Showing 318001 words to 321000 words out of 322641 words
Chapter 107 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
yadda yasamata suna yanzu dukda kullum suna maqale awaya
a bangaren zee ma sosai take missing baby boo din nata, rabonta dashi tun daren dazasu tafi saudiya gashi ba video call sukeyi ba bare su dinga ganin juna hakan yasa tayi wani irin missing dinshi, kullum idan suna waya saita dinga damunshi kan yaushe xai dawo saidai yace mata very soon insha allah
relationship dinsu yanzu yayi improving sosai don har yana neman fin na da don sosai suke zuba soyayya mai tsayawa a qwalwa
shaquwarsu tada tadawo tama ninka nada don wani lokacin ma idan suna jin yan shiriritarsu haka zasu dinga musayar kalaman soyayya ta sigar waqa atsakaninsu ta waya
yanzu zee ita kanta tasan bazata gwadama Deen komai ba akan waqa don har mammaki yake bata idan yazaro mata wani baitin
daya daga cikin dream dinta na neman tabbata don aduniya tanason waqa tana kuma dreaming tasamu wanda ra'ayinsu zaizo daya suyita tisa kansu agaba suna zubama juna baitika
Yau tunda ta tashi takejin kanta cikin wani irin happy mood don Kawai tsintar kanta tayi dawani irin nishadi ayau din
kowa ma na gidan ya shaida haka don qarara hakan ya bayyana a fuskarta da ayyukanta don tariga kowa nagidan tashi saidai suka tashi sukaga tama kusan gama aikace aikacen gidan
haka tawuni cikin nishadi don abu kadan saita fashe da dariya dana dariya da wanda bana dariya ba har batool na tsokanarta kodai she needs psychiatric doctor ne? itadai Kawai saidai tayi dariya tace yau Kawai tana cikin nishadi ne without knowing why
da daddare bayan isha'i suna zaune cikin dakinsu suna kallon wani series film cikin laptop din batool wayar zee tayi ringing
ringing dinne yan dawo dasu daga duniyar kallon dasuka bada dukkan hankalinsu akai
"mtcheew don allah shut that phone up tana distracting dina" inji batool idanunta akan laptop din batason ko janyesu daga kan screen din
harararta zee tayi tasa hannu ta danna ma film din pause wanda hakan yasa batool tashi zaune azabure
"haba meye haka?" tafada a little upset
"saina gama wayar zamu cigaba" tafada tana jawo wayar dake gab da tsinkewa
danna play batool tazo zatayi zee ta suri laptop din ta miqe tsaye tana mata gwalo
itama miqewar tsaye tayi tafara kiciniyar kwace laptop din da zee ta6oye abayanta zee na zillewa tana dariya
ahaka har kiran ya tsinke bata saniba wani yaqara shigowa
dira zee tayi daga kan gadon still laptop din abayanta tana son rugama batool dake qoqarin kamota
dago wayar hannunta tayi da niyyar kasheta ma gabadaya don taji dadin rigimar dasukeyi da batool don dama sun saba saidai number data gani na yawo akan screen din yasata yin still tana waro idanu
batool dabata lura da yanayinta ba tasamu ta kwace laptop din tana
dariya tana cewa
"got yah!"
"OMG!" inji zee tana kallon wayar idanu abude
"meye?" inji batool tana matsowa
bata amsa mata ba sai daga wayar datayi takara akunne ahankali
sallamarshi dataji cikin cool voice dinshi ya ida tabbatar da zarginta, Deen is back!
sauke wayar tayi saurin yi ta katse kiran sannan ta wawuro batool dake gabanta tawani irin rungumeta tana ihun murna
"he's back! he's back! OMG!"
saurin qwace kanta batool tayi tana cewa
"wai meye haka? who is back?"
cikin tsananin murna tace
"my boo mana! kalla da number nan yakirani, wayyo! what a surprise!" tafada tana juyi
tsaki Kawai batool taja takoma kan gadon tana bude laptop din
saita kanta zee tayi kafin taqara daga kiran daya sake shigowa
"hello?"
taji anfada daga dayan bangaren
"hello... is this for real?" tafada ahankali cikin yanayin mammaki
sautin murmushinshi tajiyo sannan yace
"kifito and see for yourself"
"infito ina?" tafada tana dan wara idanu
yar dariya yayi sannan yace
"waje, ganinan a parking space kizo kiyimin iso"
"are.. you serious?"
yar dariya Kawai yayi yace
"saikin zo" daga haka ya,katse kiran
dungule hannayenta tayi tana ihun murna sannan tayi wani juyi tafada kan batool dake kallon ta
"wai meye haka?" inji batool tana tureta daga jikinta
"wai yana waje, what a huge surprise!" tafada cikin tsananin murna
harararta batool tayi tace
"ji gulma, kamar irin batasan dazuwanshi ba dinnan. ashe ba banza ba duk wunin yau baki yaqi rufuwa ashe kinsan abinda kika taka"
"ji banza, wlh bansan da zuwanshi ba"
ta6e baki batool tayi tana maida hankalinta akan laptop din gabanta tana cewa
"saikiyi"
dunguremata qeya zee tayi tana cewa
"banza joy killer Kawai" ta tashi tanufi closet dinsu tabude
cikin qanqanin lokaci tashirya cikin wata baqar abaya ta yafa gyallenta in a simple way tadan gyara fuskarta sannan ta feshe jikinta da turare
zuwa tayi taqara dungure ma batool kai tana cewa natafi sannan tajuya tawuce dasauri
kwafa batool data dago tana kallonta tayi sannan ta maida hankalinta kan abinda takeyi
fitowa tayi daga falon sannan tafara takowa ahankali ta entrance din tanufi parking space hoping badai tsokanarta yakeyi ba bezo ba
wata baquwar ash colour motar data gani pake a parking space din yasata jin wani irin sanyi na ratsa zuciyarta
ahankali take takawa tana nufar wajen inda ko rabin kaiwa batayi ba aka bude murfin kofar daga bangaren driver yafito
tsayawa tayi daga tafiyar datake tana kallonshi yana zagayowa dayan side din motar
bata ta6a sanin har haka tayi missing dinshi ba sai yanzu, jitake kamar sun shekara basu hadu ba gashi yawani chanza yaqara yin fresh dashi
shima bangaren Deen hakan take don shima sosai yaji yayi kewarta kuma ta chanza mashi sosai cikin dan lokacin dasukayi basuga juna ba
ahankali ya sakarmata wannan cool murmushin nashi itama saita tsinci kanta da mayar mashi da martani
ahankali yashiga takowa zuwa ina take tsaye hakan yasa ta cigaba da kallonshi abubbuwa dayawa nakai kawo azuciyarta
komai nashi na daban ne hatta tafiyarshi, komai nashi cikin nutsuwa yakeyi, kai she love this guy!
saida yaqaraso gabanta ya tsaya yana dan bada tazara atsakaninsu
kallonta yakeyi da oily eyes dinshi fuskarshi dauke da murmushi, kasa cigaba da jurar kallon tayi hakan yasata sauke nata idanun qasa tana d'an murmushi
"wow! you're welcome, dama yau zaka dawo baka fadamin ba? kai amma am very happy and surprise altogether, I missed you so much" inji Deen yana kallonta
dagowa tayi ta kalleshi tana dan daga gira
shima daga gira daya yayi yace
"koba haka kikeda niyyar cewa ba?"
harararshi tayi
"to ba haka nayi niyyar cewa ba, besides fushi ma nake dakai, ashe yau zaku dawo amma shine baka gayamin ba kuma har waya munyi dasafe?"
yar dariya yayi yace
"it's a surprise, yanzu da kika ganin kamar daga sama ba kinfi jindadi ba?"
kauda kai tayi tace
"ni banwani jindadi ba"
"ai bake zaki fadi jindadinki ko rashin jindadinki ba, fuskarki zata bayyana kuma tariga ta tonamiki asiri"
harararshi tasakeyi sannan tajuya
"muje"
"to ranki shi dade"
murmushi Kawai tayi suka jera atare suka nufi cikin gida
zee tafara shiga falon sannan tayima Deen iso shima yashigo ciki bayan ya cire takalminshi saura baqaqen socks akafarshi bakinshi dauke da sallama
falon babu kowa sai qamshin dake tashi afalon
nunamashi wurin zama tayi ya qaraso ya zauna ahankali ita kuma tawuce kitchen
ba dadewa tadawo da dan tray mai dauke da ruwa da drinks tazo ta ajiye akan stool din dake kusada kujerarshi
dagowa tayi ta kalleshi saitaga shima ita yake kallo ya sakarmata murmushi
kauda kai tayi itama tana murmushin tace
"bari nakira ummy"
"nabari" yafada yana kallonta
juyawa tayi tawuce sama tanajin idanunshi kanta
saida tahaye sama sannan ya daina kallon stairs din sannan yakoma ya jingina da kujera yana murmushi kai da ganinshi kasan yana cikin farinciki sosai
ba'a jima ba yaji motsin saukowarsu hakan yasashi dagowa yaga ummy agaba zee biyeda ita
cikin murmushin kunya ya miqe tsaye ya dan sinne kai har suka qaraso falon
"A'a? maraba da mutanen saudiya, saukar yaushe?" tafada tana qarasawa ta xauna
russunawa Deen yayi yana gaisheta cikin sinnar dakai
amsawa tayi cikin kulawa tana cewa ya zauna
maimakon yakoma ya zauna kan kujerar daya taso saiya zauna nan qasan carpet din
"A'a? ka koma sama mana" inji ummy
"A'a nanma yayi ummy" yafada akunyace
"to ya hanya? ya mutanen saudiyan?"
"alhamdulillah ummy duk suna gaidaku"
"muna amsawa, yasu kaka?"
"kaka na gida tana gaisheku itama"
"muna amsawa, fatan kundawo lfy"
"lfy qalau ummy"
"to madallah... daughter kawomashi abinci kinji"
dasauri yace
"A'a alhamdulillah ummy"
"to bari nahau sama, let me know idan zaitafi Zainab"
"to ummy" Zainab dake tsaye bayan kujerar ummy tundazu ta amsa
ummy ta tashi tawuce sama
ajiyar zuciya Deen yasauke bayan hayewarta sannan yadago ya kalli zee
dariya tadanyi
"kamar na allah" tafada tana dariya
dan wara idanu yayi
"to da na wanene?" yafada yana tashi yakoma kan kujera
itama dawowa tayi gaban kujerar da ummy ta tashi ta zauna
"wow! I missed this girl so much, kinsan daga saukarmu wanka Kawai nayi na chanza nayonan? I just can't wait to set my eyes on you"
murmushi zee tayi
"miss you too"
"A'a banga alama ba, naga nikadai ma ke doqi na"
"haka dai kace"
"hakane ma"
"to ya hanya? hope kun iso lfy"
"lfy lau wlh, hope munsameku lfy"
"lfy lau, so how's saudi?"
"alhamdulillah, duk lfy.. kinsan wani abu?"
girgiza kai zee tayi
"banta6a sanin haka mutum kejiba idan yana cikin family dinshi ba saida muke saudiya... wai nine tsamo tsamo cikin mutane kuma wai family dina, wlh ko amafarki banta6a hangowa kaina haka ba, jinike kamar ba gaske ba..I was just so overwhelmed.. banta6a sanin haka family keda dadi ba.. ranakuna a saudi da misra are one of my best moment ever"
Zainab kasa daina murmushi tayi tunda yafara magana, kallo daya zakayimashi kasan he mean duk abinda yake cewa, sosai farinciki ke bayyane afuskarshi, sosai taji tana tayashi murna da hakan don wannan abin abin atayashi murna ne
"congratulations, aidama family nada dadi bazaka gane hakan ba sai kana cikinsu, gaskiya ina tayaka murna, am very happy for you"
murmushi Deen yayi sannan ya kalleta
"and all these happened because of you, har duniya ta nade bazan ta6a mantawa da mutane biyu ba arayuwarta, dake da kaka. kun taka rawar gani arayuwata sosai
kaka ta ku6utar dani takuma raineni cikeda so da qauna batareda tasan koni waye ba, takuma zamemun kowa alokacin dabanida kowa kekuma kinyi silar dawomin da komai dana rasa arayuwata, kindawomin da asalina kin dawomin da kowa nawa... tayaya za'ayi namanta daku Zainab?"
sauke idanunta zee tayi tana murmushi don kallonta yake directly in the eye, maganarshi yasata jinta very emotional har tanajin kamar ta zubda mashi kwalla
ahankali tace
"you know.. komai muqaddari ne daga allah,allah yariga ya qaddara baxaka tashi cikin danginka ba yakuma qaddara xakayi rayuwa nesa dasu sannan ya qaddara cewa a irin wannan lokacin zaka dawo garesu, daga ni har kaka Kawai kamar tools ne na gudanar da abinda allah ya tsaramaka..allah yariga ya qaddara kaka ce silar raboka da danginka dakuma qasarka while nikuma ya qaddara nice silar hadaka dasu bayan shekaru masu yawa, so muma ba wayonmu bane Kawai hakan is destined don haka allah yakamata ka dinga godemawa domin ba qaramar ni'ima yayimaka ba, akwai mutane da dama irinka basu rayu dakowa nasuba kuma harsu koma ga allah,basu ta6a komawa ga nasu saidai ko a lahira saboda basuda rabon ganawa a duniyar kaiko kanada rabon sake ganawa da danginka aduniya, kanada rabon ganin mahaifiyarka wanda tun tashinka baka Santa ba, meyakai wannan? so ka cigaba da godewa allah domin ba qaramar ni'ima yayima ba"
sosai magangganun zee suka sanyaya jikin Deen, hakane yanada rabon sake ganawa dasu ne shiyasa komai yafaru a yadda yafaru, da beda rabon ganawa dasu da qila be hadu da zee ba bare har ta silarta yasan asalinshi da ahaka zai qare rayuwarshi besan yanada mahaifiya ba a duniya, babu komai a maganar zee sai tsantsar gaskiya don yanada gashi dayake beda rabon haduwa da abbanshi saigashi shi bayanan, yatafi. qila shikuma sai acan, yana kuma fatan allah ya hada fuskokinsu a aljanna
"alhamdulillah.. alhamdulillah rabbil a'alamin... alhamdulillah bi ni'imatika alayya" yafada ahankali saikuma yadago ya kalli zee da idanunshi dasuka kada sosai
"marry me please... don allah kibari na mallakeki"
wara idanu zee tayi saidai kafin tayi magana haryakai kan knees dinshi
"please marry me"
qara wara manyan idanunta tayi in shock
"Deen.."
"am proposing the second,time, will you marry me?"
"Deen get up"
"saikin amsa min"
"Deen.."
"I mean it"
"ok..ok" tafada stana furzar da huci
"YES"
wani irin wara idanu Deen yayi
"dagaske!"
saiya tashi yadawo kan kujerar datake hakan yasata dan ja baya
"dagaske?"
"eh..eh" tafada tana qara jabaya
"yaushe? gobe? jibi? inkoma ingayama ummie ta,turo gobe ayi komai?"
tashi tayi tana kallonshi idanu aware
"aturo ina? are you serious?"
"anan mana, look barima natafi yanzunnan" yafada yana tashi
saurin shan gabanshi tayi
"ina zaka?"
"wurin ummie mana dole nafadamata yau asan yadda za'ayi agama komai on time"
"mene? are you alright? ina kata6a jin anyi hakan? Kawai daga cewa yes shikenan?"
"to me zamu jira?" inji Deen kamar zaiyi kuka
"bakaga karatu nake ba? saina gama ko ana tada wata magana"
tsayawa yayi yana kallonta kamar wanda ake fadawa mugun abu
"ka..me? Zainab sokike ki kasheni?"
"na kasheka kamar yaya?"
"Zainab bakiji abinda kikace ba? wai saikin gama karatu lokacin na sheqa kenan, haba wasane ma wannan"
"kaike daukarshi wasa but am damn serious" tafada da iya gaskiyarta
tsayawa yayi yana kallonta for some seconds saikuma yayi murmushi yace
"to ai shikenan, we shall see.. ki yima ummie magana nizan tafi"
"kamar ya we shall see? me kake nufi da hakan?"
"time will tell, yanzu dai kiyiwa ummy magana bari nashigo muku da tsarabarku" yafada yana juyawa yafice daga falon fuskarshi dauke dawani murmushi dashi kadai yasan ma'anar kayanshi
tadan jima bayan fitarshi atsaye cikin jujjuya maganar Deen sannan ta girgiza kai tahau sama don kiran ummy
tareda ummy da batool suka dawo inda tundaga sama suke hango akwatinan biyun da Deen ya ajiye atsakar falon
wara idanu duk sukayi suna ida saukowa ummy na tambayarshi wadannan kayan fa
murmushi Kawai yayi yace
"tsarabarku ce ummy, ayi hqr"
mita ummy tafara akan kayan sunyi yawa daga baya kuma takoma godiya
sai alokacin suka gaisa da batool itama tana mashi godiyar tsarabar
anan sukayi sallama ummy taba zee ledar data sauko daita tace tabashi yaba kaka
Deen yayi godiya yajuya yafita zee na bayanshi don yimashi rakiya
saida suka isa parking space sannan yajuyo yana kallon zee itakuma ta miqamashi ledar da ummy tabata tana mashi godiyar tsarabar
murmushi Kawai yayi daidai xaiyi magana mota tashigo gidan
tsayawa sukayi suna kallon motar harta qaraso wajen parking din ta parka
Aymaan da abbu ne suka fito daga motar
sunyi mammakin ganin Deen sosai don basusan da dawowarsu ba
har qasa ya tsugunna ya gaida abbu cikin girmamawa sannan sukayi musabaha da Aymaan
nan suke tambayarshi saukar yaushe yace yau
sudan dauki lokaci suna dan ta6a fira kafin suyi sallama su shige ciki
bankwana suka sakeyi da zee sannan yashige motar yatada
zee na nan tsaye haryaja yafice daga gidan sannan tajuya takoma ciki
koda takoma ciki iskewa tayi duk suna falon sunata duba kayan da Deen yakawo
akwatina biyune da qarami da babba, kallo daya zakayiwa kayan qaramun akwatin kasan na zee ne inda dayan kuma yayima kingin yan gidan
sosai suke yaba kyawun kayan harda Aymaan wanda yanzu alhamdulillah bayajin komai gameda relationship din zee da Deen don sosai allah ya sassautamashi yakuma sa yayi facing din gaskiya cewa zee fa ta Deen ce. cikin ikon allah yarage jin yadda yakeji sosai akan zee don yanzu yama fara hasasowa kanshi wata, tunaninta ya addabeshi a yan kwanakinnan kullum bayada aiki sai tunaninta, saidai yasan abune dakamar wuya ta amince mashi but he'll try his best
Bayan kwanaki uku da dawowarsu daga saudiya Deen da mussadiq suka daga zuwa Nigeria inda Deen zaije ne don waiwayar masana'antarshi shikuma mussadiq yajene da sunan rakiya amma abinda yakaishi daban
agidan Deen suka sauka inda saida suka huta sosai sannan suka nufi gidansu Lailah bisa matsawar mussadiq
sosai akayimasu tarbar mutunci inda ahalin sukayi matuqar farinciki da ziyarar tasu ta bazata
ganin mussadiq da Lailah tayi aranar yaqara tabbatar mata da abubbuwan data dade tana hasashe
tun bayan dawowarsu daga Dubai takasa nutsuwa, zuciyarta takasa samun sallama inda tunanin twin din Deen yabi yayi mata bake2 yayimata katutu azuciya
kullum idan ta zauna kalamanshi Kawai kemata yawo a kwalwa, yanayin maganarshi, salonshi, komai nashi is different
dukda kammaninsu daya da Deen saidai hallayarsu da yanayinsu ya banbanta, yayinda Deen keda sanyi sosai shi mussadiq talura is way too classic gashi kallo daya zakamashi ka iya jerashi a layin miskilai, haka Kawai takejin hallayar mussadiq yafi burgeta bisaga na Deen.
koda ta sauko don su gaisa kasa looking directly at him tayi, abin mammaki saigashi maganarshi ta tabbata don yau akallo daya taganeshi dukda shigar da sukayi iri daya.
fira sosai sukesha a tsakaninsu most especially Deen da Abba don mussadiq be cika magana sai shegen kallon daya kafe Lailah dashi babu ko kunyar su Abba
ganin abin na neman yin yawa yasa Lailah excusing kanta ta haye sama donta lura mussadiq be iya takaittacen kallo ba
saida zasu tafi sannan mamy takirata ta sauko don suyi bankwana inda anan suka d'an samu damar magana lokacin Deen da Abba are busy suna maganar aikin Deen
dagowa tayi ta kalleshi taga ita din shima yake kallo, ahankali yasakar mata guntun murmushinshi
itama d'an murmushin tayi ta sauke idanunta
"your phone?" yafada yana miqamata hannunshi
kallonshi tayi saikuma ta,miqamashi wayar hannunta
amsa yayi yay dialing sabon layin dayayi na Nigeria kiran yashigo wayarshi sannan ya katse kiran ya maida mata
"will call you later" yafada ahankali
kada kai Kawai tayi daidai nan su Deen suka qaraso wajen sukayi bankwana suka tafi.
kamar yadda yace din saigashi yakirata da daddare inda sukasha firarsu inda anan taqara sanin wasu daga cikin hallayenshi
babu abinda yafi burgeta gamedashi kamar yanayin maganarshi, idan zaiyi magana adunqule yake yinta ko abaibai wanda dole saika nutsu sosai zaka gane ma'anarta. he just know how to deal with words.
ga slang dinshi na Arab turanci yake mata amma da karin larabci saitaji turancin wani iri amma kuma ga mammakinta tamafison irin nashi din.
sati daya sukayi a Nigeria inda cikin satin Deen yashiga busy sosai saboda aikin dasuka tararmashi yayinda shikuma mussadiq ya 6ata satin wajen yad'a manufarshi awajen Lailah
Acikin satin ya bayyanama Lailah son dayake mata kuma yasamu kar6uwa don alokacin yariga yagama daita yatafi da imaninta
a kwanansu na goma suka juyo Dubai lokacin hatta yan gidansu Lailah sunsan da soyayyar dake tsakaninta da mussadiq, Deen yafi kowa kowa farinciki da hakan don aganinshi sunyi mugun dacewa dajuna
a bangaren Aymaan kuwa tunda yaga Deen agidansu lokacin dasuka dawo daga saudiya yafara neman hanyar yad'a manufarshi ga Aysha.
at last ya tsaida wata shawarar dayaga ta hakan zaisamu kusanci daita
nan yafara bibiyar Aysha a school dinsu
yalura yarinyar is so timidshiyasa yake amfani da hakan wajen tsokanarta don sosai yake samun nishadi da hakan
tun suna fada idan suka hadu har wata iriyar shaquwa tashiga tsakaninsu wadda cikin qanqanin lokaci ta rikide takoma soyayya
anan Aysha tasan ainahin menene so saboda Aymaan ba baya ba afagen love da nuna kulawa
sai alokacin taga ashe soyayyar datayi da umar abaya ba soyayya bace wahala ce don batasan haka soyayya keda dadiba sai akan