Showing 189001 words to 192000 words out of 322641 words
Chapter 64 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
dagaske mutanen nan biyu ne to akwai wani qullalen al'amari a tsakaninsu, haba kammanin yayi yawa, dole akwai wani abin da bamu sani ba"
"nima haka nake tunani Ahmad, abin da matuqar kulle kai"
Shiru yasake ratsa dakin kafin Ahmad ya dafa kafadar Aymaan
"you know what? Abinda ya kamata muyi anan shine kowannensu mu binciko asalinsu da komai gameda rayuwarsu sai muyi comparing dinsu mugani"
Kada kai Aymaan yayi
"perfect, nima ina ganin Hakan zaifi"
"yes, yanzu kai kaje kasamu zee din ta gayamaka komai gameda shi wannan din, nikuma zan samo mana komai gameda mussadiq"
"perfect! Insha allah Hakan za'ayi, zan qoqarta nasamu dukkan bayaninshi a wajenta"
Haka suka cigaba da shawarwarunsu har Saida Aymaan yaga dare nasonyi sosai sannan ya tashi suka fito sukayi sallama akan sai sun hadu, sannan yabar gidan
Da wannan firar tasu Aymaan ya kwana a rai
Haka maganar nan taita cinshi a rai a kingin kwanakin dasuka biyo baya, kodayaushe cikin son tunkarar zee da maganar yake amma be samun damar Hakan
Ana haka har watarana yasamu opportunity din ganawar daita lokacin ya sauko qasa ne daga stairs ya taddata ita kadai zaune a dining
Cikin jindadin Hakan ya tunkari dining room din yana jujjuya maganar dazai mata din.
"aslm alaiki ya ukhtie" yafada yana jan kujera ya zauna
Dagowa tayi daga abincin gabanta sai tadanyi yaqe
"wlsm" tafada a taqaice
"Me akeci ne babu ko tayi?" yafada yana dan leqa plate din
Murmushi tasakeyi sannan ta tura mashi plate din tana cewa
"bismillah"
Turo mata plate din yayi shima yana cewa
"alhamdullilah, am joking, kici ki qoshi ko kin qara qiba don naga Alamu batool wani Gani gani take mana kwanan nan, baki ga shiyasa nima na dage da cin abinci ba? Wannan yarinyar idan ta rainaka ka banu gwara kema ki dau mataki tun wuri"
Murmushi tasakeyi kawai tana jinjina barkwanci irin na wannan ahalin, kusan dik haka suke, zaiyi wuya ka xauna dasu basu saka Dariya ba
Shima dadi yaji, Ganin irin wannan murmushin a fuskarta ba qaramin sanyashi nishadi yake ba
Cigaba da cin abincinta tayi slowly tana jin idanunshi akanta, bata dago ba Bata kuma nuna tasan yana yi ba har Saida tadan qaraci da dan yawa sannan ta tura plate din gefe ta dauki cup din ruwa tadanyi sipping ruwan sannan ta ajiye
Dagowa tayi ta kamashi yana kallonta kamar yadda tayi zato
Daga mata girarenshi yayi dan murmushi a lip dinshi
Kauda kai tayi itama tana dan murmushi sannan taja kujerar ta baya tana niyyar tashi
"badai har kin qoshi ba?"
Kada mashi kai tayi tana ida tashi
"erm.. Please sit, magana zamuyi.. Idan babu damuwa" yafada yana kallonta
Dan Jimm tayi saikuma ta koma ta zauna tayi still tana saurarenshi
Furzar da iska yayi ahankali daga bakinshi sannan ya gyara zamanshi looking very serious
"Deen..."
Dagowa tayi tana kallonshi yanayinta na chanzawa
"I want to know everything about him" yafada yana kafeta da idanu kamar yadda itama ta kafeshi da nata
Qara jan kujerarta tayi baya ta miqe tsaye Hakan yasa shima ya miqe
"please Zainab, ki tsaya muyi wannan maganar tanada matuqar muhinmmanci"
"agareka ba? Ni aguna batada, please spare me" tafada tana niyyar tafiya
"Zainab Hakan nada matuqar muhinmmanci, shi zaisa abubbuwa da dama su warware mana, ciki harda asalin Deen"
"ni nasan waye shi don haka bana buqatar sanin komai gameda shi again, for me Deen is as Good as dead" tafada cikin qunar zuciya
"why? Meyasa zaki yanke wannan hukunci"
"I donโt own anyone any explanation, banason labarinshi, kai ko sunanshi banason naji an ambata, labarinshi dana sani dinma da nasan yadda zan goge shi a qwalwata da tuni nayi Hakan" tafara yunqurin barin wurin
"Koda kuwa ace bashi kika ganiba a supermarket?" maganar Aymaan ta dakatar da ita
Dan murmushin takaici tayi sannan ta juyo ta kalleshi
"dama ai ku baku ta6a yarda shi nake gani ba, kallon zauttaciya kuke min"
Ahankali Aymaan ya tako har yazo gabanta
"eh ada kallon zauttaciya nake maki, mai ganin fuskar saurayinta a fuskar kowa amma yanzu na fahimta, tabbas Deen ne kika gani, a park da supermarket Saidai bashi bane, kammaninsu ne daya amma bashi bane"
Kallon rashin fahimta tayimashi
"ban gane ba"
"meyasa baki tambayi kanki tayaya Deen yazo dubai ba? Tayaya yazama mai kudi a lokaci guda? Baki lura da motarshi ba? Harda bodyguards? Tayaya yazama haka a lokaci daya?"
Shiru tayi kawai tana kallonshi don ya soso mata inda ke mata kaikayi ne, wadannan Tambayoyin dasu take kwana take tashi a ranta.
"wannan ba Deen bane, sunanshi MUSADDIQ AL HASSAN"
"MUSADDIQ AL HASSAN?" inji zee cikin rashin fahimta
Kada kai Aymaan yayi
"yes, mu zauna na fadamaki komai" yafada yana nuna mata kujera
Kamar bazata yi yadda yace din ba, saikuma ta tafi tajawo kujerar ta zauna tareda sunkuyar da kai abin tausayi
Shima komawa yayi yaja kujerar daya zauna akai dazu ya zauna
"Zainab, Deen qaddararki ne.."
"nasani, mummunar qaddarata, am cursing the day I met him" ta katse shi da Hakan cikin muryar kuka
Ajiyar zuciya Aymaan ya sauke cikin quncin rai shima yace
"shiyasa nayi qoqarin taimaka miki da abinda zan iya don replacing Koda ba duka ba na farinciki dakika rasa a dalilinshi, nasan bazaki ta6a mantawa dashi ba so no need of making you forget him shiyasa nayi tunanin gano waye wannan Deen din dakuma nemoshi duk inda yake dukda ni kaina bansan abinda zanyi mashi ba ko abinda zai yimun.
Sai nasa batool ta satomin wayarki don samun wani hint ko kadan ne akanshi Saidai Koda na duba babu number wayar shi a wayarki saima na tuna bada layin Nigeria kike amfani ba don haka saina chanza akalar binciken nawa zuwa ga Hotuna sai naji inason sanin kammanin wannan mutumin da sunanshi kawai nakeji har lokacin
Abin mammaki da girgizarwa shine lokacin da nayi arba da fuskar mutumin da muka Hade a supermarket
Honestly kafin lokacin kallon zauttaciya kawai nake miki ganin a park kin nuna kinga Deen a supermarket ma daga ganin mutum kince shine, ko ba niba ko wani ne haka zaiyi tunani don kowa yasan wanda ake magana akai a Nigeria yake, yaushe yazo dubai kuma karki manta duk bamusan kammaninshi ba"
"Amma ganin wannan na cikin wayarki yasa kaina ya kulle, nace muddin wannan shine Deen to shine muka gani a supermarket
Hakan yasa kaina yasake kullewa, meya kawo Deen dubai?
Ganin kwalwata nason bursting saboda tunani saina yanke shawarar samun aboki kuma aminina da muka saba zama mu warware matsalolinmu atare wato Ahmad
Saidai me? Ina gwadamashi pics din Deen saiya fara wata maganar daban mai matuqar rikita qwalwa..."
Nan yashiga bata labarin yadda sukayi da Ahmad ranar be 6oyemata komai ba har kawo shawarar dasuka yanke don 6illowa matsalar
Tunda yafara magana zee ta kafeshi da idanu tama kasa ko blinking Yayinda kwalwarta duk ta rikice itama
"kana nufin ba Deen bane muka gani ba a supermarket, kana nufin bayan Deen akwai wani mai sak kammaninshi?"
Ajiyar zuciya Aymaan ya sauke
"bazan iya concluding ba yanzu sainaji waye Deen don tabbatar da hasashena... Zainab waye Deen? Su waye iyayenshi?"
Girgiza kai zee tayi
"bayada iyaye" tafada ahankali
"kamar yaya?" inji Aymaan cikin rashin fahimta
Goge hawayenta tayi da bayan hannu sannan tace
"according to him wai duk sun rasu a hadarin mota, shi bema sansu ba don yana qarami a lokacin, kakarshi kawai ya bude ido yasani"
Shiru Aymaan yayi yana lissafa magangganunta a qwalwarshi
"to iyayen nashi wadanne tribe ne?"
"wai hausawa ne" inji zee
"ok, su kingin danginshi suna ina?"
"kamar yadda nafada maka besan kowa nashi ba sai wannan kakar tashi, besan kowa ba sai ita"
Cikin mammaki Aymaan yace
"but how come? Tayaya za'ayi yaqi sanin danginshi? Ina yan uwan mahaifiyarshi da mahaifinshi?"
"nima Hakan ya dade yana kulle min kai, koni nasha mammakin Hakan, kwata2 besan danginshi ba, daga shi sai kakar tashi ke rayuwarsu"
Shiru Aymaan yayi yana kallonta na wani lokaci sai kuma ya sauke Ajiyar zuciya yana sauke idanunshi
"then cikin dayan biyu ne"
Maida hankalinta zee tayi sosai kanshi don jin abinda zaice
"ko dai wannan kakar tashi na 6oyemashi wani abu gameda shi ne ko kuma shi ke 6oyemaki wani abu gameda shi"
Cikin rashin fahimta tace
"kamar yaya?"
Dan cizon lower lip dinshi yayi yana kallon table din gabanshi sai kuma ya saki lip din ya kalleta yace
"kodai kakarshi tana 6oyemashi wani abu na asalinshi ne ko kuma kawai yayi framing up story ne gareki"
Gaban zee yafadi
"kamar..ya?" tafada cikin rawar murya
"tayiwu they are all fake, tayiwu ba kakarshi bace shima ba Deen din bane, tayiwu kawai framing story sukayi don Shigowa rayuwarki ya wargaza ya tafi.
Cikin dayan biyu, ko dai dagaske bayan mussadiq al-hassan akwai Deen ko kuma mussadiq al-hassan shine Deen, yashigo rayuwarki ne da manufa yakuma fita bayan cikar burin shi"
Saurin dafe zuciyarta zee tayi dataji kamar zata buga saboda wani mugun bugu datayi
"No.. This can't be" tafada hankali a tashe
Ganin yadda hankalinta ya tashi yasashi realizing mistake dinshi na fadamata Hakan kai tsaye bayan ga halin datake aciki
"look zee, ni bance hakane ba, kawai hasashe ne kuma insha allah ba Haka bane"
"kenan he did that purposely? Me nayi mashi dana cancanci Hakan" tafada cikin fitan hayyaci
To fa, abu kadan ya girmama, duk inda hankalin Aymaan yakai Saida ya tashi ganin yadda zee ta burkuce lokaci guda, kuka kawai take cikin fitar hayyaci tana fadin metayi ma Deen dazai sakamata da Hakan.
Nan take kingin mutanen gidan da basusan abinda ke faruwa ba suka sani, Aymaan yayi mugun danasanin fadin wannan maganar don besan zatayi affecting dinta haka ba don shi kawai hasashe yayi
Koda su Abbu sukaji abinda ke faruwa sunyi mammaki sosai sunkuma dorawa Aymaan laifin tada mata hankali da furucinshi suna cewa be yakai shi fadin Hakan bayan yasan halin da dama take ciki
Shidai kasa cewa komai yayi sai tarin nadamar data sauko mashi, da kyar dai aka samu aka kwantar mata da hankali akan tabari suji ta bakin Ahmad kafin su yanke hukunci
Dakyar suka samu suka shawo kanta ta dan kwantar da hankalinta
Hakan yasa Aymaan takurawa Ahmad da har lokacin be gama tara bayyanan Mussadiq al-hassan ba, kasancewar shi babban mutum kuma mai murdadden hali na rashin bayyana kanshi ko sirrinshi yasa tattara bayananshi yayi wahala don shi mutum ne da idan ba saninshi kayi ba baka ta6a sanin shine mai amsa sunan don be yarda da baza sirrinshi ba irin yadda sannanu keyi shiyasa wani lokacin harya shiga wuri yafita baza'a ta6a sanin dashi ba, gashi he's not a social media fan, baya komai sai whatsapp shima ba sosai ba don yana iya wata beyi ba, gashi baya pics ya watsa, idan kaga pics dinshi to daukarshi akayi bada saninshi ba don bayaso kwata2
Dakyar dai Ahmad yasamu ya tattara bayanai akanshi ya kira Aymaan ya sanar dashi
Ranar da Ahmad zaizo gidansu Aymaan din da bayanan kowa Saida jininshi yazo kan akaifa musanmman Aymaan da oganniya zee
Ita zee fargabar ta shine kar ace hasashen Aymaan yazamo Gaskiya shikuma fargabar shi tashin hankalin zee
Sai bayan la'asar Ahmad ya diro gidan
Ganinshi yasa gaban mutane da dama acikinsu faduwa
A falo duk suka zauna aka gaisa sama kowa hankalinshi ba akwance ba
Murmushi Ahmad yayi ganin Hakan saiya bude briefcase dinshi daya zo dashi ya Fiddo wani file ya dagoshi
"to alhamdullilah, wannan file din yana qunshe ne da komai na Mussadiq al-hassan"
Tsit falon yasake dauka kowa na kallon file din
Hakan yasa ya bude shi yafara zazzaro takardun ciki ya barbaxasu a centre table din da aka maido gabansu
Ahmad yafara da
"sunan babanshi *AL-HASSAN* haifafen garin madina a qasar saudiya. Su biyar ne a family dinsu kamar yadda bayanin yazo yanada yayye biyu sai shi da twin dinshi *AL-HUSSAIN* Sai gambonsu wanda itace auta, duk ba'a kawo sunansu ba and I think it doesn't matter.
Sunan mahaifiyarshi *ZAINAB BINT ABUBAKAR* haifaffiyar qasar Misra (egypt).
Sunyi aure ne a shekarar 1***
Tareda AL-HUSSAIN shima da matarshi yar madina itama
Ga hotunan su nan... Wannan shine Al-hassan.. Ga dan uwanshi Hussaini" yafada yana nuna masu hotunan
"wannan kuma matar Al-hassan ce wato Zainab wannan kuma matar Al-hussain"
Nan ma bin Hotunan sukayi da kallo inda nan take zee ta hango tsantsar kammanin Deen da matar Al-hassan wato Zainab bint Abubakar.
"bayan shekaru biyar sa auren sai Zainab matar Al-hassan ta haihu, lokacin matar hussain haihuwarta biyu ma
A lokacin ne Zainab ta haifo yan biyunta kyawawa, gasunan"
Ya gwadamasu pics din jarirrai biyu cikin kayan sanyi dukda hoton yayi dishi dishi sosai
"Ranar suna aka radawa yaran suna *MUSADDIQ* da *MUJAHEED*"
"bayan haihuwarsu da shekara kusan hudu kuma sai aka haifi gambonsu mai suna *AYSHATUL HUMAIRA* a lokacin ma Al-hassan wato mahaifinsu Mussadiq be dade da rasuwa ba, itama ga hotonta nan datake yarinya dakuma yanzu data girma" yafada yana nunamusu hotuna biyu, daya na yar yarinya da batafi 3yrs ba na biyu kuma budurwa kamar dai sa'ar batool
"Al-hassan dama dan kasuwane kuma babu laifi yanada arziqi bakin gwargwado, bayan rasuwarshi ne al-hussain ya riqe masu mussadiq dukiyarsu har mussadiq ya girma yayi karatu yakai munzalin amsar dukiyarsu sannan ya amsa yafara kasuwanci kamar dai babanshi, cikin ikon allah sai gashi allah yasama abin albarka har suka baro madina suka dawo nan dubai ya cigaba da kasuwancinshi har allah yakai shi a matakin dayake aciki yanzu"
Tsit falon yayi bakajin qarar komai don tsab idan alura tafadi a wajen aji qararta kan kowannensu ya kulle gamm
"to kunji gajeran labarin Mussadiq Al-hassan" inji Ahmad yana kallonsu
Shiru dakin ya dauka sai can Aymaan yace
"to twin din mussadiq fa? Mujaheed kace ko me? Ina yake? Ya akayi daga baya baka sanyo Maganarshi ba a labarin?"
Duk Kada kai sukayi kingin mutanen dakin da alamun abinda ke ransu ya fada
"ya rasu!"
Qwalalo idanu dik sukayi suna kallonshi
"ya rasu???" Duk suka hada baki wajen fadin Hakan
Kada kai Ahmad yayi
"eh, shekararsu uku uku, Mujaheed al-hassan ya rasu babu jimawa mahaifinsu wato al-hassan yabishi lokacin Zainab bint Abubakar nada matashin cikin Ayshatul Humaira"
Kowa sai yakoma dumbfounded, kansu yaqara kullewa
"ta..yaya ya mutu" inji zee cikin rawar murya
Kallon zee Ahmad yayi yace
"wannan ne haryanzu bamu saniba, nayi nayi nasamu information ko kadan ne akai amma babu duk hanyar danabi a toshe take, kawai dai ansan Mujaheed ya rasu amma ba'asan sila ma"
Hankalin mutanen dakin yasake tashi
Cikin rawar murya batool tace
"k..kenan? D..Deen shine.. Mujaheed?"
Kowa kallon Ahmad yake zuciyoyinsu na bugawa da qarfi
Ahankali Ahmad ya kada kai
"Tabbas! *DEEN* shine *MUJAHEED*".... โ๏ธ
Ummin fasihu ๐ง๐ปโโ๏ธ?
8/2/21, 9:40 PM - Buhainat๐: *๐๐ปโโ๏ธDEEN ๐๐ปโโ๏ธ?*
*060*
*IN TROUBLE*
_jiya bansamu posting ba don bansamu typing ba saboda baqin da nayi, kamar yadda nayi tunani kuna nan kuna cigiya sai naga cigiyar ma tafi yadda nayi tunani, wasu suna Deeeeen ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ? wasu zeeeeeeee ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ wasu Aymaaaaan ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ amma anrasa mai cewa Ashaaaaanty ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐ฃ๏ธ๐, babu komai nasan matsayina a wajenku ๐_
Dukkansu mutuwar zaune sukayi jin abinda Ahmad yace
"yes, idan mukayi duba da tarihinsu inda Deen yatashi beda kowa besan kowa nashi ba sai wannan wanda yake kira kakarshi Hakan ya isa ya tabbatar da hasashenmu, tabbas Deen twin din mussadiq ne, shine wanda akace ya mutu lokacin da basu wuce shekaru uku uku ba, Saidai silar mutuwar da yadda akayi yaje Nigeria shine abu Mafi daure kai aciki, Tambayar anan itace wacece kaka? Meye alaqarta dashi? Tabbas ita kadai zatafi warware mana wannan qullin"
"innallilahi waina ilaihi rajiun" Zainab tafada ahankali tana dafa goshi.
She can't believe this, Deen.. Deen ashe ba Dan Nigeria bane? Deen ashe yanada uwa a duniya? Deen ashe yanada yan uwa? Deen twins ne?
Nan da nan hawaye suka shiga sintiri a kumatunta abinka da ruwa ruwa dama
_*banida kowa sai kaka, itama batada kowa sai ni. Nice duniyarta itace tawa*_
Wasu sabbin hawayen suka sake gangaromata tuna wannan maganar ta Deen datayi
Itama batool hawayen take, abin dai kamar al'mara kamar a shirin film, wani irin tausayin Deen taji ya kamata, she's just imagining kanta ace tarabu da Ummy tun batasan kanta ba takuma rayu a wani wuri tareda wacce basuda alaqa kwata2 daita, a rabata da ummy, Abbu, dan uwanta dama family dinsu gabadaya, akaita wata duniya daban inda batasan kowa ba sai mai riqonta.
This is touching, so touching.
Shima Aymaan jikinshi yayi laqwass yayi sanyi, shi kanshi tausayin Deen ke dawainiya dashi, tunaninshi a yanzu shine ina yake? Ina kaka tasake kaishi?
"Tabbas hakane, kaka kawai zata iya warware mana komai, amma ina take? Ina zamu nemeta a duniyar nan? Ni jikina na bani ita ta gudu dashi, wataqila gani tayi asirinta zai tonu wajen introduction din tunda basuda kowa kuma za'ayi bincike kuma taga Gaskiya na iya fitowa shiyasa ta gudu dashi" inji Abbu
"nima haka nake tunani Abbu, tabbas akwai abinda kaka ke 6oyewa, wataqila saceshi tayi ta gudu dashi Nigeria, yanzu kuma ganin asirinta zai tonu saita qara guduwa" inji ummy
"to amma abin daure kai anan ummy shine, meyasa akace mutuwa yayi? Meyasa ba'ace saceshi ba akayi? There's something fishy here" inji Aymaan
"yes, nima ina wannan tunanin Aymaan, meyasa aka rufe details din mutuwar? Ya za'ayi mutum ya mutu shekara da shekaru kuma a ganshi a wata qasar? Definitely akwai wani qullalen al'amari tattare da wannan abin" inji Ahmad
Shiru dakin ya sakeyi kowa yayi zurfi a tunani, kan kowa ya kulle tamau
Can dai Ahmad yace
"yanzu meye mafita?" yafada yana kallon dukkan mutanen dakin
Dakin ya dauka sannan Abbu yace
"kamar yadda kafada dazu dole mu nemo kaka, kaka ce kawai zata iya warware mana wannan chakwakiyar"
"to amma Abbu ina zamu fara nemanta? Babu mammaki ma yanzu ta chanza qasa, qila bata Nigeria kwata2" inji ummy
Duk Kada kai sukayi cikin gamsuwa da maganarta
"ni a ganina kawai muje mu samesu, mufada musu cewa mujaheed be mutu ba yana Nigeria tareda wata, wataqila Hakan zai taimaka, suna iya ma taimakawa wajen ganota" inji batool
Girgiza kai Ahmad yayi
"idan baka iya kama 6arawo ba barawo saiya kamaka, tayaya zamu tunkaresu haka kai tsaye batareda wata hujjaba qwaqwara? Na farko babu Deen din kuma bamusan inda yake ba, Nabiyu babu kaka itama we can't tell inda take, gashi dama bamusan silar barin Deen