin rawa rawa yakeyi
dakyar Deen ya iya tattaro yawun bakinshi ya hadiye.sannan yace
"kaka.. wai meke faruwa ne? ina zamu?"
"koina ma,.Kawai muyi nisa danan"
"amma akan wane dalili kaka? Kawai saimu bar gari haka Kawai? haka Kawai saimu gudu mubar gari kamar 6arayi" yafada totally confused
"Kamal, bazaka ganeba amma ni nasan abinda na hango, wlh inaji ajikina idan muka cigaba dazama anan sai an rabamu, inajin hakan ajikina" tafada wasu hawayen nasake saukomata
"wazai rabamu kaka?"
"nima bansaniba Kawai mubar nan"
"amma kaka shikenan saimu bar gari? ina zamuje? wa mukedashi? wani wurin garemu bayan nan?"
"Kamal zamu samu wurin zuwa, nan ma ai sdaga wani wuri mukazo kuma muka samu nan din har muka zauna mukayi tsawon shekarunnan, mutafi insha allah zamu samu wurin zuwa allah na taredamu"
"amma kaka karatuna fa? bama wannan ba kin manta jibi za'aje tsayar da maganarmu da Zainab? duk ahakan zamu bar gari?" inji Deen dake cikin confusion sosai, kwata2 magangganun kaka doesnt make sense to him
"duk ina sane da hakan Kamal, duk wadannan basuda muhinmmanci yanzu"
"basuda muhinmmanci?" ya tambaya cikin tsananin mammaki
"eh Kamal, abinda yafi muhinmmanci shine mucigaba da rayuwa da juna..atare"
shiru Deen yayi yana kallonta kamar yau yafara ganinta saikuma ya girgiza kai yakama kafadun kaka da hannun bibbiyu ya zaunar daita gefen gadonta
"kaka meya faru? don allah ki gayamin meye silar dukkan wadannan abubbuwan"
"babu komai Kawai sonake mubar garinnan, hankalina be kwanta da zama anan ba kuma"
"meyasa hankalinki be kwanta da zamanmu anan ba din?"
"Kawai hakanan, Kawai mutafi"
tsayawa yayi again yana kallonta kamar yau yafara ganinta
"intafi inbar karatuna bayan befi shekara ba zan qarqare gabadaya?"
"wanda kayi allah yasamashi albarka, dama meye amfanin karatun don dai mutum ya iya rubuta da karantawa ne bayan hakan ko ka gama aibakada tabbacin cin abinci dashi tunda mutane nawa suke gararanba atiti da kwalinsu aiki ya gagaresu, idan mukaje inda mukaje saika samu aikin hannu mu cigaba da rufawa juna asiri"
sake sakin baki Deen yayi yana kallonta cikin tsantsar mammakin abinda take cewa can kuma yace
"maganata da Zainab fa?"
tsaki taja
"itama sai a haqura, aiba ita kadai ce mace aduniya ba ko?"
cikin tsananin mammaki yace
"a haqura?"
"eh, allah zai hadaka da wacce ta fita"
"haba kaka? jibi fa za'a tura..."
"babu inda za'a tura, kai nifa dama can bason abinnan nakeba shima munafikin uban nata baso yakeba, na me zanbari a tarwatsamin farinciki a banxa a wofi? kama cire wannan maganar aranka don yanzu kam babu ita"
jin magangganunta yayi kamar saukar guduma atsakiyar kanshi
kallonta Kawai yake totally Speechless
"kayi shiru kana kallona" tafada ganin kallon yayi yawa
"amma dai,wasa kike ko kaka?"
tsuke fuska tayi
"alamun wasan kagani a fuskata"
"to kaka idan ba wasa ba meye zamu kira wannan to?"
"kai yayi maka kama dawasa amma babu ko alamun wasa a magana ta, batunka da wannan yarinyar babu shi!"
"meyasa?" yafada ahankali yana kallon kaka da idanunshi dasuka kada sosai
"saboda nace babu shi don haka kama manta da batwwannan yarinyar don ba alhairi bace agaremu"
sosai zuciyar Deen take zafi jiyake kamar ana gasamashi ita
"amma kaka kinsan inason Zainab ko?" yafada yana kallonta da idanunshi dasukayi jajir
"zaka daina sonta ne ahankali"
ahankali yashiga girgiza kai
"kaka baxan ta6a daina sonta ba, babu ranar dazan daina sonta, kada allah ya gwadamin ranar kaka"
"Kamal ni kake fadawa haka?"
"kiyi hqr kaka, amma Zainab itace komai tawa, itace farincikina itace komai tawa bazan iya rabuwa daita ba"
hawayene suka saukomata
"itace komai taka Kamal, wato tafini matsayi agurunka?"
girgiza kai yayi yace
"ko daya kaka, kowanne da matsayinshi aguna kaka, bazata ta6a finki matsayi ba amma kamar yadda ban iya rayuwa babu ke haka itama bani iya rayuwa babu ita"
kuka sosai kaka ta fashe dashi
"ni kake fadawa bazaka iya rayuwa babu itaba Kamal? duka yaushe kasanta? kenan tafini muhinmmanci agurunka"
"kaka ba haka bane, nina rasa dalilin dayasa baki sonta bayan ita tana sonki" yafada kamar zaiyi kuka
"ni ba itace banisoba, bani daison munafikin babanta ya cutar damu ne"
"me babanta zaiyi mana? yafa amince da maganarmu kuma harnan yaxo yabaki hqr akan abubbuwan dayayi amma dukda haka bazaki sama abin albarka ba? ni yanzu meye hujjata ta janye wannan maganar? mahaifinta ya yarda har yasa aturo to menene kuma ya rage?"
"munafikine mahaifin nata, Kawai yanuna ya yarda ne amma hakan bekai zuciyarshi ba, turowan ma dayace ayi duk na manufa ne" tafada cikin kuka sosai
"manufar me kaka? meye manufarshi akai?"
"yasan bamuda kowa kamal shiyasa yace aturo, soyake ya titsiyemu"
"meye don bamuda kowa? ai ba daga sama muka fadoba, saimu fadamasu komai gameda mu, kuma koda bamuda kowa wadanda zasu tsayamana bazasu gagaremu ba, ga Mallam Nasiru da sauran mutanen arziqin unguwarnan nasan zasu tsayamana"
murmushin takaici kaka tayi
"hmmm yaro yarone, bazaka gane komai ba Kamal, bazaka gane ba"
"meye bazan ganeba kaka? kifadamin babu abinda bazan ganeba, idan akwai wani abu bayan wannan ki gayamin"
"nidai nace babu maganarka da wannan yarinyar kuma gari dolene mubarshi, kaji na gayamaka" tafada tana daure fuska don tasan duk abinda zatace mashi bazai ganeba
Tashi Deen yayi tsaye yana kallonta
"kiyi hqr kaka amma baxan iya ba, baxan iya barin Zainab ba, ina sonta"
daga haka yajuya yabar dakin
binshi da kallo tayi baki sake harya fice daga dakin
tunda suke bata ta6a sashi abu yaqiya ba sai yau
fashewa tasakeyi dawani kukan mai tsuma zuciya cikin rasa abinyi kuma....✍?
*manage please*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:45 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*093*
Tunda Deen yake beta6a shiga halin damuwa da confusion irin ranar ba
koda yafita ma rasa inda zaya yayi Kawai saiyaita yawo batareda yasan inda zaya ba
sosai damuwa tayimashi katutu arai, yarasa meya samu kaka data burkucemashi lokaci daya ta bijiro da wannan buqatar tata marar yiwuwa
nan take yamanta dawani batun shirye shiryen Introduction, damuwa ta maye gurbin doqin dayakeyi
aranar sai bayan isha'i yashigo gidan yana addu'ar allah yasa kaka tadawo hayyacinta tabar wancan maganar marar ma'ana
saidai me? yana zuwa yatarar da wani tashin hankalin inda kaka ta tsaya akan bakanta na barin garin, qarshe ma tace idan shi bazai bita ba ita zata tafi ita kadai duk yadda allah yayi daita daidai ne
sosai Deen yashiga tashin hankali ganin dagaske fa kaka take
babu roqon da baiyi mata ba da magiya harda kukanshi amma firr kaka taqiya, takoma kamar wata zautatta bataji bata gani
ganin dagaske tafiyar zatayi tabarshi yasashi shima amincewa da binta din don baxai iya rayuwa batareda itaba, itace yabudi ido yasani duk duniyar nan bayada kamarta, itace uwarshi itace ubanshi itace komai nashi
xai iya rayuwa batareda zee ba dukda rayuwar bamai dadi ba don rasata yana daidai da rasa farincikinshi amma bazai iya rayuwa batareda kaka ba, bama zai iya misalta rayuwa batareda ita ba.
haka ya amince ba don yasoba amma ya roqeta akan tabari sai gobe sai sutafi din
kamar bazata yarda ba saikuma ta amince akan gobe tafiya babu fashi ko dashi ko babu shi tafiyarta zatayi
ranar yadda Deen yaga rana haka yaga dare
ganin komai yake kamar a mafarki, jiyake dama mafarki ne da babu wanda zaikaishi murna a duniyar nan
kwata2 he never saw these coming, abin yaxomashi ne Kawai daga sama, yakasa yarda cewa zaiyi nisa da zee, nisa na har abada, yakasa ma imagine din hakan aranshi Kawai gani abin yake kamar a mafarki
Washegari ko kofar gida be leqa ba, yana cikin daki idan kuma yafito to lokacin sallah ne yayi saiyayi alwalla yakoma dakin yayi abinshi
abinci ma kasa ci yayi haka kaka ke kawo abinta tana daukewa
itama kakar kallo daya zakamata kasan she's down sosai, she looks so pale and disturbed, komai na duniya bayayi mata dadi
ganin Deen a halin dayake ciki baqaramin qara dagulamata lissafi yake ba saidai takasa yin komai akai, takasa koda consoling dinshi
haka suka qarashe wuninsu agidan cikin wani irin yanayi marar dadi wanda basu ta6ayin irinshi ba tunda suke don kowa na qunqume a dakinshi babu mai fitowa saida dalili, magana ma kanta bata hadasuba sosai kowa nafama da zuciyarshi
sai a lokacin isha'i Deen yafita daga gidan yaje masallaci don yin sallah
sai bayan sunfito yahadu da wani dan unguwar nasu mai suna Salman wanda yakasance kamar aboki ne gareshi yabashi wani envelope tareda cemashi wata zatazo sunanta Zainab don allah idan tazo yabata saqon nada muhinmmanci
tsokanarshi Salman yashigayi akan saqon menene, badai na soyayya bace shidai dan murmushi kawai yayi yayimashi sallama akan zaishiga gida don samm he's not in the mood for any joke
koda yakoma gidan awaje ya tadda kaka tabuga tagumi very worried
be tankamata ba yashige dakinshi don shima kanshi nashi damuwar ta isheshi kaya
komawa dakin yayi ya raku6e wuri guda staring at space
har lokacin yakasa yarda da abinda yake faruwa, he can't imagine wane hali zee zata shiga idan taji labarin tafiyarshi
hakan yasashi lalubo wayarshi dake kashe tun jiya ya lalubo numberta ya bugamata
jin muryarta yasa wasu emotional feelings tasomashi, she sound so innocent and cool
nan take saiyaji tausayinta ya mamayemashi zuciya
bata cancanci abinda yake shirin yimata ba, bata cancanci yayi breaking heart dinta ba bayan tasoshi da dukkanin zuciyarta, tasoshi a yadda yake batareda tayi la'akari da tarin difference dake tsakaninsu ba
nan take yaji wani irin guiltiness a zuciyarshi, ya zaiyi? ya zaiyi da rayuwarshi?
haka sukayi wayar yana iyakar bakin qoqarinshi wajen controlling muryarshi don wayar yake yana hawaye, tunanin cewa qila muryarta yakeji na qarshe yasa yakasa tsaida hawayenshi
itama taso tagane kamar ba daidai yake ba don taji a yanayin muryarshi kamar he's not ok ganin hakan yasa yaimata qaryar mura yake.
kalaman dayake mata amfani dasu da ace mai saurin ganewa ce data gane ba lafiya amma dayake bata kawo hakan aranta ba yasa batabi takansu ba sosai
wannan innocence din nata kuma ba qaramin qara tsuma zuciyarshi yayi ba har hakan yasa daga baya yakasa cigaba da wayar daita sukayi sallama akan beda charge
bayan gama wayar ya kasheta gabadaya ya zare sim card din ya karya yana hawaye sosai
sannan yatashi ya tattara important stuffs dinshi ciki harda takardunshi, sannan ya dauko wannan band din da zee tabashi ranar Valentine wanda tun ranar ya adanashi cikin wani box yafiddoshi ya daura a hannu
komawa yayi kan katifarshi ya takure waje guda staring into space idanunshi jawur.
saida dare yayi sosai kafa dik ta dauke sannan suka fito daga gidan daga su sai kayansu wanda kecikin madaidaiciyar ghana must go sai qatuwar jakar goyo dake goye abayan Deen
kulle gidan sukayi da katon kwado sannan suka nufi hanyar barin layin
tafiya suke babu mai cewa kowa komai don duk yau maganar dasuka yiwa juna qididdigagga ce
babu dadewa suka isa titi don dama basuda nisa da titi
basu tsaya ba suka cigaba da tafiya gefen titin dake kwal don motoci ma sai jefi jefi suke wucewa saboda yadda dare yayi
sunyi tafiya sosai kafin susamu wata adaidaita data tsaya gabansu don jin ko tafiya ce
kaka ce tayima mai adaidaitan magana cewa tasha zasu
saida yaqaremasu kallo sannan yafadamasu kudin dazasu bada
kaka bata musaba tace suje dukda yasa kudi dayawa itadai burinta subar unguwar kwata2
ita tafara shiga sannan aka saka ghana must go din atsakiya inda akesa kaffafu sannan Deen da saikayi zaton kurmane saboda rashin maganarshi yashiga yana rufo yar kofar adaidaitan
babu 6ata lokaci mai adaidaitan yaja sukabar wajen
tafiyarsu zuwa tashar sunyishi ne silently don babu mai cewa komai cikinsu
sosai halin da Deen keciki ke damun kaka amma batasan mezata yimashi ba, batada kalmar dazata fadamashi dazaisashi jin sanyi hakan yasa tayi shiru tana hoping cewa komai zai wuce very fast insha allah
harga allah itama tasan wannan decision din yayi tsauri sosai musanmman ma ga Deen amma ya ta iya? hakan take ganin yafi musu alhairi don aganinta gwara wannan tashin hankalin da wanda take hangomasu nan gaba
tafiyar 30mins yakaisu tashar inda sa6anin koina wajen akwai mutane sosai ga fitilu takoina yadda kasan ba tsakar dare bane
biyan mai adaidaitan sukayi suka sauka da loads dinsu
ciki suka shiga inda yawanci duk travellers ne dazasu kwana a tashar da drivers din motoci
qarasawa ciki sukayi Deen biyeda kaka dake agaba yana sauraron yadda take tambayar inane wasu daga motocin zasu tafi
shidai haryanzu ko uffan bece ba sai binta dayake everywhere she go har daga qarshe tasamo masu motar dazasu shiga wacce zata Abuja itama ta za6eta ne don taga takusan cika kuma zatayi saurin dagawa
kayansu aka sakamasu a baya sannan suka kama seat suka shiga suka zauna saboda yadda iskan daren ke kadawa sosai
akwai few mutane ma acikin motar inda wasu ma barci suke wasu kuma idanunsu biyu, cikinsu kaka ta tambayi wani time akace mata yanxu uku da rabi na dare hakan yasata sauke ajiyar zuciya takoma ta jingina jikin kujerar
dagowa tayi ta kalli Deen dake zaune silently yana kallon yatsun hannunshi saitaji yayi mugun bata tausayi
ahankali ta kama hannunshi tadan matsa tana kallonshi
be dagoba bare ya kalleta sai cigaba da kallon hannayen nasu dayayi
"kayi hqr Kamal... insha allah hakan shiyafi alhairi" tafada ahankali tana kallonshi da idanunta dasuka duri ruwa
dan murmushi yayi wanda dagani kasan na qarfin haline Kawai ya kadamata kai batareda ya kalleta ba
"yanxu gayamin meke damunka? kana buqatar wani abu?" tafada tana kallonshi cikin kulawa
"inajin sanyi" yafada ahankali
kallonshi tayi cikin tausayawa sai tajawoshi jikinta yadora kanshi a cinyarta tashiga shafa mashi kai
"sannu, ai gari yakusan wayewa harda sanyin dare" tafada tana gyaramashi hular sanyin kanshi yadda zai rufemashi kunnuwa sosai don dama shigar sanyi yayi saboda yanayinshi
ahankali Deen ya lumshe idanunshi yana sauraron bugun zuciyarshi dake bugawa abnormally
ahaka har asuba tayi
duk fitowa sukayi sukai sallah sannan suka koma cikin motar da gab take da cika don saura mutane biyu
cikin qanqanin lokaci ta ida cika aka shishiga motar akayi duk abinda ya kamata sannan driver yahau ya tada motar yaja suka fice daga tashar
Tunda Deen yake beta6a long and boring tafiya ba irin wannan
tunda motar tafara tafiya ya maida kanshi ga window yana kallon waje yanajin cewa wai yau shi zaibar garinsu Katsina bawai bari na dawowa ba A'a na har abada
dukda shekaru sunja sosai amma yana iya tuna lokacin da suka shigota sama sama, lokacin yanada shekaru goma aduniya
tunawa yayi da fadi tashin dasukayi tayi da kaka kafin susamu wurin zama inda yazaman masu gida kusan na tsawon shekaru sha takwas
dukda yasan Katsina ba garinsu bane amma hakan be hanashi jin kamar yana barin bane don duk cikin garurruwan dasuka zauna babu wanda sukafi dadewa suka kuma yi rayuwa comfortably kamarta gashi yayi achieving abubbuwa dadama acikinta marassa goguwa a memory
lokacin dasuka fita kofar Welcome to Katsina wani feeling na emptiness ya ziyarci zuciyarshi
shikenan, shikenan yatafi, yatafi yabar abubbuwa masu matuqar muhinmmanci a rayuwarshi batareda sanin lokacin sake waiwayarsu ba
sai jiyayi kamar zuciyarshi tayi dropping daidai kofar yabarta abaya yayinda yanzu gangar jikin kecikin motar ana tafiya daita
ahankali ya lumshe idanunshi, imagining yafarayi me zee keyi adaidai wannan lokacin
wataqila tanacan cikin farincikin kasancewar yau zai turo magabatanshi, wataqila takirashi, wataqila sunacan