Showing 312001 words to 315000 words out of 322641 words
Chapter 105 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
yabamu kingin magungunnanshi yayimana fatan alhairi.
sosai nagodewa mutumin da bazan ta6a mantawa da alhairinshi ba, ahaka nafito dashi abayana don nalura yanada bala'in son jiki gashi dama yanzu yake samun sauqi bazanso yayi tafiya ya wahala ba
ahaka muka fito batareda munsan inda muka dosaba ga garin babu ruwan kowa da kowa, kowa harkar gabanshi yake
karnaja xancen da tsayi, iya wahala mun wahala don saida mukayi kwana uku batareda masauki ba inda darana muke yawo ina dan yimana barar abinda zamuci idan dare yayi muzo tasha mukwana.
sosai nagaji da barar danake don bara wata iriyar qasqanttaciyar sana'a ce wanda batada dadi kwata2, na gwammaci aikin wahala abiyani da yinta gashi kuma banaso na cigaba ahaka har kyakyawana yatashi ahaka shima don sosai naci buri akanshi naji inason koyaya ne yasamu rayuwa ingantacciya
ahaka nafara neman abinyi inda daga baya nasamu aiki acikin tashar wajen wata bayerabiya mai saida abinci, dafarko wanke wanke nakemata da share share tana bani abinci safe da rana kafin daga baya yazamana har girkin nake tayata inda anan nadan koyamata wasu abincicikanmu na ghana wadanda suka samu kar6uwa sosai awajen customominta hakan yasa bayan abinci tafara biyana kudi wadanda nake adanasu don burina lokacin insamu inkama mana ko daki dayane mubar kwana tasha don kwata2 banason kwana tashar damukeyi don yawanci yan iska sunfi yawa aciki haka zasu kwana suna shaye shaye da bushe bushensu da kayan hayaqi nikuma banison kyakyawana yatashi cikin irin wannan environment din
ahaka nasamu dakyar dahada kudin kama daki daya na rabin shekara muka koma can inda daganan muke zuwa aikin kullum nida kyakyawana wanda ke maqale dani duk inda nayi baya yarda da kowa saini
sosai kyakyawana keda shiga ran mutane don mutane dayawa sunsanshi suna kuma sonshi don mutane sunsha bashi kyautar abubbuwa don yana matuqar burgesu saboda kyawunshi (kunsan yare dason kyawawa)
ataqaice dai saida mukafi shekara agarin kafin na tattara muka bar garin muka koma garin minna inda anan nasa kyakyawana Makarantar primary da islamiya nikuma nakama sana'a ina kula damu
nabaro lagos ne badon komai ba saidon dama ni garin beyimin ba, banaso kyakyawana yatashi acikinta bare yatashi da al'adunsu don sai ahankali hakan yasa ina tara isassun kudadden danaga zai ishemu natattaro muka barota
sosai na jajirce akan ilimin kyakyawana, komai dazanyi duk saboda shi ne, nayi sana'o'i kala2 wadanda nikaina bansan iyakarsu ba nidai burina na inganta rayuwar kyakyawana wanda shikadai nake iya kira nawa kuma shikadai nake kallo inji dadi
ataqaice dai munyi zaman garruruwa daban2 nayi sana'o'i daban daban dik don riqe kaina da kyakyawana wanda nake mashi kallon duniyata
ina qaunar Kamal qaunar dabaxan iya misaltawa ba don da ata6amin shi gwara ni ata6ani sau dubu
Kamal yataso yaro mai matuqar sanyi da rashin hayaniya, bayada hayaniya kwata2 ga tsantsar biyayya ga nagaba, gashi allah yabashi kwalwar daukar karatu don tun yana primary yake ciwo kyaututuka na hazaqar karatu both islamiya da boko hakan yake qara qarfafamin gwiwa wajen qara zagewa don tallafawa karatunshi
shaquwar dake tsakanina da Kamal bata misaltuwa, nice komai nashi kamar yadda shine komai nawa, Kamal yakasance yarone mai tsananin tausayawa da jin qai, bayada qiwuya ko kadan don duk yawancin sana'o'i na tare dashi mukeyi yana matuqar taimakamin sosai
ahaka harya girma yagama primary yakuma yi saukarshi tafarko inda alokacin ne muka sake tattarawa muka bar garin muka koma Katsina lokacin yanada shekaru goma sha biyu
zan iya cewa duk tafiye tafiyanmu da zama garurruwan damukayi babu wanda naji dadinshi kamar na Katsina
cikin ikon allah na tsayar da sana'a datayi matuqar amsata na saida Koko da qosai inda da ita muka samu muka,cigaba da rufama kanmu asiri
anan nasamoma kyakyawana Makarantar secondary ta gomnati ya cigaba da zuwa inda anan ma yayi fice saboda hazaqarshi ahaka harya kammala yakuma fito da sakamako mai kyau
inada burin kyakyawana yayi karatu mai zurfi kodan inganta rayuwarshi gashi nalura shima yanason karatun sosai hakan yasa naji inason ya cigaba da Makarantar gaba da secondary
kasancewar babu kudin shiga Makarantar alokacin hakan,yasashi zaman gidan shekara daya inda anan maqocinmu wanda yazama kamar dan uwanmu yasama mashi wani shagon kafinta ya dinga zuwa, acikin shekara guda din nayita tari don babu laifi inasamu sosai da sana'ar nan,tawa ta Koko da qosai gashi Kamal shima yana dan samo wani abu andcan shagon nasu
ahaka muka hada mukaita tarawa har shekara tazagayo muka samu yashiga Makarantar gaba da secondary din wanda dik shine burinmu
zan iya cewa nafishi farinciki da fara zuwa Makarantar dayayi don harwani alfahari nakeji araina idan na kalleshi naga wannan yaron nawane rainonane.
Deen yarone mai,matuqar sanyi hakan yasa wasu ke amfani da sanyinshi wajen cutardashi hakan yasa yake matuqar bani tausayi kuma nake tsayamashi tsayin daka bana kyale duk wanda ya ta6amin shi, kowama yasan irin yadda nakeji dashi kuma banison komai ya ta6ashi shiyasa ake shakkar yimashi wani abin don akanshi banajin nauyi ko kunyar kowa
haka muka cigaba da rayuwa har zuwa lokacin da Zainab tashigo rayuwar Kamal..."
cigaba tayi dabada labarin yadda akayi case din incident dinsu master inda anan tafara saninsu Zainab da yadda Deen ya kwanta asibiti harwani da zumuncin dasukayi da ahalin Zainab bayan lokacin saita gangaro kan soyayyarsu dakuma yadda soyayyar tasu bata kwanta mata ba tunfarko saboda dama tunfarko tahangomasu matsala a soyayyar
nan ta gangaro kan yadda su daddy sukazo dashi da abokinshi Alhaji Abubakar(baban asaad) sukazo suka nuna rashin son dangantakar dake tsakanin Deen da zee dakuma cewa tajamashi kunne yafita harkar yarsu harzuwa lokacin dasuka dawo kuma dakansu daga baya suka bada haquri akan abinda sukayi suka kuma yarda da soyayyarsu wanda itama dole ta amince saboda yadda talura Deen nason zee din
saikuma tagangaro zuwa maganar data tadamata hankali na batun Introduction dinsu wanda dafarko bata tashi hankalinta ba sai lokacin da wannan abokin daddyn yazo gidan shikadai lokacin Deen bayanan yana Makaranta yafadamata batun Introduction din yana kuma cewa dangin Deen suke buqatar gani najini don gaskiya bazasu wani yarda da bayada kowa ba sai ita don ba'a ta6a yin hakaba tunda ita kakarshi ce dole dai ace yanada dangi bayan ita babu yadda za'ace ita kadai ce danginshi saidai idan akwai wata qullaliya don haka su bazasu lamunci rainin wayau ba don bincike zasuyi na sosai da sosai bazasu aurama diyarsu marar asaliba
tofa abinda yatashi hankalin kaka kenan alokacin komai ya dagulemata taga kamarma sunsan babu abinda tahada da Deen
hankalinta yatashi sosai don saitaga kamarma sosuke su rabata da Deen din gabadaya
hakan yasa alokacin ta tashi hankalinta ta burkuce ma Deen akan dole subar garin don saitaji garinma yaficemata akai gabadaya
hakan shine dalilin barin garin nasu har suka koma Abuja
nanma tabada labarin irin rayuwar tsukun dasuka shiga a Abujan kafin allah ya dafamasu suka hadu da Alhaji Shamsu wanda ta silarshi Deen yazama abinda yazama yanzu, ahaka harta gangaro kan wannan tafiyar dayayi dakuma yadda ranta be kwanta da tafiyar ba don jitayi ajikinta kamar zata rasashi ne ashe kaddarace ta kirashi.. kaddarar haduwa da ainahin ahalinshi...✍?
*insha allah page 100 littafin zai qare, so start saying byebye to DEEN👐🏻*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/19/21, 6:39 PM - Buhainat😝: ahaka suke firar inda jefi jefi zee da Lailah kesamusu baki Aysha da batool nema masu surutun
sallama sukaji anyimusu daga bayansu hakan ya katsesu daga firarsu duk suka dago suna amsawa
"barka" yafada cikin murmushi
suma martanin murmushin suka maida mashi suna amsawa banda zee da tunda tadago suka hada ido ta kauda kai
"please kudan bani aronta for a few minutes..please" yafada yana nuna zee
kallon juna batool da Aysha sukayi sukayi murmushi
"oh.. sure" inji batool sai takama hannun Lailah tana cewa
"kinga mukoma daga can sis"
suka wuce sukabar daga zee sai Deen awajen
qarasowa Deen yayi ya tsaya yana fuskantar zee dahar lokacin bata qara kallonshi ba
harde hannayenshi yayi a qirji yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi
jin shirun yafara yawa yasa zee dagowa sai taganshi a yadda yake yawani kafeta da ido
hade fuska tadanyi taqara kauda face
ahankali cikin muryar rad'a taji yace
"angry bird"
dagowa tayi ta kalleshi
dan budamata idanu yayi yace
"yes, my cute angry bird"
harararshi tayi Kawai tafara qoqarin ra6ashi tawuce
"you know what?" ya dakatar daita da hakan
tsayawa tayi batareda tajuyoba
"banta6a ganin hallita mai kwatankwacin kyawunki ba aduk duniyar nan"
qarasowa yayi gabanta yana kallonta
"tell me.. what did you do to me?"
dagowa tasake yi ta gallamashi harara ta kauda kai
"zan wuce" tafada ciki ciki
kaucewa yayi daga kan hanyar yana dan bowing
"as you wish ma'am"
kauda kai taqara yi cikin qoqarin 6oye murmushin dake neman su6ucemata tazo tasake ra6ashi tawuce
"please kibani digits dinki idan babu damuwa" yafada daidai tawuceshi
batareda tajuyo ba ko ta dakata daga tafiyarta tace
"akwai damuwa"
"ok please ki taimaka ki daga idan nabugo" yasake fada da d'an qarfi don tafara yimashi nisa
banza tayi dashi ta cigaba da tafiyarta
"i'll take your silent as yes" yaqara yafada yana kallonta
dan murmushi Kawai zee tayi tana cigaba da tafiyarta, Deen won't change, her silly timid guy
agefe kuma bayan su batool sunbasu wuri suka samu wani wurin suka koma suka tsaya suna fira suna cigaba da jiran fitowarsu abbu
Lailah kasa concentrating tayi a firar tasu don hankalinta gabadaya yana gasu Deen data baro, she can't help but feel jealous, wani irin kishi taji tanaji ganin wanda take mugun crushing tsaye da wata
duk yadda taso maida hankalinta akan firarsu batool kasawa tayi don banda satar kallon inda suke tsaye babu abinda takeyi
ahaka har zee tabaro Deen tadawo wajensu inda hakan yayi daidai da fitowarsu abbu da kingin daga cikin gidan suna fira suna dariya
anan hankalinsu yadawo kansu gabadaya
wata sabuwar sallamar aka sakeyi tsakanin juna kafin su rakosu har wajen motocinsu
zee zata nufi motarsu ummy Aymaan yabude mata kofar tashi motar yana cewa tashiga fuskarshi da murmushi
dan maida mashi murmushin tayi taqaraso tashige motar batareda ta yarda tajuya takalli saitin inda takeji ana kallonta ba
maida kofar Aymaan yayi yarufe yajuyo zai wuce suka kusan karo da Aysha data gama bankwana da batool data shiga bayan motarshi
saurin jabaya Aysha tayi tana cewa
"oh..sorry"
rolling idanu Aymaan yadanyi yazo zai wuceta ciki ciki yace
"clumsy gal"
binshi da kallo tayi don tajishi harya zagaya seat dinshi
kamar ance yadago sai suka hada ido don har lokacin shi take kallo
kamar dama shi take jira yadago ya kalleta saita gallamashi mugun harara tareda murgudamashi baki sannan tajuya tawuce wajensu ummie dake dagama su ummy hannu
dan murmushi yayi yana dan girgiza kai Kawai sannan yashige motar
shishigewa motocin kowa yayi suka rurrufo sannan suka tada
har lokacin ummie bata daina dagamasu hannu ba fuskarta dauke da murmushi shikau Deen yakasa dauke ido akan zee dake cikin motar Aymaan
Ahaka motocin suka jera suka bar gidan
anan kingin suka juya suka koma ciki
dayake dare yayi sosai yasa Kawai su mamy dasu kaka suka wuce masaukinsu shima Alhaji haka inda Lailah zata kwana tareda Aysha duk sukayima juna bankwana suka shishige
adaren ranar Lailah kasa barci tayi, jitayi komai ya dagulemata
ganin Deen nason wata ba qaramin jagulemata lissafi yayiba hakan yasa ranar banda juye2 babu abinda takeyi don barcin yaqi zuwa
a bangaren Aymaan ma haka, zuciyarshi takasa sukuni, yakasa hqr da tunanin zee dukda yanajin qamshi qamshin rabuwa daita, ganin barcin ya gagara yasashi miqewa daga baya yayo alwalla yafara nafilfilu inda daga qarshe yaita addu'ar za6in alhairi yana addu'ar allah ya sassautamashi soyayyar zee a zuciyarshi yakuma bashi haqurin da juriyar rabuwa daita idan batashi bace....✍?
*manage🙏🏻*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
*🙍🏻?
8/19/21, 6:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*099*
*SEMI-FINAL*
*TWO DAYS LATER*
Acikin kwanaki biyunnan sosai su kaka dasu ummie suka zama kamar family
zama suke yadda kasan sun dade dasanin juna don sosai zumunci yaqullu atsakaninsu wanda ga dukkan alamu zaiyi qarfi sosai don juma'a mai kyau tundaga laraba ake ganeta
kaka tazama kamar wata kakarsu ta gaskiya don yanzu ba iya Deen ba hatta mussadiq da Aysha sunyi wani irin shaquwa da kaka, musanmman ma Aysha don tazama kamar wata kaka's pet kullum tana sashenta fira inda tadage wai tana koyon hausa awajen kaka
mussadiq ma babu laifi yana yawan zuwa sashen kaka saidai be faye surutu ba Kawai dai zaije ne yayi zaune yana kallon firarsu da Aysha sannan yasha furar kaka wanda tunda tabashi yafara sha sau daya yaji duk duniya babu abinda yata6a yimashi dadi irin furar hakan yasa kullum yake lalla6owa yazo part din ya zauna baya fita saiyasha furar, itama kaka lura datayi da hakan yasa kodayaushe take tanadarmashi furar don ta lura masoyinta ne sosai
abu nabiyu dake kaishi part din kaka kuma Lailah ce, yarinyar da tunda yafara dora idanunshi akanta a airport yakejinshi ba daidai ba
haka Kawai yake samun kanshi dason tsareta yaita kallo batareda shima kanshi yasan amfanin kallon ba agareshi, Kawai dai burinshi kullum ya sameta ya kafamata wadannan idanun nashi yana kallo
saidai ya lura yarinyar kamar bata magana don dafarko yayi tunanin she's the silent type sai daga baya daya tattara hankalinshi akanta yana studying dinta yagano damuwace ta maidata hakan don akodayaushe haka zaka ganta so moody bata magana saita kama, mostly yafi ganinta tana danne dannen wayarta with unknown expression a fuskarta
yau ma kamar kullum part din kaka yashiga
sanye yake da kayan gida don bedade da fitowa wanka ba bayan sundawo daga Yawon zagayen companies dinsu dayayi da Deen
he's too tired shiyasa suna dawowa yashige toilet yayi freshen up sannan yafito ya shirya cikin qanannun kaya yafita yabar Deen dake jibge a kujera tunda suka dawo waya kare a kunnenshi yana magana qasa qasa sai zabga murmushi yake kamar wanda akewa wani babban albishir
direct part din kaka yanufa don alokacin saiyaji babu abinda yakeso kamar furar kaka
da sallama yashiga part din inda as usual ya iskesu a qayattacen falon nata daita da Aysha data daddage tana koyon hausa sai mamy daga gefe tana gyara wasu kaya don gobe zasu koma 9ja
atare duk suka dago suna amsa sallamarshi ya qaraso cikin falon
"sannu.. dai zuwa" Aysha tafada cikin yanayin hausarta data fara koya tana kallon mussadiq fuska washe
harara ya gallamata yana zama kusada kaka cikin larabci yace
"idan na wanka maki mari ko?"
6ata fuska Aysha tayi tana kallon kaka
dariya Kawai kaka tayi tana cewa
"kyaleshi kishi yake don kinfara iyawa shi be iyaba"
dukda Aysha batasan me tace ba amma tasan rarrashi ne hakan yasa tadan tura baki tana sake komawa gefen kaka tana dan murmushi
shima mussadiq murmushin yadanyi sannan yashiga gaidasu kaka da mamy suna amsawa cikin fara'a, kaka sai tsokanarshi takeyi shikau saidai ya sunkuyar dakai yana murmushi don besan me take cewa ba
ba jimawa kaka ta tashi ta tafi wurin fridge din dakin tabude taciromashi furarshi data dama donshi tazo ta ajiye mashi nan take fuskarshi ta washe babu ko kunya yaqara jawo furar yabude yafara aikata don shi kanshi har mammakin yadda yakeson furar nan yake, gani yake da za'a bar bashi komai naci acigaba da bashi fura as abinci tsaff zai iya rayuwa yana shanta ita kadai
haka yaita shan furarshi yana sauraron su kaka dasuka dasa darasinsu inda mamy ce yar fassara don idan Aysha tayi tambaya da turanci mamy ke fassarawa kaka itakuma saita bata amsa
yana cikin sha yafara yawo da idanunshi a falon
something is missing, akwai abinda babu a falon
_Lailah_
dan dakatar da shan furar yayi yana tunani
gobe su Lailah zasu bar Dubai sukoma Nigeria and har lokacin magana bata ta6a hadasu ba saiko gaisuwa sama sama irin hyy hello.
ya lura idan yazo waje taganshi saita fara quramashi idanu kamar Maison tantance wani abu, daga bisani kuma saita janye idanunta akanshi baxata qara yarda ta kalleshi ba
shima most time yanason yimata magana amma saiya fasa saboda yanayin damuwar dayake hangowa qarara afuskarta hakan yasa saiya zubamata idanu instead yaita kallo kamar t.v
saida yasha fin rabi sannan yarufe kingin furar yatashi ya maida a fridge din
dagowa kaka tayi ta kalleshi bayan yadawo yazauna tace
"harka qoshi?"
yanayin yadda tayimashi nuni yasashi gane metace hakan yasashi yin dan murmushi yana kada kai
"na'am shukran laki, jazakillah" yafada ahankali
murmushi itama kaka tayi sannan tajuya kan Aysha daketa maimaita wata kalmar hausa cikin son riqewa
yadan qara zaman yan mintuna sannan yatashi yayi musu sallama yafita, he was wondering ina tashiga don a irin wannan lokacin batada wurin zama sai part din kaka
main house din yashiga inda ya tarar babu kowa dama kuma ummie batanan hakan yasashi fita waje
haka Kawai zuciyarshi tabashi yaje garden din gidan wanda hakan yasashi nufar wajen hannayenshi zube a aljihu yana takawa ahankali cikin tafiyarshi
tundaga nesa ya hangota zaune kan kujera ta kafe waje guda da ido glass cup mai daukeda fresh milk ahannunta
tsayawa yayi yana kallonta kamar mai karantar wani abu tattare daita sannan yafara takowa ya nufota
saboda zurfin datayi a tunaninta yasa batasan sadda yazo wajen ba sai jitayi an zare glass cup din hannunta
adan firgice ta juyo sai taganshi zaune a kujerar dake facing dinta yakai kofin abaki yana sipping ahankali
quramashi idanu tayi kamar mai son tantance wani abu kamar yadda tasaba kullum insun hadu can saikuma ta janye idanunta ta maidasu qasa
ajiye cup din yayi yana gyara zamanshi yace
"yes bashi bane.. ba wanda kike tunani bane, mussadiq ne" yafada da turanci
dagowa tayi ta kalleshi
"muna kama sosai ko? kamar da saikin dauki mintuna kina kallona kafin ki iya tantance waye agabanki, aganina da dagaske abinda kike tunani hakane da bazaki dauki lokaci kafin ki iya tantancemu ba don a kallo daya zuciyarki zata baki ko waye agabanki"
kallon rashin fahimta take mashi don duk takasa gane kan maganarshi
"you're confused gal... so confused, you're confusing your brain and mind, yakamata kiyi realizing gaskiya izuwa yanzu"
"gaskiya? as in?" inji Lailah tana kallonshi still confused
komawa yayi ya jingina da kujerar yana kallonta qasa qasa yace
"as in abinda kike tunani bashi bane, abinda kwalwarki ke tunani yasha banban da abinda zuciyarki ke tunani"
yanayin yadda tayi da fuska yasashi sanin yasake kullemata kai hakan yasashi yin guntun murmushi yace
"you think you love him? No, kisake bincikar zuciyarki"
wannan karon kallonshi take sosai
"what did you mean?"
"I mean you two don't really deserve each other, there's someone who deserve you most, zuciyarki tagane hakan amma haryanzu kwalwarki takasa gane hakan"
shiru tayi tana kallonshi nawani lokaci, wai akan me yake magana ne? badai akan Deen ba, idan ma akanshi ne tayaya yasani? shi kanshi Deen din bata tunanin yasan tana sonshi bare ya gayamashi
"look, wani lokacin zuciyarmu tafi kwalwarmu saurin gano abu, so goes yours don haryanzu zuciyarki bata iya gane mere presence din wanda kwalwarki take ikirarin kinaso, meyasa akallo daya zuciyarki bazata baki cewa eh shidin ko bashi bane? meyasa saikin dauki lokaci kafin ki iya tantance hakan... because your heart doesnt really beats for him, you're decieving yourself ne