Showing 165001 words to 168000 words out of 322641 words

Chapter 56 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6130

ta bayan zee sannan ta dago fuskarta dago zee daga jikinta tayi cupping fuskarta


"Kiyi hqr kinji? Allah na tareda masu hqr, insha allah komai zai wuce maki kamar be ta6a faruwa ba, be strong and move on. Dama tun tasowarki badashi kike rayuwa ba, daga baya ne yashigo rayuwarki yanzu kuma ya tafi, ki dauki Hakan kamar haduwar hadarin kaka ne, ya hada kuma ya baje ya 6ace 6att kamar ba'ayi ba

Ki dauki naki case dinma Hakan, ki dauka baki ta6a rayuwa dashi ba, karki bari abinda yayimiki yayi tasiri aranki da har zaiyi pinning dinki down, fight Zainab! Fight the feelings and move on!"


Mummy batasan hawaye take ba Saida taga zee takai hannu tana sharemata Hakan yasa ta sake jawota a jikinta tasake rungumeta


Lumshe idanu zee tasakeyi tana jin inama inama

Inama abubbuwan da mummy ke lissafowa yanzu suna da sauqin yi

Inama tana iya yakiceshi kamar yadda tace ta cigaba da gudanar da rayuwarta kamar da, inama inama 😭


Ahankali ta bude idanunta sai suka sauka acikin na daddy sake tsaye bakin kofa Tundazu basusan shigowarshi ba


He looked very sad and disturbed, idanunshi shima sun Kada sosai yana kallon diyar tashi with pain all over his face


Tashi tayi daga kafadar mummy tana cigaba da kallon daddy.

Hakan yasa mummy Juyawa inda take kallo taga ashe daddy ne


Ahankali daddy shima ya qaraso bakin gadon ya zauna shima kusada mummy ya Kamo hannunta guda

"daughter" yafada a matuqar sanyaye


Cigaba da kallonshi shima tayi kamar mai karantar wani abu A fuskarshi

"come dear, come" yafada yana miqomata hannayenshi duka biyun


Ahankali ta matso ta shige cikinsu a sanyaye daddy ya rufesu a bayanta


Rasa da wadanne kalamai zaiyi amfani dasu wajen rarrashinta yayi Hakan yasashi cewa
"Am sorry daughter, am so sorry!"

Qara narkemashi ajiki tayi tana qara rufe idanunta


Sun dan jima ahakan sannan sukayi breaking hug din suka ba Dr din damar dubata dakyau


Saida yagama dubata yayi mata Tambayoyi wanda mostly duk qin amsawa tayi Saidai idan yace meke yimata ciwo ta nunamashi saitin zuciyarta kawai don ita kadai kemata radadi jitake kamar a ciremata ita ta huta.


Cewa Dr yayi ahada mata tea a bata tasha kafin yadawo yaqara yimata allurar barci don sosai zata taimaka mata wajen ragemata damuwa wanda itace sanadin ciwon zuciyar datake complaining din


Yadda yace din akayi

Kakkauran tea aka hada mata daddy ya amsa yana bata a baki tanasha har Saida yafi rabi sannan ta kauda kai alamun ta qoshi

Ganin Hakan yasa daddy kiran Dr din yazo ya harhada alluran dazaimata yayi mata su


Ba'a qara minti biyar ba wani barcin yazo yaqara yin awon gaba daita.


A lokacin ne daddy yasamu damar kiran yan uwa da abokan arziqi yana masu albishir farkawarta, sai washe baki yake cikin farinciki



*WASHEGARI*


Tunda garin allah ya waye mutane keta tururuwar zuwa ganin zee


Daddy baki be rufuwa baya zaune baya tsaye kodayaushe yana kan hanyar rako yan dubiyan ganinta ko kuma raka masu tafiya waje


Sosai manyan mutane keta ziyarta asibitin don Saida kowa yasan da Hakan yau ga sadakar da mummy tasa akayita yima mutane patients na take away din jollof da swan water dukda dai suma patients din ba baya ba don saika tara kake iya zuwa irin wannan asibitin.


Zee kau haryanzu babu uhm ba uhm uhm, duk wanda yazo dubanta Saidai tabishi da idanu, idan kuma ana yimata ya jiki Saidai ta amsa ta hanyar lumshe idanu ta bude kawai


Kayan dubiya kau tashasu qumshi qumshi don duk wanda yazo ganinta saiya ajiye mata qatuwar ledar kayan dubiyan shi


Acikin masu zuwa dubata harda Asaad da qannenshi biyu mata

Yanmatan sai wani daddage hanci sukeyi kamar yadda suka saba, Asaad mane ke da dan sauqi sauqi don shi ya nutsu sai kallon zee da duk basu isheta kallo ba yakeyi kamar zai hadiyeta.


Haka suma suka qaraci zamansu har lokacin tafiyarsu yayi inda anan Asaad ya ajiye mata damin kudi a gefenta sannan shima yabi bayan masu fita


Yadda bata kalli kudaden ba Haka shima wanda ya ajiyesu din bata kalleshi saima maida idanu datayi ta lumshe tana sauraron yadda daddy keta yabon kirki da hankalin Asaad.


Haka dai suka qarasa Wunin ranar cikin yin baqin yan dubiya don da wasu sun shigo sai wasu su fita haka sukaitayi har dare sannan abin ya lafa itakuma zee sai a lokacin tasamu nutsuwar yin tunaninta dakyau.


Saidai bata dade dafara tunanin ba Dr yasake dawowa yayi mata allurar barci don tunanin ne ba'ason tafiye yi a wannan condition din shiyasa akama bari yan dubiyan sukaita zuwa ko sun Janye hankalinta daga tunanin yanzu kuma da babu su sai akayi mata allurar don tayi barci tasamu rest of mind.



Washegari kau baqi yan Ruma ne suka sake dawowa ciki harda Umma

Sosai Zuwansu yadan debe mata kewa musanmman ma da akazo da yaran


Haka taita wasa da sultan da aka doromata shi saman gadonta kamar yadda ta buqata tanayi tana sauraron su mummy da su Aunty raliya daketa firarrakinsu


Duk lokacin da ta kalli sultan sai ta tuna Da ranar da Deen ke wasa dashi acan Ruma lokacin bikin Aunty Feenah



The smile, the dimple, fararen haqoran, the pink lips da kwantaccen sajenshi, dukkansu sai flashing sukeyi a idanunta


Ahankali ta hada goshinta dana sultan kamar yadda Deen yayi wancan karon

Bangalewa sultan yayi da Dariya kamar yadda yayi wancan lokacin, itama tsintar kanta tayi tana murmushi


Ahankali yadda ita kadai zata iya jin abinda take cewa tafara magana


"Bansan abinda yasa ake kiranshi karayar zuciya ba(heartbreak)

Jinake kamar wani sashe na jikina ma ya karye"


Qara bangale mata baki sultan da besan abinda take cewa ba yayi, itama murmushi mai ciwo tayi sannan ta cigaba da cewa

" Wasu na cewa da ciwo ka jira wani


Wasu na cewa da ciwo ka manta da wani

Amma Mafi ciwo aciki shine karasa abinda zakayi aciki

Ka jira?

ko ka manta?"


" Ka yimin rauni fiyeda yadda na cancanta, dama haka kakeda mugunta?

Naso ka fiyeda yadda ka cancanta
Dama haka shashanci na yakai?"

Hannu sultan ya dago ya dora akan bakinta ita kuma ta bude bakin ta dan yimashi cizon wasa

Saurin zare yatsarshi yayi daga bakin nata yana dan 6ata fuska dukda ba sosai ba ta ciza

"The worst feeling is not being lonely, it's being forgotten by the one you'll never forget" taqara fada cikin rada tana kallon puppy face din sultan


Fashewa sultan din yayi da kuka hakan yasa hankalin mutanen dakin dawowa kansu


"oh ni sultan ka cika rigima wlh, kawoshi karya dameki" inji Aunty Raliya tana zuwa wajenta ta daukeshi


Zee batace komai ba sai komawa datayi ta jingina da jikin gadon ta lumshe idanunta tana cigaba da sauraron firarrakinsu.


Yau kasancewar surukar daddy na asibitin Hakan yasa yau ba'a zauna asibitin ba wai saboda kunya Saidai kiran dayaitayi ma mummy dik lokacin da yaso jin muryar zee sai ta bata su gaisa dukda ba magana take ba sosai don daga farkawarta zuwa yanzu za'a iya qirga magangganunta datayi




Sai can da marece wajajen 5pm su Umma sukayi shirin tafiya inda kafin sutafi Saida kowanne yaita yimata nasiha da rarrashinta akan tayi qoqari ta manta dashi tayi moving on

Jinsu kawai take amma a zuciyarta tasan Hakan da kamar wuya don a dare guda zaka iya kamuwa da son mutum amma zaka iya 6ata shekarun rayuwarka batareda ka iya mantawa dashi ba

*MANTUWA* kalmace mai sauqi wajen fada a baki Amma mai matuqar wuya a aikace.



Washegari da zee ta cika kwana takwas a asibitin Ummu batool ta dira Nigeria


Sosai su daddy sukayi mammakin zuwan nata don bata sanar dasu zatazo ba saboda sanin halin daddy yana iya cewa basai tazoba itakuma bazata iya ba don gashi dama ta dade rabonta da Nigeria kuma ga rashin lafiyar zee wanda take jinta kamar ita ta tsungunna ta haifeta shiyasa Koda ya fadamasu tafara shirye shiryen tahowa Nigeria din batareda yasani ba.


Sosai ta tausayawa zee data ganta don acikin yan kwanakinnan ta chanza sosai

She's no more that active Zainab din ta koma wata silent and dull daita, ga ramar datayi acikin yan kwanakinnan wanda ya bayyana sosai


Sosai Ummu batool ta tausaya mata don harda kukanta tana cewa sai allah yasaka mata shima kuma haka


Itadai zee bata cewa komai kamar yadda ta saba a kwanakinnan Saidai deep down tanajin zafi idan aka soki Deen ko aka zageshi, ta rasa meyasa



Saida suka qara kwana biyu a asibitin kafin a sallamesu

Cikin kwana biyun nan Saida asaad yasake zuwa dubata kuma kamar wancan karon ya tisata gaba yanata kallo ko me yake kallo a jikin baqar African oho?


Haka ma babanshi Alhaji Abubakar, kusan kodayaushe tare suke tareda Alhaji Farouq don duk cikin ma abokan daddy Alhaji Abubakar yafi tsayawa taredashi a wannan halin shiyasa daddy ke qara jin qaunarshi a cikin zuciyarshi yakuma qara aminta dashi ganin yadda dukda butulcin da diyarshi tayimashi Hakan be hanashi tsayawa a side dinshi ba a lokacin buqata, da wani ne da gefe zai koma yana yimasu Dariya.



A ranar dasuka cika kwanaki goma sha daya aka sallamesu daga asibitin, lokacin zee ta murmure sosai physically Saidai ciwon da ba'a iya gani wato na zuciya.


A ranar saboda murna Saida daddy ya shirya yar kwarya kwaryar party na welcoming dinta home duk don ya faranta mata

Haka ma'aikatan gidan suma sukaita zuwa yimata barka da dawowa

Ita dai iyakarta dan murmushi daga kuma Hakan zata maida fuskarta yadda take.


Da daddare ma Ummu batool biyota tayi dakinta acewarta itama nan zata kwana wanda tayi Hakan ne a hikimance don kar abarta ita kadai har tasamu damar fara wannan tunanin da ba'aso din

Saidai abinda basu saniba shine shi abu idan yana a rai ko kasamu nutsuwa ko baka samu ba yana ranka kuma dole ka tunashi a kowanne motsin da zakayi


Kuma rashin ba zuciya damar nutsuwa tayi tunanin abinda ke qumshe a cikin ta shike jawo ta cinkushe ka rasa me keyima dadi a duniya




Zee ta chanza sosai, idan nace sosai ina nufin sosai da sosai


Ta tashi daga wannan zee din mai tsiwa, classic mai yawan ado da kwalliya takoma so silent, moody and simple


Rabon da ta zauna da niyyar yin kwalliya Koda simple makeup ne tun ranar introduction dinsu da za'ayi

Yanzu dai data samu tayi wanka ta zura duk abinda ya tari gabanta shikenan sai takoma ta nade a gado ko kuma ta zauna tayi shiru kamar kurma.


Sosai take ba su daddy tausayi shiyasa duk suke iya qoqarinsu wajen ganin sunyi cheering dinta up.

Haka kawai daddy zai kwashesu da zee da mummy da Ummu batool su fita park ko shopping ko cinema duk don cheering dinta up.

Mummy ma yanzu babu batun daure dauren fuska don wani sa'in ma Sai kazo ka taddata zaune tanata bata labari kala kala duk nasa nishadi


Haka ma Ummu batool wanda haryanzu tare suke kwana dakinta, itama tana iyakar bakin qoqarinta wajen ganin ta debemata kewa takuma sanyata nishadi


Saidai abinda basu saniba shine gangar jikinta ne kawai taredasu, ainahin ruhinta na taredashi ya tafi dashi

Without Deen she's incomplete and she'll never be complete.




***


Zaune suke a falo dukkansu ana kallo ana fira, zee a kwance tayi pillow da cinyar Ummu batool idanunta a lumshe dukda ba barcin take ba


Dagowa Ummu batool tayi ta kalli daddy da mummy tace
"Yaya da matar yaya, akwai wata magana dake son fadamaku amma ban saniba ko zakuyi maraba daita ba"


Duk maida hankalinsu sukayi akanta, mummy tace
"haba in-law kifadi koma menene mana, kinsan kinfi qarfin komai a wajen mu"


Murmushi Ummu batool tayi sannan tasa hannu ta shafa kan zee da idanunta ke a lumshe har lokacin

"mezai hana idan natashi komawa Dubai natafi da daughter ta? Aganina idan ta cira daga nan zataji sauqin abin sosai kuma zatayi saurin mantawa"


Duk shiru sukayi babu wanda yace komai, ganin Hakan yasata cigaba dacewa

"kuma kunga acan bazata kasance lonely ba, ga batool ga aymaan duk zasu debemata kewa, sai inga yafi taita zama anan, zuciyarta bazata yi saurin healing ba kamar idan tabar nan din"


Shiru wajen yasake dauka can sai daddy yace
"to banqi ta taki ba sister, amma karatunta fa? She's in 300level yanzu, baki ganin tafiyarta ba kamar watsarda wadannan shekarun data diba tana karatun bane?"


Murmushi Ummu batool tayi

"yaya kenan, to kai kanada tabbaci zata iya cigaba da karatun yanzu? Kuma a the same makarantar? Kufa kukace acan suka hadu kuma acan ne wajen haduwarsu kusan kodayaushe, bakwa ganin Koda taso manta komai zuwanta makarantar zai dinga dawo mata da memories din baya?"


Nan ma shiru sukayi

Sai ta cigaba dacewa

"amma idan can ne zamu sama mata wata makarantar Koda school of nursing ce, kuma zatayi saurin moving on acan don can garine dayasha banban da nan kuma haka ma mutanen ciki ba na nan bane, zatayi saurin manta past dinta, ga kuma batool zata debemata kewa sosai amma nan fa? Batada wani sublings ita kadai ce ko wannan ma kadai ya isheta"



Duk shiru suka sakeyi suna jujjuya maganar kuma suna hango tsantsar Gaskiyarta aciki, tabbas idan Zainab ta cirama qasarnan komai zaifi zomata da sauqi kuma zatayi saurin mancewa da past dinta.

Daddy ne yasake cewa
"hakane lil sis, abinda kika fada haka yake kuma muma zamuso tayi moving on, mun gaji da ganinta ahakan amma matsalar anan shine ita, anya zata yarda kuwa?"


"eh daddy" inji zee dake bisa cinyar Ummu batool still idanunta arufe


Duk juyowa sukayi suka kalleta itama daidai nan ta bude idanunta sannan ahankali ta miqe zaune tana kallonsu


"daddy na amince, zanbi Ummy (haka dama take kiran Ummu batool), inason nayi nisa da nan, inason intafi wani wajen, Hakan zaisa naji sauqin abinda nakeji.

Daddy, mummy please ku yarda, ku yarda ta tafi dani, please" tafada a sanyaye tana kallonsu da lumssasun idanunta da haryanzu haskensu be dawoba bawai don kuka ba A'a sai don rashin kukan don tunda abin yafaru bata zubar da ko digon hawaye ba da sunan kuka.



Ajiyar zuciya daddy ya sauke sannan yace
"Hakan zaisaki farinciki?"


Da sauri zee ta kadamashi kai cikin doqin da rabonsu da ganin irinshi a fuskarta har sun manta


Kallon juna daddy da mummy sukayi sukayi murmushi

Daddy yace
"shikenan, as you wish princess. Allah yasa Hakan shiyafi alhairi"


Ga mammakinsu sai sukaga wani qayattacen murmushi ya su6uce mata wanda rabon da su ga irinshi a fuskarta harsun manta... ✍️



Kwana biyun nan Saidai kuyi hqr dani, bana samun yin typing da wuri am kinda busy these days






Ummin fasihu πŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:39 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEEN πŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*








*054*






*DUBAI πŸŒ‡*








Cikin dan qanqanin lokaci su Ummu batool da Zainab suka fara shirin juyawa Dubai



Sosai Zainab ke zumudin zuwa qasar don koyaya take moody idan ka tado mata maganar tafiyar sai kaga tadan washe ba kuma ke jawo haka ba sai ganin datake databar qasar barinta zatayi da duk wani damuwanta


Siyayya sosai sukayi na tafiyar a bangaren daddy kuma yaje yayi musu settling komai na tafiyar.


Ranar da saura kwana biyu tafiyar sukaje zaga dangi don zee tayi bankwana dasu ciki harda yan uban daddy dake garin, su mutanen Ruma kau Saidai sukayi bankwana ta waya don lokacin yariga da ya qure bare suje kuma dama ai yan Ruman basu dade dazuwa ba.


Ranar daren dazasu bar qasar kasa barci zee tayi.


Ranar kwana tayi kuka, kukan da batayi ba tun faruwar wannan abin.


Toilet tashige ta kunna shower tashiga ciki tayita kukanta har Saida muryarta ta disashe

Ko daddare ma kasa rintsawa tayi, tana Kwance lamo kamar mai barci amma ba barcin take ba

Rayuwar dasukayi da Deen kawai take tariyowa a kwalwarta From A-Z

Tayi kukan da bata ta6a yiba a wannan daren shiyasa koda ta tashi washegari idanunta sukayi suntum suka kumbura


Su mummy basuyi mammakin haka ba don sunsan kukanta mai dalili ne, gwara ma tayi ta wanko abinda ke zuciyarta da ta barshi a daskare a wajen.



Jirgin qarfe 12pm zasu bi Hakan yasa sukabar gida Tun qarfe 11:15am suka dauki hanyar airport.


Tafiya suke sunata fira cikin raha ana Dariya banda zee da idanunta ke kafe akan glass din motar na gefenta tana kallon masu wucewa, tana yiwa Nigeria kallon qarshe don ta qudura a ranta ita da Nigeria kuma sai wani ikon allah





11:30am dot suka shigo filin jirgin saman


Parking daddy yayi a parking space sannan duk suka bubbude koffofin motar suka shiga fitowa.


Zee ce qarshen fitowa.

Wani iska ne ya bugi fuskarta Hakan yasa ta lumshe idanunta tana shaqar iskar sannan tasake budesu


Su daddy ke fiddo trolley dinsu daga cikin motar Yayinda itakuma ke bin harabar airport din da kallo ba wai na qauyanci, A'a na bankwana, tana bankwana da her beloved country Nigeria inda zata tabar mutane masu matuqar muhinmmanci acikinta wanda bata jin zasu qara haduwa nan kusa Saidai idan su zasu bita can.

she's gone too, maybe forever, maybe not.



12 saura minti goma su Ummu batool da Zainab sukayi bankwana dasu daddy


Rungume zee su mummy sukayi in turn duk suna iya qoqarin ganin basu bayyana rauninsu ba ta hanyar xubar da hawayen dake forming a idanunsu.


Itadai zee barin nata tayi suka gangaro don bataga amfanin riqesu ba

Saida sukaji ana qara sanarwa sannan suka haqura da bankwanan suka juya Ummu batool riqe da hannun zee suka fara tafiya


Tunda suka fara tafiya zee bata qara waigowa ba har Saida suka kai daidai kofar dazasu shiga cikin inda passengers din keta shiga sannan ta waigo


Su mummy da daddy ta hanga can nesa tsaye still suna kallonta, dan murmushi tayi musu dukda batada tabbacin zasu gani saboda nisan dasuka yima juna sannan ta juya suka ida shigewa.


Mummy ce ta dora fuskarta akan kafadar daddy hawayenta na gangaro mata

Dafe bayanta daddy yayi idanunshi akan kofar da suka shige shima yana trying very hard don ganin yayi controlling emotion dinshi.


Ahankali zee kebin Ummu batool dake riqe da hannunta still suka isa inda ake tantancewa aka tantancesu suma sannan suka shige ta inda zasu bi su 6illa filin da jirgin da zasu hau yake.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login