Showing 132001 words to 135000 words out of 322641 words
Chapter 45 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
na biyun qarshe
Jitayi qaffafuwanta bazasu iya daukarta ba Hakan yasata xamowa itama tayi kneeling ta rufe fuskarta da taffukan hannunta tana shesheka ahankali
Shima kallonta yakeyi yanajin zuciyarshi na raunana, yanajin kamar ya rungumota a qirjinshi ko zaiji sauqin abinda zuciyarshi ke mashi
Haka kawai su biyu kejin kamar wannan shine happy moment dinsu na qarshe, dalilin da yasa zuciyoyinsu ke basu Hakan ne basu saniba
"I love you" yayi maganar kusan cikin rada
Dago fuskarta tayi daga tafukan hannunta ta kalleshi da bloodshot idanunta
"please don't leave me, no matter what" itama tafada cikin karyewar zuciya
"never, I will never" yafada yana jin kamar shima yayi hawayen, idanunshi shima sun Kada
Share hawayen fuskarta tayi sannan ta jawo jakkarta ta bude taciro wani box itama jaa Saidai yafi na Deen girma
Dagowa tayi ta kalleshi taga shima ita yake kallo
Murmushi tayi mashi daidai saukar wani hawayen saikuma tayi saurin sharewa da bayan hannu sannan ta bude box din carefully
Dagowa tayi taga shima kallon abinda ke cikin box din yake sannan ya dago ya kalleta
Bands ne guda biyu aciki jere jajjaye, daga tsakiyar band din akwai wani heart shaped bud
Ahankali ta cirosu tana nuna mashi murmushi a fuskarta
Kallonsu yayi sannan ya kalleta shima murmushi na forming a fuskarshi
Ajiye daya tayi ta riqe daya ta lalubi wani botton ajikin bud din band din nan take tsakiyar band din take kamar fuskar agogon hannu yashiga bada wuta yana bada rubutun
_*Deezeen*_
Idan kuma ya dauke yasake dawowa sai yabada
_*together forever*_
"wow!" Deen yayi exclaiming yana kallon band din cikin sha'awa
Nuni tayi mashi ya miqo hannunshi
Miqawa yayi yana murmushi
Ahankali ta daura mashi a wrist dinshi saigashi yayi mashi d'ass a hannu gwanin kyau
Shima duqawa yayi ya dauko dayan dayan ta miqamashi hannunta itama ya daura mata ahankali
Murmushi sukayi ma juna sannan suka jera hannayen nasu mai band din kusada juna suka danna dan qaramin botton din nan take haske yakawo da rubutun
_*DEEZEEN 💞*_
Da
_*TOGETHER FOREVERâ¤ï¸*_
.... âœï¸
UMMIN FASIHU 🧚ðŸ»â€â™€ï¸?
8/2/21, 9:38 PM - BuhainatðŸ˜: *ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸DEEN ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸?*
*044*
*ASAAD*
Kwance take kan gado ruff da ciki kaffafunta asama tana dan wasa dasu
Ring din yatsarta ta qurama ido wanda yawancin lokuta irin haka idan tana zaune bata komai saita tisa zoben agaba tana kallo tana jin wani shauqi na musanmman na tasomata
Kwantar da kanta tayi akan filo tayi lamo tareda qure waje guda da ido ita kadai tasan abinda ke kai kawo a kwakwalwarta
Knocking da akayi a kofa ya dawo daita daga guntun tunaninta.
Kallon kofar tayi sannan ta miqe zaune
"yes?"
Turo kofar akayi aka shigo sai taga ashe mummy ce
Sauko da kaffafunta tayi qasa tana cewa
"mummy?"
"ki shirya kinyi baqo yana falon baqi" inji mummy
Dan daga girarenta zee tayi tace
"baqo kuma?"
"eh, Kiyi maza karki 6atawa mutane lokaci " inji mummy tana Juyawa zata tafi
Binta da kallo zee tayi harta fita tana wondering wane irin baqo kuma da daren nan
Duba agogon bangon dakin tayi taga 8:30pm sai kuma ta tashi don yin yadda mummy tace
After dress baqa kawai ta dora kan kayan jikinta ta yafa gyale sannan tadan gyara fuskarta tayi spraying turare a jikinta sannan ta dauki wayarta ta fita
A qasa ta tarar da mummy
"yauwa dauki wadannan kitafi dasu" inji mummy tana nuna wani tray dake kan centre table din falon
Tsayawa zee tayi tana kallon tray din dake dauke da kayan motsa baki cikin mammaki
"ko bakiji ba" inji mummy tana hade rai
Wucewa zee tayi wajen tray din not saying anything ta dauki tray din ta nufi hanyar fita
"behave yourself ok? Karki saki ki 6atamin rai" taji mummy na fadin Hakan a bayanta
"to" kawai tace ta ida ficewa tana jin wani haushi a zuciyarta
Ko ba'a fadamata ba tasan wani ne yazo wurinta don dama ansaba hakan donma sundan ja baya yan kwanakinnan saboda bata kulasu ko sunzo din, da kenan da batada Deen bare yanzu.
Ta6e baki tayi ta qarasa guest room din tayi knocking ahankali sannan ta tura kofar tana sallama
Ahankali taji an amsa cikin masculine voice
Qarasa Shigowa falon tayi batareda ta kalli gefen da mutumin ke zaune ba ta qarasa centre table din dakin ta ajiye tray din sannan ta nemi kujera dan nesa dashi ta zauna
Sai a sannan ta dago tadan kalleshi sama sama ta kauda kai
"Sannu" tafada ahankali tana gyara zamanta
Sai a lokacin shima gayen ya Janye idanunshi daga kan wayar hannunshi ya kalleta itama sama2 ya kauda kai yana cewa
"sannu"
Wani abu taji ya tsayamata a maqoshi amma saita hadiye ta koma itama ta jingina da kujerarta tafara latse latse a wayarta
Shiru dakin yasake dauka banda qarar a.c babu abinda ke tashi dakin
Sun kusan minti 20 ahakan wayar zee tafara ringing cikin low tone
Ko bata duba ba tasan ko wanene don dama shi kadai keda wannan ringing tone din
Dan murmushi tayi Saida takusan katsewa sannan ta daga ta kara akunne
"Ranki ya dade" taji cool voice din Deen na fadin Hakan tacikin wayar
Murmushi tayi sannan tace
"tareda naka"
Shima murmushin taji yayi yace
"barka da daren juma'a"
"barkanmu dai, where is my kaka?"
"Your kaka tana dakinta Dakyar nasamu na faki idonta nafito"
Dan wara manyan idanunta tayi
"kafito? Katafi ina?"
"ina kofar gidanmu, inason jin muryarki ne kuma dataga na shiga daki zata biyoni taga ko menene so I decided gwara na gudo waje"
Dariya zee tayi ahankali tace
"kai ko? Allah yasa ta leqo ta ganka wajen to"
"babu ko wuya Indai kaka ce, ni wlh nagaji yakamata ta dinga kyaleni Hakan tunda na girma amma kullum cikin samin ido take kamar qaramin yaro" ya qarashe a dayan bangaren yana kumbura fuska
Dariya tasakeyi ahankali sannan tace
"wulaqanci? Yanzu kaka kake cewa tana samaka ido?"
"to, ai Gaskiya ne, am very sure da cikin gida nake da yanzu tabiyo sahu tana _kyakyawana? Lfy ka qunqume daki?_" yafada yana kwaikwayon maganar kaka
Rufe bakinta zee tayi tana Dariya ahankali sannan tace
"ka qaddara kayi a gabanta, takanas zanzo gidan na fadamata"
Shima dariyar yayi yace
"dakau kin ja ta zaneni radam"
Wara idanu tayi
"dagaske? Tana iya dukanka?"
"sosai ma, ai haryanzu kallon dan 5yrs takemin, tsaf zata zaneni nikuma naita kuka ðŸ˜" ya qarashe maganar da muryar kuka
Murmushi mai sauti tayi tace
"nikuma naita Dariya ba? ina maka waqar mai kukan banza"
Kumbura fuska yayi
"hakama zakice?"
"eh mana, bayan haka ba har videoing dinka zanyi na dora a social media with caption *crying kaka's boy*"
Sake hada gira yayi
"ashe dai bakya sona"
"Sai yanzu ka sani?"
"sadly yes"
Murmushi tayi
"am glad yanzu kasani"
"hmm marar M... Wai kinsan wani abu?"
"A'a saika fada"
"dazu nayi composing wata waqa, bakijita ba, very muah!" Yafada cikin doqi
Dariya marar sauti tayi
"har kasan tayi dadi?"
"bani nayita ba?"
"don kai kayita ai bakai zaka yabeta ba sai kabari wadanda suka jita su yabeta"
"to ai shiyasa zanyimiki kijita"
"to shikenan, ina saurare"
Gyaran murya taji yashiga yi Hakan yasata fara Dariya marar sauti, kamar kau yasani sai yace
"to ai ina iya farawa kuma kiyita yimin Dariya"
Dariyarta ce tafito fili
"hmm there you go" inji Deen yana hada rai
"ni Dariya nayi, bafa Dariya nayi ba"
"ba Dariya ba kikayi? Ni kurma ne?"
"to sorry, inaji"
Jitayi yaqara gyaran murya ita kuma taqara kasa kunne murmushi a fuskarta
"to ai kuma kina iya cewa baitin is so long"
"ni yaushe nacema zance Hakan?"
"na sani ne ai, kina iya kushemin abuna duk yadda nakeji daita kau"
Dariya tasakeyi sai taga kamar inuwa inuwa a gabanta Hakan yasata dago idanu sai taga mutumin ne ya miqe tsaye
Dan wara idanu tayi don ita harga allah ma ta manta da akwai wani a dakin
Ganin zaiyi magana yasata saurin cewa Deen
"excuse me Deen, I'll call you later" tafada tana katse kiran batareda ta tsaya jin Amsarshi ba
Saurayin dake kan wuya akan wulaqancin datayi mashi yace
"zan tafi, thanks"
"thanks too, agaida gida"
Kada kai yayi kawai yana cizon lower lip dinshi sannan yafita a fusace leaving the door open
Binshi da kallo tayi harya fita sannan ta sauke Ajiyar zuciya tana rolling idanunta sannan itama ta tashi ta nufi tray data ajiye wanda ko ta6ashi ba'ayi ba ta dauke tana ta6e baki tafito ta maido kofar ta rufe.
Luckily bata tarda mummy falon ba hakan yasa tawuce da tray din kitchen taba daya daga cikin maids din ciki tafito
Tana fitowa taci karo da mummy dake sakkowa daga stairs Hakan yasa gabanta yadan fadi
"harya tafi?" inji mummy tana kafeta da idanu
"eh, yatafi yanzu yanzunnan" inji zee tana rarraba idanu kamar marar gaskiya
Mummy bata sake cewa komai ba tazo ta wuce ta tashige kitchen Hakan yasa zee sauke Ajiyar zuciya sannan itama ta nufi sama
Saida tagama shirin barcinta sannan ta haye gado bayan ta qure a.c din dakin
Wayarta ta dauka ta lalubo number Deen takira kamar yadda tace mashi
Kamar kau jira yake a ringing na biyu ya dauka yana sallama
Lumshe idanu tayi ahankali ta bude sannan ta gyara kwanciyarta tana amsa sallamar
â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸
Dagowa daddy yayi yana kallon zee data zauna yanzu murmushi a fuskarta.
"daughter ta" yafada shima yana mata murmushi
"na'am daddy na" tafada cikin shagwa6a
"ya weekend?"
"alhamdullilah daddy na" tafada tana murmushi
"kinsan abinda yasa nayi kiranki?"
"A'a daddy"
Gyara zama daddy yayi Yayinda mummy haryanzu bata dago ta qara kallonta ba Tun amsa gaisuwarta datayi, ita gani ma tayi kamar fushi take
"jiya wani yazo wurinki ko?"
Jimm zee tadanyi fara'ar fuskarta na dan tafiya
"eh daddy" tafada ahankali
"masha allah, ya fadamaki ko wanene?" inji daddy again
Shiru tadanyi sai kuma ta girgiza kai ahankali
"To sunanshi ASAAD, d'a ga babban aminina kuma abokin kasuwancina Alhaji Abubakar"
Dagowa tayi ahankali ta kalli daddy, ita sai yanzu ma ta tuna Da maganar data ta6a ji daddy nayi da mummy akan d'an Alhaji Abubakar din
No wonder, dama tasansu tasan halinsu na jin kai, shiyasa ma jiya qila yafara daddaga mata kai besan idan dagin kai ne gidanshi ne yazo.
"yau da safe ya kirani yana gayamin abinda yafaru a tsakaninku, banji dadi ba Amma kuma laifina ne da ban sanar dake zuwanshi ba dakuma gayamaki ko shi waye, I think duk Hakan yajawo matsalar tun farko.
Shiyasa nace bari na kiraki nayimiki bayanin komai dalla dalla yadda zaki fahimta"
Shiru dakin ya dauka babu mai cewa komai Hakan yasa daddy cigaba da cewa
"kamar yadda na fadamaki sunanshi Asad, First born din Alhaji Abubakar.
Yaro ne haziqi don Yanzu haka yagama masters dinshi ne a qasar india ko sati biyu beyi da dawowa ba kuma insha allah next week zai fara aiki a daya daga cikin manyan companies din babbanshi a matsayin mai jagorantar kamfanin
Asad yana da komai da kikeso bama ke kadai komai da kowacce mace zata so shiyasa nama fara tunkararki da wannan maganar
Bayan haka kuma faruwar Hakan zai qara qulluwar zumincinmu dake tsakanina da Alhaji Abubakar kuma zamu qara girma da qima a idanun juna
Nasan jiya rashin sani ne yasa kika qi kulashi Hakan ma nagayama Alhaji Abubakar din amma zai qara dawowa yau sai ku fuskanci juna dakyau"
Shiru dakin yasake dauka zee bata dagoba kuma ba tace komai ba
"baki ce komai ba dear"
Sai a sannan ta dago ta kalleshi sannan tace
"Dad... I think basai yasake dawowa ba"
Shiru daddy yayi yana kallonta sai kuma yace
"basai yasake dawowa ba kamar yaya?"
"saboda ko yasake dawowa din bazamu fuskanci juna ba"
Shiru dakin yasake dauka, haryanzu mummy batayi magana ba Saidai wani kallo datake jifan zee dashi, zee na ankare da kallon amma taqi kallon gefen mummyn don karma tarasa qwarin gwiwarta
"meyasa?" inji daddy yana kallonta yanayin rashin jindadi na bayyana a fuskarshi
"saboda bana sonshi Dad..."
"ke!! Wato haryanzu bakida hankali ban saniba? Ina maki kallon wacce tafara hankali ashe haryanzu da saura?!" inji mummy a matuqar fusace
Sauke idanunta zee tayi tana dan qara shigewa kusada daddy
"ya isa maimuna" inji daddy Ahankali
"ya isa din me? Yarinya shikenan bazata ta6a hankali ba, don gidanku ke kika haifemu ko mu muka haifeki dazaki maidamu shashashai? Duk wanda yazo da abinda zakice? Dama ina ganin dawowarki jiya nasan ba lau ba ke kenan Duk wanda yazo beyi miki ba? Me kika dauki kanki? Ko atunaninki cigaba zakiyi da zama damu har abada!"
Daddy ne yaqara katseta da
"haba Maimuna, ya isa Hakan mana, daga fadin ra'ayinta saiki hauta da fada?"
"haka ma zakace Alhaji? Yarinya shikenan sai abarta tayita abinda taga dama babu kwa6a? Dama kai ka lallatata ai, idan ba Haka ba tsabar wulaqanci duk wanda yazo sai tace bata sonshi, sotake mu tisata gaba muyita kallo kenan har ta tsofe a gida?
To bari kiji, diya mace qa'idattacen lokaci gareta, wlh tun kinada sauran damar ki ki rufama kanki asiri ki za6i miji tun kafin yazamo ke ke neman ayi za6i dake" inji mummy cikin mugun 6acin rai
Shima daddy da ranshi yafara 6aci yace
"haba Maimuna? Wannan meye to kike mata? Baki ne ko me dazakice zata zama ita za'ayi za6i daita? Wannan maganar kwata2 be dace ta fito daga bakinki ba a matsayinki na Uwa"
Kauda kai kawai mummy tayi tana huci itakau zee banda hawaye babu abinda takeyi
Juyowa daddy yayi Wurin zee daketa dauke hawayenta cikin sassauta murya yace
"daughter?"
Dagowa tayi ahankali ta kalleshi da watery eyes dinta
"bakya sonshi ko kika ce?"
Ahankali ta gyada kanta avoiding mummy's gaze
"to masha allah, Zainab ni mahaifinki ne kuma mai son farincikinki, bazan ta6a yimaki dole ba, na riga da na dauki alqawarin auramaki muradinki ba don komai ba sai don dorewar farincikinki wanda nima shine nawa
So karki wani damu, ni bazan yimiki bakin ki tsofe agida ba kuma bazan miki bakin kizama za6in wasu ba, insha allah saikin za6a kin darje da kanki kin kawoshi da kanki nikuma na cika miki burinki ta hanyar auramaki shi"
Farinciki ne ya mamaye zuciyar zee Yayinda mummy kuma ta kauda kai cikin tsananin takaici
"Thank you so much daddy... Kuma.. Dama ni yanzu akwai wanda.. Nakeso" tafada ahankali
Ba daddy kadai ba har mummy Saida ta waigo ta kalleta sai kuma suka kalli juna sannan suka maida kanta again
"menene?" inji daddy unbelievably
Murmushi kawai tayi ta Kada mashi kai tana sunne kai, karo na farko data fara jin kunyar daddy
Washe baki daddy yayi
"masha allah, to kingani ko? Kinga abinda nake fadamaki, baki bari yarinya tagama fadin abinda zata fadaba kinyi jumping to conclusion" daddy yafada yana kallon mummy data qara kauda kai
Cikin farinciki yajuyo gun Zainab dataji wani sanyi na ratsa zuciyarta yace
"wanene shi to? Gayamin everything about him"
Murmushi zee taqarayi a kunyace tana jin wani yaqini a zuciyarta
"Daddy kaima ka sanshi ai"
Dan wara idanu yayi
"dagaske? Tofa, to wayeshi din?"
"School mate dinane, Sunanshi DEEN"
Tsittt dakin yayi
Kallon kallo aka shigayi tsakanin mummy da daddy Saidai kowa da kalar kallonshi
Daddy kallon rashin fahimta mummy kuma kallon mammaki
"Kina nufin Kamaldeen?" inji mummy a mammakince
Bata dago ta kalleta ba ta kada kai alamun eh
Sake kallon juna mummy da daddy sukayi
"wai wanene Hakan?" inji daddy in confusion
Shiru mummy tayi tama kasa cewa komai
"daku fa nake"
"ta fadamaka mana, tunda itace mai maganar" inji mummyn tana kallon zee
Maida kallonshi yayi akan zee din dake kallonsu itama
"daughter na, kiyimin bayani, ni banganeba haryanzu"
Zee da jikinta yafara sanyi tadan tattaro kingin kuzarinta sannan tace
"Kamaldeen, wanda yayi rescue dina a wajensu Master, wanda ya kwanta hospital ta dalilin incident din"
Diff... Wutar daddy ta dauke na wucin gadi
"What?!" Yafada in shock... âœï¸
*please Manage ðŸ‘, yau Dakyar nasamu nayi wannan biki garemu kuma jiya ma ban samu zaman yiba, sanin cewa kuna nan kunata jira yasa nadanyi wannan don jiya ma ba'ayi ba
Ayi hqr, da babu gwara babu yawa
Natafi cin shinkafar biki
🚴ðŸ»â€â™‚ï¸ðŸš´ðŸ»â€â™‚ï¸ðŸš´ðŸ»â€â™‚ï¸ðŸš´ðŸ»â€â™‚ï¸?
Ummin fasihu 🧚ðŸ»â€â™€ï¸?
8/2/21, 9:38 PM - BuhainatðŸ˜: *ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸DEEN ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸?*
*045*
*THE CHALLENGE*
Dagowa zee tayi tana kallon daddy jin yadda yayi magana sai gani tayi shock ne written all over his face, sai taji jikinta yayi sanyi
"I.. Don't get you" inji daddy yana kallonta cikin son gasgata abinda kunnuwanshi suka jiye mashi
Shiru tayi takasa cewa komai
"wa kike nufi, I don’t get you" daddy yasake fada
Hadiye wani abu daya tattaru a maqoshinta tayi sannan tace
"wannan Deen din wanda keda pneumonia wanda aka kwantar dashi asibiti dalilin attempt dinsu master akaina"
Ganin yayi shiru yana kallonta yasata yin tunanin ko haryanzu be gane bane Hakan yasata qara cewa
"yace kunma Hade a wajen daurin auren Aunty Feenah Har kuka gaisa ma, wannan mai grandmom din?"
"daughter are you ok?" inji daddy yana Binta da kallon mammaki
Itama kallon rashin fahimta tashiga yimashi
"ki rasa wanda zakice kina so sai wannan yaron?" inji daddy still cikin mammaki
Gaban zee yashiga harbawa ahankali ta cigaba da kallon daddy batareda tasan na cewa ba
"wai maimuna bakiji abinda muke cewa bane kikayi shiru?
Wai kinsan wa take nufi?
Wannan yaron? Wannan poor yaron? Yaron wannan tsohuwar? Shi wai take so"
Bugun zuciyar zee yashiga qaruwa tana zuciyarta na dan fara nauyi
"haba Zainab, haba Zainab, da kyanki da matsayinki da arziqinki ki rasa wanda zakice kina so sai wannan flirty poor guy?"
Dagowa zee tayi ta kalli daddy tana jin zuciyarta na Bugun daya kusan faso qirji
"Duk masu kudin dake zuwa nemanki? Duk masu matsayin dake zuwa nemanki, duk freaking rich, classic guys nake sonki ki rasa wanda zakice kina so sai wannan?"
"b..but daddy, meye aibunshi?" inji zee cikin rawar murya
Sake Binta da kallon mammaki daddy yayi not believing what he's hearing
"mene? Meye aibunshi kikace? Wai daughter when did you change? Yaushe kika chanza? Magangganunki sam basuyi kama da naki ba"
Itadai mummy kasa cewa komai tayi sai kallonsu kawai datakeyi
"daddy ni aganina what matters is Good characters not wealth" inji zee dakeji kamar tayi kuka
"wai yaushe kika chanza daughter? Ni dake munsan qualities din dakike buqata a namiji, wanda kike ambata min yanzu bana tunanin yanada ko daya"
"that was then daddy, wancan tunanin na da ne, yanzu na gane ba duk kyalekyali keda amfani