Showing 300001 words to 303000 words out of 322641 words
Chapter 101 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
yana nan",inji saurayin
"to amma kai karasa aikin daya burgeka sai kanikanci kana fari tass dinka? ca6 wlh da nikeda farinka babu abinda zaisani kanikanci wlh saidai aikin office" inji Dogo
"kaji marar kishin kai yana kushemana sana'a to wlh kamar kayi a kunnen oga"
"yo ai gaskiya ne, kanikanci banda kwalliya da baqin mai me ake aciki, dubeni fa da haske na nazo garejin nan amma yanzu nazama dawanau"
dariya suka fashe daita
"a gidan ubanwa kaxo da haske? dama a dunan ka kazo sai uban qasusuwa banda ma rashin godiyar allah ai kaima kasan kamori kanikanci tunda gashinan kayi 6ul6ul dakau banda uban kai me kake dashi?"
"tubarkallah bismillah" inji mutumin da akema tsiya din
Deen be tsaya qarasa jin caftar su ba yawuce yana addu'ar allah yasa ogan ya daukeshi aikin don haka Kawai yaji aikin yashiga ranshi lokaci daya
da wannan tunanin ya qarasa wajen aikinshi inda yashiga yin aikinshi
yana fitowa daga sallar zuhr yawuce direct garejin yana addu'ar allah yasa ya tadda ogan
cikin sa'a kau ya taddashi inda yaga mutumin magidanci ne don zaikai irin shekara arba'in dawani Abu dinnan
saida suka gaisa sannan ya gabatar mashi da buqatarshi nason fara zuwa garejin
da farko kamar baxai yarda ba don acewarshi yara sunmashi yawa saikuma yace yaje yadawo gobe idan allah yakaisu zai duba
godiya Deen yayimashi sannan yatafi cikeda saran samun aikin
Washegari kau tunda wuri yaje don harwani doqin zuwa yakeyi inda anan ogan yace ya daukeshi aikin yakuma gayamashi sharuddan garejin tareda gabatar mashi da sauran yaran garejin su biyar Dogo, Sule, Habeeb, Nura da Yusuf
yakuma gayamashi a matsayinshi na junior dole yabi wadanda ya tadda koda ya girmeshi don yanzu shine junior dinsu kwata2 kuma akwai banbanci a sallama don anayine according to seniority
duk Deen ya amince da hakan sannan ogan yace yana iya tsayawa yau din kokuma yaje yabari sai gobe yafara zuwa
cewa Deen yayi zaifara yau din hakan yasa ogan ya hadashi da daya daga cikin yaran (Habeeb) akan yatafi dashi cikinsu
ranar Deen yaqara sanin yadda yan garejin suke don shaqiyai ne na gidan gaba
zolaya babu wanda besha ba wurinsu inda suka rad'amashi balarabe da qarfi da yaji don babu wanda ya tsaya bi takan sunanshi kawai sun rad'a mashi nasu wato balarabe
ranar saidai yazama dan aike, dauko wancan spanner miqo wancan haka sukaita aikenshi idan be ganeba suyimashi bayani, at the end of the day aka sallamesu inda nashi sallamar duk yafi na sauran qanqanta
be damuba ya amsa yai tahowarshi gida yanajin dadi don sosai yaji dadin yininshi daya a garejin don mutanen garejin badai ban dariya ba, suna aiki suna shaqiyancinsu hakan yasa koyaya kaje zauna wajen saisun saka nishadi
saida yakoma gida yagayama kaka sabon aikin dayasamu yakuma bata sallamarshi
kaka bataji dadi ba don sallamar batakai abinda yake samu a kasuwa ba gashi tana ganin aikin aikin qarfi ne zaifi na kasuwar wahala amma ganin yadda Deen yanuna yanason aikin yasa bata hanashi ba saima fatan alhairi datayi mashi
to daga wannan lokacin Deen yazama bakanike shima yazamana kullum yana gareji
Atashin farko Deen yayi popular a garejin, bayada surutu ko kadan saidai rashin kyashi dinshi yasa yaran garejin ke sonshi sosai don saidai kaji ana balarabe miqo kaza, balarabe yi kaza kuma nan take zaiyi yana haddace me akeyi
dayake yana son aikin sosai hakan yasa yake saurin dauke komai batareda anyimashi maimaici ba, ga tambaya don duk abinda yashige mashi baya jinkirtawa wajen tambaya
kaifin kwalwarshi da karsashinshi a aiki yasa cikin qanqanin lokaci yayi suna a garejin inda ogansu keji dashi sosai saboda tsantsar biyayyarshi da kaifin kwalwarshi
duk cikin yan garejin Deen yafi sabawa da Habeeb don jininsu yafi haduwa dukda Habeeb nada surutu sosai sa6anin Deen
shaquwarsu yasa Deen fara kwana shagon da Habeeb ke kwana kasancewar unguwarsu daya
kullum tare suke zuwa gareji sukoma tare lokacin kwanciya kuma su hade a shago, wannan yasa abotarsu taqara qarfi sosai
cikin yan watanni Deen yayi suna a garejin na ban mammaki, sosai customomi keson aikinshi don dayawa saisuka dawo idan sun kawo aiki basusan kowa ya ta6amasu mota sai Deen
gaskiyarshi da rashin ha'inci irin na wasu daga cikin yaran garejin yasa customomi sukafi sonshi ga uwa uba sanyinshi da biyayyarshi dake matuqar burge mutane sosai
hakan yasa nan da nan ya kwacema sauran customomi inda duk cikin yaran garejin yafi kowa customers dukda shine junior dinsu
gashi ogansu ya yarda dashi sosai yana kuma yawan dorashi akan abubbuwa da dama saboda yarda dayayi dashi kasancewar ogan ba a iya kanikanci Kawai ya tsaya ba harda kasuwanci irin nasu na yan gwangwani
daga baya ma saima ya miqa kusan ragamar kasuwancin hannun Deen don saiya zama kamar wani assistant dinshi don duk cikin yaran garejin babu mai makullin shagon kasuwancin ogan sai Deen
wannan cigaban daya samu sosai saiya tsonewa wasu daga yaran garejin ido musanmman wadanda ke ganin sundade sosai a garejin tayaya wannan daga zuwanshi a dinga fifitashi akansu a matsayinshi na junior dinsu
hakan yasa suka fara yimashi hassada suna ganin be cancanci matsayin dayake akai ba
tun suna iya 6oye hassadar dasuke mashi harsuka kasa don dagabaya qarara suka fito suna nunamashi qiyayya, Habeeb ne Kawai mai kaunarshi tsakani da allah
dayake hassada ga mai rabo taki take zama hakan yasa kodayaushe Deen cigaba Kawai yake samu takoina wanda hakan yasa yan garejin hada kai don qullamashi sharrin daxai dusashe tauraruwarshi
ranar ranace da Deen bazai ta6a mantawa ba inda aka nemi wasu kayan engine akarasa a shagon wanda kudinsu ba dan kadan bane
abin ya tadawa kowa na garejin hankali musanmman Deen don bayan ogansu shikadai keda key din shagon hakan yasa kullum shine qarshen tafiya gida
tun ana daukar 6atan kayan wasa har akaga dagaske sun 6ata din inda babu wata wata aka dora ayar tambaya akan Deen
dayake ogan irin mutanen nan ne dabasu yarda da qaddara ba ko asara nan take ya manta da tsantsar amanar Deen da gaskiyarshi yahau tuhumarshi acewarshi dole yasan wani abu gameda 6atan kayan
nanfa hayaniya ta tashi ogan ya murje ido akan sai Deen yabiyashi kayanshi
sosai hankalin Deen yatashi don tunda yake ba'a ta6a yimashi qazafi irin haka ba, duk yadda yaso wanke kanshi qin yarda dashi ogan yayi inda sauran yan garejin keta qara zugashi akan karya yarda
mutane biyu Kawai suka goyi bayan Deen da Habeeb dawani maqocinsu a garejin mai saida tayoyi
ganin hakan yasa Deen cewa zai biya amma allah yasani bashi yadauka ba, be ta6a sata ba kuma insha allah bazai ta6a yiba
haka yadawo gida zuciya a quntacce yaba kaka labari inda itama ta tayashi jimami sosai tana tayashi jin zafin qazafin da akayimashi
haka Deen ya tattaro yan kudaddenshi dayake tarawa kaka tacikamashi yabiya ogan daga ranar kuma ya daina zuwa garejin
sosai rayuwa tasake juyema Deen inda yasake komawa halin qunci na da
dama wannan aikin dayakeyi ke dan debemashi kewa hakan yasa yanzu yaqara komawa gidan jiya na halin damuwa
komawa yayi tsohon shagonsu na kasuwa ya cigaba da aikin dako badon yanason aikin ba saidon baison zama hakanan
sosai yayi missing gareji da kanikanci don yanason aikin sosai saboda aikin ma kanshi nasashi nishadi na musanmman
har lokacin alaqarsu da Habeeb nanan don dafarko shima Habeeb yaso barin garejin Deen ya hanashi hakan yasa anytime he's free yake leqo Deen acikin kasuwa
haka rayuwa ta cigaba da kasancewa har watarana Deen a hanyarshi tadawowa daga kasuwa lokacin har magrib takusa yagamu dawani mutum yana fama da motarshi
harya wuce saikuma yadawo ya qarasa wajen mutumin yana mishi sallama
amsawa mutumin yayi yana dagowa yana kalleshi hakan yasa Deen cewa
"motar taqi tashi ne?"
kamar wanda dama ke akan qaya yace
"eh wlh dan saurayi, kaganta nan narasa meke damunta gashi sauri nake zani wani wuri gashi duk garejijika sun kulle na rasa yadda zanyi" yafada da alamun damuwa a fuskarshi
"bari mugani..." inji Deen yana sunkuyawa gaban motar yana dubawa
haka kawai yaji kwadayin kanikancin na tasomashi, rabonshi da ta6a mota da niyyar gyara tun lokacin dayabar garejinsu
mutumin dai tsayawa yayi yana kallon Deen don kwata2 bemashi kamada bakanike ba, hakan yasashi tsayawa kallon ikon allah
saida Deen yadan dauki lokaci a sunkuye sannan yacema mutumin yashiga motar ya tada yaji
hakan kau mutumin yayi yashiga yatada Deen ya sake sunkuyawa yana gyaran
cikin qanqanin lokaci motar ta tashi
sosai farinciki ya lullu6e mutumin wanda hakan yakasa 6oyuwa a fuskarshi hakan yasa yafito yanata mashi godiya yana tambayar dama shi bakanike ne?
murmushi kawai Deen yayi bece komai ba
kudi mutumin yabashi amma firr Deen yaqi amsa, dik yadda mutumin yaso ya amsa qiyawa Deen yayi hakan yasashi haqura
nan mutumin ya tambayeshi inane garejinsu, kamar Deen zaice bayada gareji saikuma yayi mashi kwatancen tsohuwar garejinsu kawai
godiya mutumin yasake mashi suka rabu
Bayan kwana biyu mutumin yaje garejin da Deen yaimashi kwatance don sosai Deen ya kwanta mashi yakuma shiga ranshi farat daya gakuma tunda yake bada gyaran mota ba'a ta6a yimashi gyaran dayaji dadinshi ba irin wannan
saidai koda yaje bega Deen ba yakuma tambaya inda yana musu kwatancenshi suka gane Deen ne
abinne yasosama yaran garejin rai don tun barin Deen garejin ba ranar banza da baza'a zo nemanshi ba, wasu ma har barin kawo aiki sukayi garejin
hakan yasasu cewa su basu sanshi ba qila ba daidai yaimashi kwatancen ba
daidai nan Habeeb yazo wurin jin abinda ake tattaunawa yasashi yin caraff yace kodai balarabe yake nema
dasauri mutumin ya kadamashi kai yace eh yana kama da balarabe
caraff daya daga cikin yaran garejin yace inda balarabe ne toya andade da korarshi daga garejin saboda sace sacen dayakeyi
ran Habeeb ya6aci da kalamanshi nan yashiga maidamashi cewa saidai insune 6arayin amma Deen ba 6arawo bane kuma zakaran da allah yanufa dacara ko ana muzuru ana shawo saiyayi sannan yajuyo kan mutumin yace aiki ya kawo ko balaraben yake nema?
mutumin daketa kallonsu tundazu yace balaraben yake nema hakan yasa Habeeb yace yataho yakaishi wajenshi
sosai hakan ya 6ata ran yaran garejin don ba haka sukaso ba, dukda sun raba Deen da garejin sunkasa rabashi da masoyanshi don hatta ogansu shima yanzu danasanin abinda yafaru yakeyi don barin Deen garejin nashi ba qaramin cibaya yajamashi ba
Cikin motar mutumin suka tafi neman Deen inda akan hanya Habeeb ke labartama mutumin duk abinda yafaru da barin Deen din garejin hakan yasa Alhajin tausayawa Deen yakuma ji yaqara shiga ranshi fiyeda da
koda suka isa shagon basu iske Deen ba don acewar co-workers dinsu be dade da tafiya gidaba don wani lokacin yana komawa gida cin abincin rana
Alhajin be gajiba yace suje gidan nasu shidai yanason ganinshi
babu musu Habeeb yakaishi har gidan nasu inda anan suka hade da Deen da fitowarshi kenan da niyyar komawa kasuwar
sosai Alhajin yaji dadin ganin Deen nan suka gaisa cikeda mutuntawa inda saida Alhajin ya tunama Deen inda suka fara haduwa don shi harya manta
nan Alhajin ya buqaci zai dinga kiranshi duk lokacin dayakeda gyara yazo yayimashi
babu musu Deen ya amince mutumin yabashi card dinshi mai dauke da address dinshi da number waya shima Deen yabashi number wayarshi
haka kau akayi don duk lokacin da Alhaji Shamsu kamar yadda sunanshi yake ya buqaci gyaran mota zai latso Deen yazo yayimashi wani lokacin har hanya yakemashi yayima wasu don sosai yakeson aikin Deen saboda qwarewarshi
shima Deen sosai yakejin dadin aikin Alhajin don mutumin akwai sanin darajar mutane, dukda shi mai kudine amma hakan besa ya qyamaceshi ba, yana nunamashi qauna sosai
ahaka ne suka hadu da diyar Alhajin mai suna Lailah agidan Alhajin wanda tun a farkon haduwarsu ta afka soyayyarshi kuma haryanzu tana sonshi batareda yama san tanayi ba don shi banda gaisuwar mutunci babu abinda ke hadasu daita
Alhaji Shamsu yanada mata daya sai 'ya'ya shidda duk mata, hudu daga cikinsu duk sunyi aure sai Lailah dake karatunta haryanzu sai yar qanwarta kuma autarsu Afrah
Alhaji bayada d'a namiji kodaya kuma tunda yake beta6a jin qaunar mutum kamar yadda yakejin yadda yakeji gameda Deen ba hakan yasa ya daukeshi kamar danshi yana nunamashi qauna ta tsakani da allah
ana haka watarana yabashi aiki inda yayimashi text din address din inda zaije yasamu motar don lallacewa tayi ahanya yabarta yahau wata yadawo
sashi yayi yafara aikin gashinan zuwa
haka kau akayi inda Deen yaje wajen yafara aikin motar
can yana tsaka da aikin tunanin zee yafadomashi kamar yads tunaninta ke yawan kawomashi ziyara akodayaushe
dukda yasan yanzu zee tayimashi nisa hakan besa yadaina tunaninta ba
akodayaushe cikin tunaninta da begenta yakeyi
fuskarta tayimashi gizo a idanunshi smiling like an angel hakan yasashi shima sakin guntun murmushi ahankali
_old good memories of you.._
_never want to fade in my brain_
_you're stick to my brain like a magnetic glue_
_never wanting to shift for a bit_
_an angel.._
_the angel... that I never saw someone like her that exist_
_an angel..._
_the angel that will always never exist_
cikin cool voice dinshi yacigaba da waqar wanda anan take yake composing dinta
dama yanzu haka yake, haka kawai yana zaune shikadai saiya fara waqa wanda mostly tana zuwa ne duk lokacin dayayi nisa cikin tunanin zee dinshi
shikanshi besanin sadda yake farawa saidai yaji kawai yanayi kuma waqar nazuwa ne from the bottom of his heart don abinda yakejine yake furtawa directly a sigar waqar
haka yaitayi yana aikinshi yana waqarshi, dayayi wannan yayi wannan, wasu da hausa wasu da turanci
nan da nan yagama aikin ko harda waqar datayi making dinshi busy yasa yaga saurin aikin oho?
yana gamawa ya maida gaban motar yarufe yadago yana share gumi
tozali da Alhaji dayayi agabanshi yasashi dakatar da abinda yakeyi yana dan wara idanu
"Alhaji yaushe kazo?" yafada da mammaki
"tun lokacin daka fara waqarka" yabashi amsa
kunyace takama Deen hakan yasashi sunkuyar dakai yana sosa gefen wuya
"ashe ka iya waqa? gaskiya tunda nake banta6a jin muryar datayi captivating dina irin wannan ba"
kunya Deen yaqaraji hakan yasashi cewa
"to ko ka gwada motar kotayi?"
murmushi Alhajin yayi yashiga motar yatada yajita tayi daidai hakan yasashi fitowa yana cewa tayi sosai
murmushi Kawai Deen yayi
Alhaji yasake cewa
"kanada ra'ayin yin waqa? yadda naji muryarka dinnan awaqa nasan baqaramin mawaqi za'ayi anan ba"
sunkuyar dakai Deen yaqara yi cikin jin kunya don dayasan Alhaji na wajen babu ma abinda zaisashi yi don yanajin kunyarshi sosai
"kayi shiru?"
"Alhaji bafa wani iyawa nayi ba"
"wani ba iyawa kayi ba? wai kajika kuwa? gaskiya zan kwadaitamaka jaraba waqar muji don gaskiya inaji ajikina voice dinka zai mayar dakai wani, idan kanada ra'ayi kayimin magana zan tsayamaka insha allah, ai waqa ma babbar sana'a ce kuma baiwace babba, kayi tunani Akai"
da to kawai Deen ya amsa badan yadauki maganar serious ba
cemashi yayi yakai motar gida shi yanzu wani wurin zashi sannan yashige motar yawuce
tun Deen na daukar maganar Alhaji wasa harya ga dagaske fa yakeyi don kodayaushe cikin yimashi maganar Alhajin yake
tun yana zillewa beso haryaji shima sha'awar gwadawa din inda a gwajin farko ya burge mutane dayawa
ahankali ahankali da taimakon Alhaji dakuma qarfafa gwiwarshi Deen yacigaba da waqar inda ahankali waqoqinshi suka fara samun kar6uwa acikin al'umma
kan kace me? cikin ikon allah cikin qanqanin lokaci Deen yayi fice yakuma yi suna acikin mawaqan zamani
sosai Alhaji yayi farinciki da hakan yakuma ginamashi studio inda zai dinga gudanar da harkar waqarshi
sosai waqar ta kar6eshi don cikin qanqanin lokaci yayi suna yana kuma samu sosai acikinta wanda hakan yajawo chanjin rayuwa agaresu har suka mallaki gidan kansu
ahaka ya nemi Habeeb abokinshi qwallin qwal yamaidoshi wajenshi yazama manager dinshi inda suke gudanar da harkar waqar tare
ahankali Deen ya chanza daga poor timid guy zuwa rich handsome guy wanda harda kyawunshi ke qara mashi farinjinin jama'a yakuma zama abinda yazama yanzu....✍?
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/5/21, 8:17 AM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*095*
"duk abinda nazama na zama hakan ne ta dalilinki Zainab, am sorry for going away just like that, nayi danasanin tafiya nabarki, nayi danasanin rashin tsayawa kai da kafa wa soyayyarmu, natafi nabarki batareda tunanin ya zakiji bayan kingane na gujeki, I should have stay.. I should have tell you komai alokacin qila mu iya shawo kan matsalar atare, saigashi sanadin stupidity dina nayi wata irin rayuwa marar armashi kwata2, I guess that's what I deserve... and the amazing thing is yadda kikayi connecting dina da wadanda kwata2 banma san dasuba duk tsawon rayuwata... namaki sharri kinsakamin da alhairi, be kamata na iya hada idanu dake ba, bansan ta ina zanfara ba, bansan da wadanne kalamai zanyi amfani dasu ba wajen godemiki, all I know is samin masu golden heart irinki a duniyar nan zaiyi matuqar wuya"
lumshe idanunta dasuka gaji da zubda hawaye zee tayi tasake budesu ahankali jikinta duk yayi sanyi dajin labarin Deen, he went through alot hakan yasa taji wani irin tausayinshi ya lullu6eta, mutum da gatanshi da family dinshi amma yasha wahalar duniya
bata tunanin tunda mussadiq yake yasan wani abu wai aikin qarfi, kallo daya zakamashi kasan cewa shi real ajebo ne, besan komai ba sai hutu, yana nan cikin hutu da jindadi while twin dinshi nacan yanashan wahalar duniya, such is life
"Zainab please forgive me, let's forget our past and start afresh.. ina sonki Zainab son da bazan iya misaltawa ba, ada naji kamar na hqra dake jin cewa ke matar wanice amma yanzu bazan iya ba... ki hukuntani takowace hanya amma banda ta hanyar juyamin baya..idan kikayi hakan zan zauce... zan mutu ...please" yaqarashe ahankali yana kallonta in the eye da oily eyes dinshi dake jiqe sanadin hawayen dayayi
itama shi take kallo takasa janye idanu akanshi ganin yadda yawani marairaice mata
komai nada ne yashiga flowing back a qwalwarta, tunawa tayi da farkon haduwarsu, tunawa tayi da yadda dafarko basa shiri takuma tuna yadda akayi suka shirya
sosai memories din ke flooding qwalwarta inda take tuno rayuwar dasukayi a school inda suka zama kamar wasu besties, tunawa tayi da incident dinsu master da yadda yakusan rasa rayuwarshi akanta, tunawa tayi da soyayyarsu, yadda yake treating dinta like a queen, beson 6acin ranta ko kadan, yadda yake nunamata tsantsar so da qauna...
"Zainab please give me another chance...kisake bani dama na nunamiki yadda nakesonki a zuciyata, kisake bani dama na nunamiki haryanzu wutar qaunarki na ruruwa a zuciyata, bata ta6a mutuwa ba kuma baxata ta6a mutuwa ba har abada... please kisake bani wata damar" yafada softly but romanticly
"Zainab!.."
atare suka dago daga Deen har Zainab din suka kalli saitin inda aka aka kirata
Aymaan ne suka gani daga dan nesa dasu yana kallonshi shima fuskarshi expressionless
"Akhie?" zee tafada ahankali tana tashi tsaye don daman har lokacin a kneeling position suke
sai a lokacin tama lura da yadda marece yayi sosai, mammaki yakamata don ita harta manta dama cikin school suke
ahankali Aymaan yafara takowa yana kusantosu hakan yasa shima Deen miqewa yana kallonshi batareda wani yanayi yanuna