Showing 153001 words to 156000 words out of 322641 words

Chapter 52 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6151

Shigowa


Idanunta ne suka fada cikin oily bright eyes dinshi dake shining as ever.... ✍️





Juma'at mubaraq in advance � 🌜





Ummin fasihu πŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:38 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEEN πŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*






*050*







*THE INTRODUCTION*









Kasa ko kyafta idanu tayi akanshi kamar yadda shima Hakan yake a wajenshi.


Basusan sunyi missing juna ba har haka Saida sukayi arba da juna


11days, kwana shadaya rabonsu dasa juna a ido abinda be ta6a faruwa ba Tun bayan fara soyayyarsu.


Hakan yasa yanzu dasukayi arba da juna suka kasa Janye idanunsu akan juna


Ahankali ya tako still idanunshi akanta har ya iso bakin gadon shima daga bayan daddy.

Janye idanunshi yayi daga kanta sannan ya duqa ya gaida mummy


Cikin fara'a mummy ta amsa mashi tana sakejin qaunarshi har cikin zuciyarta

Miqewa yakeyi yana Tambayar mummy ya me jiki tana amsawa da da sauqi sannan suka gaisa da Dr yana tsokanarshi wai badai patient dinshi bane ya murmuje haka

Shidai murmushi kawai yayi yana sunkuyar dakai yana dan satan kallon zee da itama ta sunkuyar dakai ta wutsiyar ido.


Da daddaya suka fara barin ward din har yarage daga Deen sai zee


Dagowa yayi ya kalleta sai yaga haryanzu kanta a sunkuye yake sai yadanyi murmushi sannan yaja kujerar da mummy ta tashi akai ya zauna.


Tana jin yadda idanunshi ke piercing din fuskarta amma taqi Dagowa saima jujjuya Ring dinshi dake yatsarta datake yi


"ya jiki?" taji yafada ahankali

Ahankali ta Kada mashi kai batareda ta dago ba


"I missed you" taji yaqara fada


Ahankali ta dago itama ta kalleshi Saidai batace komai ba sai cigaba da kallonshi datayi


"kin rame" yasake fada ahankali

Hakan dayace yasa itama ta hango nashi ramar

"you too" tafada ahankali itama


Murmushi yayi
"dole na rame, kwana na 11 banga abincin ruhi na ba"


Dan murmushi tayi tana sadda kai tanajin duk wata damuwarta na fecewa daya bayan daya.


"am sorry for what kaka said, naso na dakatar daita amma taqi yin shiru" yafada yana kwa6e face

Dagowa tayi ta kalleshi
"da Gaskiyarta ai, wataqila wani abin daddy yayi muku"


Girgiza kai Deen yayi
"babu abinda yayimana kawai rudun tsufar kaka ne, daddy is very nice"


Dan murmushi zee tayi
"ka fadamin Gaskiya"


"na ta6a miki qarya?"


Shiru tayi don ta tunano ko ya ta6a din saiya katse mata tunanin da

"hankalina ya tashi sosai lokacin da kuka gama wayar da kaka, gashi inason miki magana amma kaka ta cire layin ta karya dole nafita wani shagon kati na ari wata wayar nakira but ba'a dagawa tun lokacin hankalina ya ida tashi don zuciyata na fadamin ba lfy. Jiya ko barci banyi ba"


Murmushi kawai tayi tana kallonshi not saying anything

"am glad you're ok now and am glad baxamu qara yin nisa da juna ba, daddy ya amince" yafada cikin doqi


Fadada murmushin ta itama zee tayi sai kuma ta dan 6ata fuska

"what?" inji Deen yana dan daga mata gira

"Kaka fa" tafada tana marairaice fuska


Dariya yayi
"Kaka too is ok with everything"


"dagaske?

"yes, sunyi magana da daddy dama duk rudun tsufa ne" yafada yana Dariya

"to don Allah me daddy yayi muku, naji tafadi Hakan jiya"

"babu komai fa nace miki"


"please tell me" tafada a marairaice


"please stop asking" Shima yafada yana karya wuya


"is it really bad?"

Daga kafadunshi yayi yace
"not that bad"


Zata sake magana ya katse ta ta hanyar cewa
"shhh, Kiyi shiru ba'ason marar lfy yana surutu"


Harararshi tayi zata sake magana yace
"shhh, Kiyi shiru, ni zanyi maganar kekuma sauraro ne naki, ok?" yafada yana dan Hade gira


Murmushi tayi ta kauda kai

Jin shiru yasa tasake juyowa ta kalleshi sai taga shima ita yake kallo

Daga gira daya tayi alamun ya?

Sai yayi mata murmushi
"I love you" yafada in whisper

Sauke idanunta tayi tana murmushi

"I love your face, your smile, your everything, don Allah ki warke dawuri mukoma school yadda zamu dinga hadewa kullum, kewarki nason kasheni"


Murmushi tasakeyi
"ni zan warkar da kaina?"


Girgiza kai yayi sai kuma ya bude taffukan hannunshi cikin sigar addu'a yace
"ya rabb kaba wannan baiwar taka lfy yadda zamu dinga zuwa school muna ganin juna kullum

Allah kasa ta maida qibarta karta tsaya haka kamar sugar cane"

Wara idanu zee dake sauraronshi Tundazu tayi tace
"kutt.. Nice sugar cane"


Jada baya yayi da kujerar yana Dariya

"sorry, to kamar fish bone"

Qara Wara idanun tayi shikuma ya cigaba da yimata Dariya.


Sun dade ahakan suna fira suna Dariya har mummy tashigo ta iskesu


Sosai mummy tayi mammakin ganin yadda ta gyagije kamar ba ita ba, fuskarta beaming in smile, sai a lokacin itama taqara jinjina soyayyarsu takuma qara tabbatar wa Deen shine farincikinta



Deen be qara dadewa ba yayi musu sallama yatafi don tareda yimusu alqawarin zasu dawo da kaka anjima


Ji Zainab tayi kamar tace mashi kar yatafi shima jiyake kamar kar ya tafi haka dai sukayi sallama rai babu dadi yatafi.


Sai a lokacin ta tashi tayi alwalla ta rama sallolinta na asuba dabatayi ba da zuhr sannan ta hada da asr da ake cikin yi lokacin.


Tana gamawa mummy ta gabatar mata abinci kuma taci sosai tasha magunggunanta


Kallo daya zaka mata ka fuskanci tana cikin farinciki dukda haryanzu zuciyarta na dar dar akan wannan al'amarin musanmman ma a 6angaren kaka da bata tabbatar da nata amincewar ba.


Sai wajajen biyar daddy yasake dawowa hospital din da siyyayar abubbuwan dayasan tanaso wanda mostly duk fruits ne, ya shaqo babbar leda dasu.


Sosai daddy yashiga tarairayarta fiyeda yadda yake mata ma da, tun bata ida Sakin jikinta dashi ba har ta gyagije suka koma yadda suke


Yana taredasu har magrib sannan ya tashi ya fita


Sai bayan isha'i yadawo tareda Deen da kaka dasuka Hade a waje


Tunda zee tayi ido hudu da kaka ta maida kanta qasa tanajin yadda gabanta ke faduwa don ita tunda ta fahimci kaka bata shiri da wanda ya ta6a mata Deen take taka tsantsan daita don ga dukkan alamu zatayi masifa


Saidai ga mammakinta sai taga akasin abinda tayi tunanin gani don lfy lau aka gaisa tayi mata ya jiki cikin fara'arta data saba yimata don harda guzurin kayan fruits datayo mata

Ganin Hakan yasa ta dan saki jikinta itama

Fita daddy yasake yi don yin magana da Dr don Gaskiya beson su kwana asibitin tunda taji sauqi gwara su koma gida duk yan ide iden da ba'ayi ba Dr yabiyosu har gida a ida.



Hira sosai kaka da mummy keyi kamar babu abinda ya faru, kwata2 babu wanda ya tada maganar misunderstanding din daya faru tsakaninsu saima firar duniya dasuke tayi abinsu


Sukau mutanenku yan saurare ne kawai, sun kasa kunne sai sauraron hirarsu mai cike da ban Dariya suke idan akayi abin ban Dariya sai su kalli juna suyi murmushi


Sun dan jima ahakan daddy yasake Shigowa tareda Dr

Saida aka sake gagaisawa sannan Dr yaqara dubata yaga komai normal sannan ya rubuta masu sallama bayan ya basu maggungunanta


Daga zee har Deen babu wanda yaji dadin sallamar don that means su da haduwa sai a school kuma


Sai wajajen 10 saura duk suka fito lokacin har daddy yasa an kawo wata motar dazata sauke su kaka gida.


Cikin farinciki da aminci suka rabu su kaka suka hau motar da bala zaija sukuma su daddy suka hau dayar motar inda daddy ne zai jasu sannan suka fito daga asibitin gabadaya kowa ya dauki hanyarshi.


Da kanshi daddy ya raka zee har dakinta yana lalla6ata kamar wata kwai


Saida ya zauna suka qara dan fira sannan ya tashi ya fita bayan sun yima juna Saida safe



Saida tayi wanka tayi shirin barci sannan ta haye gado ta kwanta don dama tariga taci abinci a can haka asibitin tasha maganinta.


Kwanciya tayi shiru idanunta akan p.o.p.

Takasa yarda haryanzu wai daddy ya amince da Deen.

Just like that? Saikuma ta tuna irin qaunar da daddy ke mata tabbas bazai ta6a barin ya rasata ba muddin yana da yadda zaiyi ya ceci rayuwarta

Murmushi tadanyi, da tasan da Hakan da duk ba'a kai yanzu ba, da tuntuni zatayi faking sickness din amma dukda haka alhamdullilah, what matters is ya amince din don haka bata tunanin tanada wata matsala a rayuwa.


Tunawa tayi da wayarta Hakan yasa ta miqe zaune tana waige waigen inda zata ganta

Can qasan gado ta hango ta tafiddo ta.

Danna power botton tayi sai taga takawo haske amma charge dinta yayi low


5 missed calls tagani a gaban screen din

Swiping tayi ta shiga call log sai taga baquwar number ce mai kiran

Har tafara tunanin waya kirata saita tuna Da Deen yace ya nemeta da wata wayar da ya aro, tabbas shine kenan.

Danna ma ainahin number Deen din kira tayi dukda taji yace kaka ta karya layin

Kamar kau yadda ta zata bata shiga ba hakan yasa ta kashe wayar gabadaya ta jonata a chaji takoma ta kwanta tana jin zuciyarta wasai


Bata wani jima ba barci ya sadado yayi gaba daita






Washegari garas zee ta tashi sai dan abinda ba'a rasaba.

Har daki daddy yazo dubata yakuma sata taci abinci yabata maggungunanta tasha.

Sosai yake kulawa daita kamar kwai

Yana nan zaune daita har wajajen 9am lokacin da Dr yashigo Domin duba lafiyar ta

Saida ya duddubata yaga komai normal sannan ya qara jaddadamasu akan ta cigaba da shan maganin akan lokaci insha allah zata ida warwarewa.


Tare da Drn daddy yafita don dama shi yake jira yazo ya duba mashi diyarshi kafin ya fita aiki.


Sai a sannan zee tasamu damar fitowa daga dakin itama tafara biyawa dakin Mummy suka gaisa sannan tadawo falon qasa ta zauna.


Tana ahakan wajajen 12pm kira yashigo wayarta

Dubawa tayi taga baquwar number ce

Kamar karta daga saikuma wani tunani yazo mata saita daga aikuwa hasashenta ne yazamo Gaskiya don Deen din ne


"patient"


Murmushi tayi
"waye Hakan?"

"kinfini sani, yaya jikin?"

"alhamdullilah, naji sauqi sosai"


Sautin murmushin shi taji
"masha allah, allah yaqaro sauqi"


"Amin ya allah" ta amsa tana yin filo da hannun kujerar datake akai


"yasu mummy?"

"mummy lfy lau, ina my kaka?"


"Your kaka tana nan lfy lau tana gaidaki da jiki"


Murmushi tayi
"ina amsawa sosai, nima ina gaida ta"


"to zataji... Baki tambayeni ba"


Dan daga gira tayi
"Me?"


"this strange number"

Murmushi tayi
"yanzun ma aro kayi?"


"nop, siyan wani layin nayi so you better save it"

Yadda yaqarashe maganar bossily yasata Dariya

"yes boss!" tafada tana Dariya


Shima dariyar yayi

"yaushe zakiyi resuming school?"

Daga kafadu tayi
"Don't know, qila saina ji sauqi"


"O'O! Ba kinji ba?"


"O'O! Ban ida warwarewa ba" tafada cikin kwaikwayon Maganarshi



Ko bata ganshi ba tasan 6ata fuska yayi
"please get well soon, am missing you badly"


Murmushi tayi kawai amma gani take duk missing dinta dayake bekai wanda takeyi ba

"insha allah" tafada tana murmushi

"kinga exams nata matsowa, we have alot to cover"


"yeah, insha allah ai Dr ma yace naji sauqi sosai saura strenght dina ya dawo"


Jitayi yace
"Ya rabb kadawo mata da strenght dinta ta tashi tajita da qarfi kamar super man"


Dariya tayi tace
"da kaine punching bag dina na farko"

Wara idanu yayi daga can 6angaren

"Ca6 baxaki iya ba"

"why not?"


"saboda fuskata ba don punching akayita ba, bazaki iya dora ko yatsa daya akanta ba da sunan duka bare naushi"



"Me zai hana?"


"kyawun ta mana"


Dan wara idanu tayi
"fahari ko?"


"No, Gaskiya ce ai"

"tayaya to kasan tanada kyau"


"nasani mana, ba ina duba mirror ba"


Dariya ya bata amma batayi ba

"haba? Namiji dama na duba mirror?"

"baya dubawa dama?"

"haka nazata"

"to nidai ina dubawa"


"to kuma yaya akai ka gane kyawun?"


"ba nagani a mirror ba?"


Dan gasping tayi cikin mammaki 😱
"dama mutum idan ya kalli kanshi a mirror yana gane kyawunshi?"


Cikin confusion yace "ke idan kika kalli mirror bakya ganin kyawunki?"


Dariya tayi marar sauti sannan tace
"A'a ni ban ta6a gani ba"


"to me kike gani?" ya tambaya confused


"kawai dai nasan nice, thats all"

"bakya kallon large white eyes dinki, da pointed hancinki da qaramin red lips dinki da cute kumatunki da long lashes dinki, duk bakya tsayawa kallo?"


Dariya taqara yi tana rufe bakinta don karya ji

"ni duk bana gani kawai nadaisan nice kawai and the moment na ajiye mirrorn saina mance yadda fuskar take"


Wara idanu yayi
"yanzu bakya gane fuskarki without mirror"


"ko kadan, kai kana ganewa ne?" tafada tana qumshe Dariya jin ya dauki abin serious


"Are you kidding me? Tayaya za'ayi na mance fuskata? Nine fa?"


"abin mammaki, kenan kana iya gane kanka? Tayaya zaka iya riqe fuskarka ba Saidai wani ya riqemaka ba tunda ba ganin kanka kake ba?"

Qara shiga confusion yayi yace
"to Saidai idan bakida lfy amma tayaya za'ayi ki kasa gane fuskarki?"


Dariyar datake riqewa Tundazu ya kuce mata tashiga yi


Ajiyar zuciya ya sauke


Cigaba da Dariyar tayi

"Gaskiya yakamata Dr yaqara duba ki, I wonder yadda ma akayi na yarda da maganar ki tunfarko bayan nasan bakida lfy"


Wara idanu tayi still tana Dariya

"nice banida lafiyar?"

"ga zahiri?" Shima yafada yana Dariya


Haka sukaita firarsu Saida yan kudin da Deen yasa suka qone sannan.


Bata sake bugamashi ba ta tashi ta haye sama don tasan idan ta bugamashi kuma sai allah yayi don ita ko awa zasuyi kudin bazasu qare ba gashi idan suna waya basu iya taqaita ta ba don dasun fara mancewa da komai suke sai kansu kadai






*fast forward*




A cikin kwanaki uku zee ta warke sumul kamar bata ta6a ciwo ba


Sosai take samun kulawa a wajen iyayen nata musanmman daddy dayake riritata fiyeda yadda yakeyi ada.

A bangarenta da Deen kau sai abinda yayi gaba don kodayaushe suna maqale awaya suna firarnan tasu mai antaya kowannensu acikin nishadi.

Ata koina komai tafiya yake masu so smoothly sun mance da wata aba wai damuwa.




A ranar da yakama kwana biyar da kwanciyar zee hospital wanda yayi daidai da ranar asabar da daddare lokacin kwanciyar su mummy.


Suna Kwance suna firarsu kamar yadda suka saba

Daddy ne ya qara fuskantar mummy sannan yace
"ya kika ga daughter na yanzu? Very cheerful and lively"


Murmushi mummy tayi
"hmm kaidai bari, ai yaran zamanin kenan, baka yimasu dole idan kuma kayi kai zaka fara ganin sakamakkon shiyasa muddin kasan abinda sukeso mai kyau ne kawai ka miqa wuya"


"ai naso nayi ganganci maimuna, dana rasata ai shikenan na shiga uku"

Dariya mummy tayi ganin yanayin daya fadi ya shiga ukun.


"Ato ai kaine wani sa'in baka jin shawara, wlh ni tunda ta ambaci sunan yaron nan naji hadin yayi min don Gaskiya yaron yanada wata baiwa da ba kowanne keda ita ba, ga nutsuwa uwa uba ladabi. Wlh tun a asibiti halayyar yaron nan ke burgeni Gaskiya kaka tayi qoqari"


Murmushi daddy yayi
"ai nima naso tafka babban kuskure, don nagartar yaron na tabbatar da nagartar shi kawai selfishness ne dakuma burin dana dauka na dorawa auren daughter na ne, I thought hamshaqin mai kudi zata kawo shiyasa data kawo wannan naji nakasa yarda"


"ai kudi ba shine farinciki ba, yara nawa suke auren masu kudin amma kaga babu kwanciyar hankali? Kaga sai bushewa suke a tsaye bayan akwai komai na more rayuwa a gidan, kawai fatan miji nagari shiya dace ga kowacce diya mace ba bawai kudi ba don wasu ga kudin amma rashin kwanciyar hankali ya hana sucisu cikin jindadi" inji mummy


"ai duk na gane Hakan yanzu, na zauna nayi karatun ta nutsu nagano money is not everything kuma nayi bincike akan hallayarshi nasamu nagarttatun result, shiyasa na yanke shawarar gayamashi ya turo ranar laraba idan allah ya kaimu"


A mammakince mummy ta juyo tana kallonshi

"turowa kuma?"

"yes, yaturo ayi Introduction"

"but why the rush?" inji mummy still cikin mammaki


"hmm ke baki san halin da ake aciki bane
Allah yayiwa diyarki farinjinin masoya, mutanen dake tunkarata da son abasu ita ko wa 'ya'yansu ko wa kansu basuda iyaka, kullum cikin atracking dina suke akan maganarta amma saboda nayi alqawarin bazan yimata dole bane yasa duk bana maida hankali akai Saidai nace suje su tunkareta idan ta amince dasu to ni banida matsala

Dukda Hakan ban tsiraba kullum cikin zarya ake wajena shiyasa na yanke shawarar kawai sawa zanyi yaron datake so ya turo a daidaita magana kinga duk wanda yaji an badata bazai qara damuna ba"


Shiru mummy tayi sai kuma ta Kada kai
"kuma fa hakane, amma sai inga yayi wuri dayawa abari takusan gama school mana"

"ai ba auren za'a daura ba bakuma sa biki za'ayi ba kawai introduction ne, ma'ana suzo neman auren ta ya kasance an tsayar da magana, kinga idan shi yayi graduating yafara service sai asa bikin lokacin dazai gama service sai a daura auren dama kuma nariga na fidda post dazan bashi a daya daga cikin companies dina kinga sai suyi settle down ga mata ga aiki, ko yaya kika gani?"


Tuni mummy tahau fara'a batasan sanda ma tayi mai half hug ba

"perfect! Hakan yayi sosai wlh, kai amma naji dadi"


Murmushi daddy yayi ganin yadda mummyn ke murna sai yace
"kinga basai acemashi ya turo wannan larabar ba, basai sun takura kansu ba da kawo kudi yanzu duk mun zama daya kawai fatanmu allah yasama abin albarka"


"Amin ya allah Alhaji, Gaskiya bansan yadda zan iya musalta maka farincikin danake ciki ba, am supper happy, at last nafara jiyo qamshin auren diyata"


Dariya daddy yayi ganin yadda ta rikice don murna sai yace
"wayaga uwar amarya"


Jujjuya idanu tayi
"hmm za'ayi abu" tafada cikin cin buri


Dariya daddy yasake yi yace
"to yanzu sai agayama su mutanen Ruma ko sai asamu kosu yusuf suzo"


"har saisun zo?"


"yo ba diyarsu bace? Ni nan kinsan banida yayye ko qanne maza sai only qanwata JAMILA(ummu batool) kuma ba anan qasar suke ba bare nace mijinta ya wakilceta

Kinga idan daya daga cikin kawunnan nata na Ruman suka zo sai nasamu aboki ko daya nima ayi zaman tunda kawai introduction ne basai anyi wani gayya ba"


"hakane wlh, Gaskiya tsarin yayi, allah ya taimaka yasa ayi taro lfy a watse lfy"


"Amin amin Hajiya ta, insha allah bikinnan zai zama one in town, zamu jijjiga Katsina"

"Allah Alhaji na" tafada cikin tsananin jindadi

"Allah hajiyata"

Da wannan firar suka kwanta a ranar kowa zuciyarshi fess.




Washegari ummu batool ce ta fashe kwan wa zee don ita batasan anayi ba Saida ummu batool din ta kirata tana kodata tana cewa tun saura wata biki zasuzo nigeria su tare don sune amara qirjin bikin

Tace ba don


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login