Showing 303001 words to 306000 words out of 322641 words
Chapter 102 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
a fuskarshi ba
saida ya qaraso gabansu sannan ya dakata idanunshi akan Deen dashima nashi ke kanshi saiya dan sakarmashi guntun murmushi yabashi hannu
"aslm alaika"
amsar hannun Deen yayi shima yana danyin murmushin da iyakarshi lips
"wa'alaika sallam warahmatullah"
daga haka kowa yajanye hannunshi Aymaan ya maida kallonshi kan zee
"mutafi if you're through" yafada yana kallonta
sauke idanunta tayi daga kallonshi saboda wani kwarjini dayaimata
batace komai ba tazo tawuce tayi gaba Deen yabita da kallo
ahankali ya maida kallonshi kan Aymaan dake kallonshi haryanzu
dan murmushi Aymaan yasake yimashi sannan ahankali yace
"bansaniba ko awajenku it's proper amma anan kokuma ince a musulunce bedace namiji yatare mace daba muharramarshi ba ahanya harya tsaidata tsawon lokaci haka, the proper way shine zuwa gidansu yanemi izinin magabatanta kafin yayi hakan... fatan za'a gyara"
daga haka shima yajuya yabi bayan zee dahar tayi nisa
binshi da kallo Deen yayi cikin tafarfasar zuciya
idan yace be 6atamashi rai ba yayi qarya, he just appear from nowhere ya 6atamashi moment kuma har yanada gut din fadamashi baqar magana?
furzar da huci yayi ahankali yakai hannunshi akan sumarshi yana scratching dinta
***
tafiya suke babu mai cewa kowa komai, motar tawani dauki shiru kamar babu kowa ciki
Aymaan hankalinshi nakan tuqinshi itakuma idanunta nakan kwalta bata yarda ta janyesu akai ba
tafiya yake slowly don kwata2 motar bata gudu don gani zee take qila da aqafa take dasai tafi motar sauri saidai batace komai ba don ko hada ido bata yarda sunyiba don wani iri takeji sosai, jitake kamar ta 6ace daga motar ta huta, hakanan takejin rashin jindadin taddasu dayayi da Deen akuma yanayin daya taddasu, sosai takejin wani iri akan hakan, shi wonder me tunaninshi zaibashi akan hakan
jitake taqara su isa gida tafita daga motar saboda yadda takejin kanta amatuqar takure amma saiwani tafiya yake slowly kamar snail
ahankali taga ya gangara gefen titi hakan yasata dagowa tana kallon inda suka shiga
akaro nafarko tunda suka taho tajuyo ta kalleshi lokacin yana neman wurin parking
sake kallon wajen tayi sannan tasake juyowa ta kalleshi daidai shima yajuyo ya kalleta
murmushi yasakarmata hakan yasata janye idanunta kanshi Kawai takasa cewa komai
"want some ice cream?" yafada ahankali cikin romantic voice
dagowa tayi ta kalleshi saikuma tayi saurin kauda kai ganin irin kallon dayake mata namasu jin barci
girgiza kai tayi alamun A'a
murmushi Kawai yayi bece komai ba ya bude motar yafito ya zagayo ya budemata
dagowa tayi ta kalleshi
"get down dear" yafada ahankali
qara girgiza mashi kai tayi tace
"banason ice cream..."
"get down kona fiddoki dakaina" ya katseta da hakan
tsayawa tayi tana kallonshi kamar da mammaki sai gani tayi ya sunkuyo kamar zai daukota hakan yasata saurin yin baya tana cewa
"wait.. zan..zan fito" tafada tana zaro large eyes dinta
wani qayattacen murmushi yasaki yaja baya yana cewa
"better"
ahankali ta sauko tana sissine kai cikin kunya
murmushi Kawai yasakeyi yarufe kofar sannan ya nunamata hanya alamun suje
babu musu tafara tafiya suka nufi Icecream joint din
"which flavour kikeso?" inji Aymaan yana zaro wallet dinshi
"vanilla" ta amsa ahankali
juyawa yayi kan attendant din yayi mashi bayanin abunda sukeso
babu 6ata lokaci akayimusu packaging din Icecream din da snacks acikin yar babba babbar leda aka basu Aymaan ya amsa yabiya sannan suka juya
motarsu suka koma suka shiga Aymaan ya tada motar sukabar wajen
yanzu ma a slow speed suke tafiya motar tayi shiru
ahankali Aymaan ya waigo yadan kalli zee dake wasa da yatsunta ledar siyayyarsu akan cinyarta
maida kallonshi yayi kan titi yadanyi murmushi
"you still love him right?" ta tsinci muryarshi da fadin hakan
dagowa tayi ta kalleshi saikuma ta janyesu dasauri ganin shima yajuyo xai kalleta
"hmmm, am sorry na katsemuku moment dinku nasan I shouldnt interrupt you guys, sorry" yafada yana flashing dinta da murmushi
girgiza kai zee tayi dasauri tace
"ba yadda kayi tunani bane"
"koma dai yayane be kamata kidinga ke6ewa da namiji daba muharraminki ba, batool fa saidai takoma gida ita kadai wai ta nemeki bata ganki ba gashi anata kiran wayarki bakya picking... Zainab you're matured enough dazaki banbance daidai da akasinsa, bawai cewa nake karki kulashi ba ko karku ke6e kuyi magana ba but do that in a proper way... Makaranta fa yabiyoki yakuma jaki inda babu mutane, mezamu kira wannan?"
zee da tunda yafara magana takejin zuciyarta na bugawa sosai tadago ta kalleshi da idanunta dasuka fara durar ruwa
"it's.. it's not what you think" tafada ahankali
"waya gayamiki am thinking of something? am thinking of nothing Zainab.. I trust you kuma nasan hakan ba laifinki bane.. abinda Kawai nakeso na fahimtar dake shine try to do things in proper ways ok? ina baki shawara ne amatsayina na dan uwanki kuma yaya agareki, wannan dadewar dakikayi da dawowar da batool tayi babu ke bakisan iya tashin hankalin dazai iya jefamu aciki ba.. mu family dinki ne... we care about every slight thing about you... aduk abinda zakiyi kifara sa family dinki agaba kafin wani abin... shawara ce amma" ya qarashe da murmushi a fuskarshi saidai deepdown shikadai yasan abinda yakeji
ganinsu dayayi tareda Deen ba qaramin dokarmashi zuciya yayi ba kuma haryanzu zuciyarshi bata bar hucin zafi ba Kawai daurewa yake yana iyakar qoqarinshi wajen controlling kanshi
zee da jikinta yayi sanyi sosai da magangganunshi ta sauke idanunta qasa ahankali
"am sorry" tafada ahankali
murmushi yasakeyi
"don't be, Kawai dai ki kiyaye"
"insha allah" ta amsa asanyaye
murmushi yasakeyi
"now fiddo Icecream dinki kisha kar yayi melting"
"zansha idan muka isa gida"
"no kisha yanzu, idan ba hakan ba zan maki wata fassarar"
kallonshi tayi, kamar zatayi magana saikuma tafasa ta bude ledar ta fiddo daya daga cikin robobin Icecream din ta bude tasa dan spoon din ta diba takai baki saita dago idanunta suka hada ido
murmushi yayi mata itama tadan maida mashi tana sauke idanun qasa
babu wanda yaqara magana acikinsu harsuka qarasa gida
parking yayi a parking space sannan suka fito atare
atare suka shiga cikin gidan zee agaba Aymaan abaya
murda handle din kofar tayi tashiga da sallama hannunta riqeda da ledar snacks din
ummie da batool dake falon suka dago suna amsa sallamar
qarasowa zee tayi cikin falon tana dan murmushi azuciyarta tana tunanin mezata gayawa ummie idan tace ina ta tsaya
"A'a? harkun dawo? kungama practical din" inji ummie tana kallon zee
"p..practical?"
"eh sungama.. koda najema gab da zasu gamane don ko 10mins banyiba dazuwa suka fito" inji Aymaan dashima yashigo dakin
kallon Aymaan tayi suka hada ido ya kauda kai
"ayyah, sannu" inji ummie tana maida hankalinta kan t.v tana cigaba da kallon program din datake kallo
"bari nahau sama" inji Aymaan yana wucewa zee tabishi da kallo qasa qasa
"inyee meye wannan din?" taji muryar batool data taso tadawo kusada ita nacewa hakan tana fizge ledar hannunta
hade rai zee tayi tfara qoqarin amsa hakan yasa batool miqewa tayi hanyar sama
miqewa itama tayi tabita tana saita bata ledarta
murmushi Kawai ummie tayi tana girgiza kai tacigaba da kallonta
asama kau bayan sungama guje2nsu suka zube agado kowa na maida numfashi
batool ce tajuyo tana kallon
zee dake kallon sama har lokacin tana maida numfashi
"ina kika tsaya ne zee? babu inda ban nemeki ba amma banganki ba kuma inata kiran numberki bakya picking"
juyowa itama zee tayi tana kallonta
shiru tadanyi sannan tace
"wane practical,ummie ke magana akai?"
harara batool ta gallamata
"na tambayeki kina amsamin tambaya da tambaya?"
ajiyar zuciya zee tayi tamaida kallonta sama tace
"ina tareda Deen ne"
"Deen?" batool tafada cikin mammaki
"yes"
"kamar yaya kuna tareda Deen? doing what? yaushe ma kika fara saurararshi?" inji batool tana kallonta sosai
qara sauke wata ajiyar zuciyar tayi sannan tace
"yau... yau na tsaya na saurareshi, he told me everything" tafada batareda tabar kallon sama dakin ba
"what did he told you?"
"labarin da tsayi" zee ta amsa
"to amma yafada.miki dalilin tafiyarshi?"
"yes... kaka tasa suka gudu saboda gudun kar asirinta yatonu cewar batada wata alaqa da Deen, taji ajikinta sirrinta zai bayyana shiyasa ta yanke wannan hukuncin shikuma Deen bayada option dole yabita saboda tayi threaten zata tafi ita kadai lokacin dayaso kawomata gardama, shikuma baya iya rabuwa daita kasancewar itace komai nashi, ita kadai,yabude ido yagani a duniya amatsayin danginshi shiyasa yabita suka gudun"
shiru batool tayi tunda tafara maganar harta kai aya
"that makes sense amma duk wayonta gashi sirrin ya bayyana, waya gayamata anama allah wayau?" inji batool
ajiyar zuciya zee tasake saukewa sannan ahankali tace
"kuma... kuma wai ashe yadawo 3weeks bayan tafiyarshi, can you imagine wai daddy saiya cemashi nayi aure yakuma yimishi koran kare? banta6a tunanin daddy zaiyi haka ba"
"daddyn yayi hakan?" inji batool cikin mammaki
"yes.. nima nayi mammaki sosai, meyasa daddy zaiyi hakan? koda yayi hakan ne don yarama ai bekamata yace nayi aure ba, tunda harya dawo dakanshi ai yakamata ya tsaya ya saurareshi idan ma hukunci zai yanke mashi saiya yanke mashi wanda bekai wannan tsauri ba don wannan ba Deen kadai yayimawa ba harda ni, 3weeks da tafiyarshi lokacin ina cikin halin desperation, imagine da lokacin yasanar dani dawowarshi da bansha duk wahalar danasha ba"
ajiyar zuciya batool ta sauke
"gaskiya kamar daddy be kyauta ba amma saidai bamusan dalilin dayasa yayi hakan ba.. anyway komai yawuce ai gashi yadawo kamar ba'ayi ba"
lumshe ido Kawai zee tayi batace komai ba
"yanzu wane matsayi yake agareki"
bude idanu tayi tajuyo tadan kalleta
"kamar ya?"
"ina nufin ya matsayin soyayyarku?"
"wai he want another chance"
"zaki bashi?"
shiru tadanyi saikuma tace
"I don't know"
shiru yadan ratsa dakin kafin can zee tasake katse shirun da
"wane practical ummie ke magana akai dazu?"
dan ta6e baki batool tayi tace
"well, wannan duk shirin Akhie ne, lokaci daya muka dawo dashi ganin nikadai nadawo babu ke yasashi tambayata nagayamashi komai saiyace to bari yakoma school din yaduboki wai idan nashigo aka tambayeki ince kin tsaya wani practical ne ganin zaki dade yasa kikace intaho zaki kira yaya Aymaan yadawo dake..shikenan saiya juya ko shigowa beyiba yakoma school din"
shiru zee dake kallonta tunda tafara magana tayi saikuma ta sauke ajiyar zuciya ta maida idanunta ta lumshe tunani kala kala na kai kawo a kwalwarta
***
tsaye yake agaban balcony inda yazama favorite wurinshi yana kallon harabar gidan dake tarr da haske kamar ba dare ba
mussadiq ne yashigo wajen waya kare a kunnenshi ya qaraso wurin kujeru yaja guda ya zauna yana cigaba da wayarshi yana kallon bayan Deen
saida yagama wayar sannan yadanyi murmushi yana ajiye wayar kan table
"eh gaskiya ka afka dayawa..love is suffering someone here" yafada cikin sigar tsokana
Deen beko juyoba bare ya tanka mashi
"you know what yakamata karage tunani, don taqi sauraronka saika tsangwami kanka haka? dama nasan wannan stubborn girl din bazata saukoba so easily, kabi komai ahankali komai zai warware"
juyowa Deen yayi ya 6allamashi harara
"karka qara kiranta stubborn"
yar dariya mussadiq yayi yace
"but she is.. wannan yarinyar? uhmm nikadai nasan halinta"
"baka kaini sanin halinta ba Mallam"
ta6e baki mussadiq yayi
"whatever Kawai dai nidai shawara zanbaka karage saka kanka damuwa don taqi sauraronka"
"waya gayamaka taqi saurarona? ta saurareni nakuma gayamata komai"
"wow, yaushe?"
qarasowa Deen yayi wajenshi shima yazauna kan kujera daya
"yau, I told her everything"
"wow, sai tace me?"
"bata kaiga magana ba wannan gayen yazo?"
"who?"
"wannan doctor din"
yatsine fuska mussadiq yayi saikuma yata6e baki
"that annoying fringe"
"kabar cemashi hakan"
"why? I don't like him from the beginning"
"amma yanada kirki"
"hmmm koba kirki ba"
"seriously mussadiq yakamata kabar gaba dashi saboda mutumin kirki ne, harda shifa wajen taimaka mana mukayi re-uniting ga yadda yakula da ummy lokacin datayi collapsing, the man has a good heart"
ta6e baki mussadiq yayi ya cigaba da danne dannenshi Kawai
"saidai nalura kamar yanason zee"
"fidda kamar, sonta yakeyi kuma shi taqama yake cousin dinta ne shiyasa yake wani jijji dakai yana nuna isa akanta, abinda yafi 6atamin rai gameda shi kenan" inji mussadiq
ajiyar zuciya Deen ya sauke yace
"koma menene nata zee tawace.. insha allah, insha allah zee matata ce"
"allah yasa"
"amin ya rabb"
"kunyi waya da master din naka?" inji mussadiq
"yes.. munyi magana nagayamashi komai though briefly, nasan very soon zasu duro Dubai"
"kace nakusan ganin your so called kaka" inji mussadiq yana dan ta6e baki
wani kallo deen yayimashi
"kardai kafadi wani abu akan kakata"
"to mai kaka" mussadiq yafada yana ta6e baki sannan yamaida hankalinshi kan wayar hannunshi shikuma Deen ya jingina da kujera ya harde hannayenshi a qirji yana kallon sararin samaniya....✍?
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/7/21, 4:46 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*096*
*NIGERIA*
Sosai Alhaji Shamsu ke mammakin wannan al'amari
kiran wayar Deen ba qaramin sashi a rud'ani yayi ba, ga wasu magangganu daya gayamashi masu birkita kwalwa
dukda sama sama Deen yabashi labarin kasancewar labarin bana waya bane amma yagane abinda Deen keson gayamashi
idan ba kunnuwanshi suka ji ba daidaiba yana nufin yahadu dawasu dayake ikirarin familynshi ne
tayaya hakan zaya faru bayan tunfarko yabashi labarinshi inda yacemashi bayada sai kaka kuma shi bahaushe ne, ya kwatsam kuma zaice yahadu dawasu kuma family dinshi ne? kuma bama a qasarnan ba a Dubai?
sosai kan Alhajin ya kulle yakasa samun amsoshin tambayoyin daketa kai kawo a kwalwarshi
kenan Deen nacikin qoshin lafiya duk kwanakinnan? fadin tashin hankalin dasuka shiga a yan kwanakinnan 6ata bakine don kowa hankalinshi atashe yake dajin su Deen shiru musanmman kaka dahar wata rama tayi saboda tashin hankali da damuwa
tunawa yayi da maganar Deen nacewa don allah yasama musu visa sutaho harda kaka Dubai akwai qullallen al'amarin da dole kaka zata iya warwarewa
dama kuma Alhajin yayi niyyar zuwa Dubai din duk saboda jinshi shiru da akayi don harya gama komai na tafiyarshi inda zaibi jirgin dazai tashi jibi
tattaunawarsu da Deen yasashi fara cuku cukun nema masu kakan visa suma inda tafiyar zata hada dashi da hajiya da kaka sai subar su Lailah da Afrah gidan qanin Alhajin
koda labari yaje ga Lailah na tafiyar tasu saita burkuce ta dinga kuka ita don allah aje daita
sosai ta tada hankalinta akan hakan don dama bayan kaka babu wanda yakaita shiga damuwar rashin Deen don kusan kodayaushe cikin kuka take duk tayi fayau daita don damuwa
izuwa yanzu su mamy duksun gano son Deen take hakan yasa take basu tausayi
ganin cewa idan ba'a tafi daita dinba zata qara shiga damuwa yasa Alhajin hadawa daita a tafiyar gashi dama anci sa'a suna cikin hutun Makaranta
nan da nan Alhajin yayi cuku cukun tafiyarsu inda adaren ranar tafiyar yagama settling komai inda Washegari zasubi jirgin qarfe goman safe mai zuwa Dubai
ranar ko barcin kirki kaka kasayi tayi, dukda Alhajin be gayamata sunyi magana da Deen ba don ita gani take Alhajin ya yarda ne sutafi nemanshi tare don tunfarko dama tanace zata bishi Alhajin ne be yarda ba
haka takusan kwanan zaune zuciyarta fall addu'ar bayyanar Deen, danasanin barinshi wannan tafiyar kau tayishi yafi cikin kwando
Washegari tunda safe suka fara shirye shiryen tafiya don jirgin nasu dawuri zai tashi
qarfe tara tayimasu cikin airport inda cikin qanqanin lokaci suka gama settling komai qarfe goma nayi dota jirginsu ya lula sararin samaniya yadauki hanyar dubai
***
ahankali Aymaan ke jujjuya dan qaramin puzzle box din hannunshi yana arranging din puzzle din, daya kumayi arranging dinsu sai yayi scattering dinsu saikuma yasake arranging dinsu
dagowa Ahmad yayi karo na ba adadi ya kalleshi saikuma yadan girgiza kai
"Aymaan"
dan dakatar da abinda yakeyi yayi batareda ya dago ya kalleshi ba kuma bece komai ba
gyara zama Ahmad yayi yana kallonshi sosai
"Aymaan wai meke damunka ne kwanannan? yaushe muka fara 6oyewa juna damuwar juna? Aymaan you're not ok these days kuma you don't want to share your problem with anyone, aganinka barin damuwa aranka shine mafita?" yafada yana kallon Aymaan daya cigaba da jujjuya abin hannunshi kamar badashi yake ba
ganin beda niyyar amsa mashi kuma baxai amsa mashin ba yasa ya yunkura yaqwace puzzle box din daga hannunshi yana cewa
"am talking to you idiot!"
komawa jikin cushion din Kawai Aymaan yayi ya lumshe ido yana sauke nannauyan numfashi
"Aymaan... listen Aymaan barin kashi aciki baya maganin yunwa, kana cikin damuwa why not kayi sharing dinta dani? ko babu komai zakaji sauqi na kayi sharing din damuwarka dawani kuma ina iya samamana shawara dazata taimaka, ba haka muke dakai ba kaima kasani we're like brothers muna sharing damuwarmu mukuma zauna mu samama kanmu mafita atare, banajin dadin ganinka a wannan yanayin kwata2" yafada cikin kwantar da murya yana kallon Aymaan da har lokacin idanunshi ke a lumshe
"Ka gayamin damuwarka please, I can help"
"you can't help" Aymaan yafada ahankali still idanunshi a lumshe
"meyasa? just tell me, we can't say" inji Ahmad
sai a lokacin Aymaan yabude idanunshi wadanda suka kada sosai ya kalli Ahmad
"you can't Ahmad, baxaka iya taimakamin ahalin danake ciki ba, I... am broken" yaqarashe cikin raunin murya
ganin hakan yasa Ahmad saurin dawowa kusadashi yana kama hannunshi daya
"meyasa nafara son abinda tunfarko ba nawa bane? why? meyasa nafara son wacce bazata ta6a mayarmin da so ba? why?"
"Aymaan..."
"kasan ciwon dake tattare dason wanda baya sonka kuma baxai ta6a sonka ba? kasan zafin dake tattare da ganin wanda kakeso yana son wani? ni haka tawa qaddarar so zatazomin? ada soyayya stuffs duk shirme na daukesu ina ganin Kawai rashin aikin yine amma jibeni yanzu.. crying over love while wacce nakeyi domin ta ma batasan inayi ba, what did i do to deserve this Ahmad? meye narasa na d'a namiji da xaisa bazata soni ba nima? meye Deen yafini? me Deen yafini dashi? meyasa ko sau dayane bazata waiwayeni ba? at least tanuna tasan inayi, tanuna tasan dani, what did I do to deserve all these pain?"
sosai hankalin Ahmad yatashi ganin yadda Aymaan ke hawaye sosai, kana kallonshi zakasan he's really in pain
"Aymaan please... kabar kukan nan haba kamar ba namiji ba"
"tears are not sign of weakness, but of courage. hiding your emotions is self destructive and will never allow you to heal... haka Zainab ta ta6a gayamin kuma yanzu nagane hakan, babu abinda kecikin maganarta sai gaskiya, my heart is hurting ahmad, it's hurting terribly" yafada wasu hawayen nasake saukomashi
Ahmad da jikinshi yayi sanyi sosai yajawo Aymaan jikinshi cikin sigar rarrashi yana cewa
"Aymaan ba kome mutum keso yake zama alhairi agareshi, wani abin kanasonshi amma ba alhairi bane agareka shiyasa allah ke hanaka, allah shine mafi sanin daidai kuma ya tsara komai na rayuwarmu da dadewa, kayi hqr Aymaan kadage da addu'a, idan zee ce mafi alhairi agareka allah ya karkato da hankalinta kanka idan ba ita bace allah yaxa6a maka mafi alhairi, ka daina ganin laifin Deen ko zee, kadage da addu'a Kawai, wani baya ta6a auran matar wani"
haka Ahmad yayita kwantarma Aymaan hankali da kalaman rarrashi harsaida Aymaan yaji sassaucin zugin da zuciyarshi kemashi
***
A babban filin jirgin garin Abu dhabi jirginsu yasauka inda cikin qanqanin lokaci pasinjojin jirgin suka shiga saukowa daga jirgin
can na hango su Alhaji Shamsu cikin masu saukowa tareda su kaka suna saukowa suma
cikin qanqanin lokaci suka sauko sukayi clearing komai suka amshi kayansu
dukda damuwar dasuke ciki hakan be hanasu ganin haduwar qasar ba wacce tahada jinsin mutane qabilu daban daban
ahankali suke takawa suna nufar hanyar barin airport din dake dauke da mutane