Showing 150001 words to 153000 words out of 322641 words

Chapter 51 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4305

da duk dawainiyar dakukayi mana da qaunar da kuka gwadamana amma dan allah karki sake nemanmu, ba don mu ba don Allah"


Kittt.... Taji an katse kiran


Ahankali ta Saki wayar hannunta ta fadi sannan itama ta zame ta zauna kan bedside locker tana kafe waje guda da ido... âœï¸





Ummin fasihu 🧚ðŸ»â€â™€ï¸?
8/2/21, 9:38 PM - BuhainatðŸ˜: *ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸DEEN ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸?*










*049*








*THE ACCEPTANCE*







Maida kanta tayi baya ta jinginashi da bangon bayanta tareda lumshe idanunta



Ita kadai tasan abinda cikin, duk yadda zata musaltashi bazai misaltu ba.


Ta dade sosai ahakan sannan ta bude idanun ahankali ta qurawa saman p.o.p. Din dakin idanu.


Batasan iya lokacin data dauka ahaka ba sai jitayi ana bubbuga kofar dakin


Maida idanun tayi again ta lumshe batareda ta Ko motsa ba.


Bude kofar akayi mummy tashigo

Ganinta zaune akan bedside tana kallon sama yasata ida Qarasowa dakin

"Zainab?"

Bata motsa ba bare ta nuna alamun taji

Ida Qarasowa tayi tadan bubbuga mata kafada
"ke Zainab?"


Sai a lokacin ta bude idanunta dasukayi jawur sannan ta sauke kanta qasa tana cije lower lip dinta


"lfy?" inji mummy tana kallonta


Girgiza kai kawai tayi ahankali batace komai ba

"ki bude baki kiyimin magana mana"


Ahankali ta bude bakin cikin muryar da ita kanta batasan tanada ita ba tace
"lfy lau"


Tsayawa mummy tayi tana kallonta, sosai take bata tausayi amma ya ta iya? Ita kanta daddy fushi yake daita bayama mata magana bare ace zata iya wani abu akai

"kinci abinci?" ta tambayeta a tausashe

Kada kai tayi saikuma ta qara bude baki tace
"eh"

"Good yanzu ki tashi kiyi sallah kinga anfara kiraye kiraye"

"to" tafada ahankali


"tashi to" inji mummy tana dan ja baya don bata damar tashi


Ahankali ta dafa gefen bedside locker din ta tashi tsaye saikuma tayi baya zata zube mummy tayi saurin tarota


"subhanallilah! Are you ok? Jiri kikeji?"


Qoqarin miqewa tsaye tayi tana girgiza kai ahankali Saidai ta kasa tsayawa

"zauna, zauna anan" inji mummy tana kaita gefen gado


Zama tayi takoma ta jingina da gadon tana sauke Ajiyar zuciya

"bakida lfy ne Zainab?"

Idanunta a lumshe ta girgiza kai tana sauke numfashi ahankali

"jiri kikeji?"


Ahankali ta Kada kai
"sannu, bari naje na hadomiki tea kisha saikisha magani ki kwanta anjima kyayi sallar" tafada cikin tausayawa


Itadai zee batace komai ba kuma bata bude idanun ba sai sauke numfashin data cigaba dayi ahankali.


Ahaka taji alamun fitar mummy


Wasu hawaye ne suka kufto daga rufaffun idanun suka gangaro, batayi qoqarin hanasu gangarowa ba don itama tana da buqatar zubdasu Hakan yasa tabasu damar zuba iya son ransu.


Bata san dawowar mummy ba sai jitayi an dafa kafadarta

Bude jajjayen idanun tayi ahankali ta kalli mummy taga itama mummyn kallonta take


"menene kuma Zainab?"


Sauke idanunta tayi a qasa sannan ta girgiza kai ahankali


"Wani abu yafaru kuma?"

Sake girgiza kai tayi ahankali wasu hawayen nasake zubowa

Ajiyar zuciya mummy ta sauke sai ta ajiye mug din tea din hannunta ta zauna kusada ita

"Zainab komai yayi zafi maganinsa allah, don Allah kibar takurawa kanki haka, insha allah komai zai warware, komai zai zama tarihi" tafada cikin sigar rarrashi


Itadai batace komai ba kuma batayi motsiba

"ki zama mai daukar kaddara Zainab walau mai kyau ko akasin haka, kibar sama kanki damuwa arai Hakan na iya affecting lafiyar ki, Kiyi hqr kinji? Insha allah idan kamal mijinki ne babu abinda zai hana ki aureshi amma idan kika cigaba da sama kanki damuwa komai ma na iya faruwa"

Haka taita yimata nasiha, Itadai zee nata saurare batace komai ba har tayi ta gama


Tea din tabata tasha sannan ta bata magungguna suma ta sha sannan tasata kwanciya yadda maganin zaiyi aikinshi yadda anjima zata tashi da qwari qwarin jiki.


Kwanciyar tayi Saidai ko kadan barci be nufo idanunta ba


Haka taita kwanciya har mummy tasake dawowa dakin


Da taimakonta ta tashi tayi alwala tayi sallah sannan ta sake tilasta mata tadanci abinci sannan ta koma ta kwanta.


Haka ta qarasa Wunin nan rabi a Kwance, sosai jikinta ya saki tanajin batada qarfi ko kadan.


Da daddare ma Dakyar tasamu wani barci marar dadi ya dauketa can cikin dare.


Washegari da wani zazzafan zazza6i ta tashi, jikinta yayi ringis sai fidda hucin zafi yake.


Lokacin da mummy tashigo don tadata rikicewa tayi ganin halin da ta tararda Zainab.


Babu shiri tafita ta nufi part din daddy gudu gudu sauri sauri.


A falo ta tarar dashi zaune sanye da brown jallabiya yana qoqarin Kamo tasha

Ganin yadda tashigo a rikice yasashi dakatar da abinda yakeyi yana kallonta da ayar tambaya



"Alhaji zoka gani, Zokaga halin da Zainab ke ciki"


Gaban daddy yafadi Hakan yasa yayi saurin miqewa tsaye yana Sakin remote din hannunshi

"meya faru? Meya sameta?" yafada yana yin gaba batareda ya tsaya jin amsoshin tambayoyinshi ba

Maramashi baya itama tayi suka fito daga part din


Kusan lokaci daya suka sake Shigowa dakin nata inda take Kwance yadda mummy tabarta.


Da sauri daddy yayi bakin gadon ya zauna yana kamo hannun Zainab din


Jinshi rauu da zafi yasashi wara idanu a rikice shima


"Daughter? Daughter! Innallilahi waina ilaihi rajiun" yafada yana dorota jikinshi

Kallon mummy dake tsaye itama gefe hankali tashe yayi yace
"wai meke faruwa ne? Meya sameta?"


Jitayi Tambayar ma tabata takaici sai tace
"ka fini sanin meke faruwa, idan kayi sanadin rasa yar dayar da allah yabamu ai sai kowama ya huta" tafada hawaye na cicciko idanunta


Maida kallonshi yayi akan zee dake sauke numfashi mai zafi ahankali tama kasa bude idanu tsabar yadda takejin jiki


Wayarshi yayi saurin lalubowa a aljihu yashiga kiran family doctor dinsu

Ba'a daga ba a kira na farko ba sai ana biyu


Sallama Dr yayi daga dayan bangaren

"Dr ba lfy, ga daughter na nan in a critical condition, I badly need your help"

Cikin rikicewa shima Dr a dayan bangaren yace
"innallilahi waina ilaihi rajiun! Meya sameta? Ganinan zuwa yanzu"


"No, bari muzo, bazamu iya jira ba muhade a hospital kawai"

"ok.. Ok sir, nima yanzu zan kamo hanya saikun iso"


Katse kiran daddy yayi ya kalli mummy

"maza dauko mata hijab dinta"

Da sauri Mummy ta bude closet dinta ta ciro mata yar madaidaiciyar hijab dinta da taimakonta dana daddy suka samata sannan daddy ya tashi daita ajiki ta tallabeta kamar ya dauki jaririya.


Daddy ne agaba mummy abaya kallo daya zakayi musu kasan a mugun rikice suke


A back seat ya shimfidar daita mummy tashiga itama ta dora kanta a cinyarta sai daddy yakoma mazaunin driver ya bude yashiga yana danna uban horn tun kafin ma ya ida zama sosai


A rikice security yafito, Ganin an tada mota yasa ya tsaya yana kallon motar dazata juyo don ganin su wanene


Hango daddy dayayi a mazaunin driver dakuma nuni dayake mashi na ya bude masu gate yasashi rugawa da gudu ya shiga wangale masu gate din.


Da gudu daddy yaja motar suka zo suka fice suka halba titi.



Sosai daddy ke tsula gudun tsiya akan titi donma gari be ida wayewa ba babu motoci sosai akan titin


Cikin dan qanqanin lokaci suka isa inda kusan shigowarsu tareda Dr din.

Da sauri Dr yafito daga motarshi yanufo tasu da gudu daidai shima daddy ya fito

"Alhaji meke faruwa ne?"

"Tana ciki" inji daddy yana bude seat din baya

Leqawa Dr din yayi saikuma yayi cikin hospital din da sauri

Da taimakon mummy aka fiddota daga cikin motar daidai nan Dr yadawo da wasu nurses jaye da gadon gurgura marassa lfy


Ahankali aka dorata akai sannan aka shiga gurgurata zuwa cikin asibitin mummy da daddy biyedasu cikin tashin hankali.



A wajen ward dinda aka shiga suka ja burki kowa yayi cirko cirko cikin tashin hankali


Da taimakon nurses din aka maida ta kan gadon cikin ward din sannan Dr din yashiga bata taimakon gaggawa don sosai jikinta yayi mugun rauu kamar a oven.


Zainab najin duk abinda akeyi amma she's too weak don ko bude idanunta ma takasa, jin kanta take kamar ta cireshi ta jefar ko zataji sauqin abinda takeji


Sun kusan awa akanta sannan suka samu daidaita temperature dinta aka kuma daura mata drip.


Saida Dr yagama komai Sannan ya juya da niyyar fita yasamu su daddy dayasan suna can cikin tashin hankali

Jiyayi an kama ha6ar rigar shi Hakan yasashi saurin juyowa.

Zee ce riqe da rigar amma still idanunta gamm a rufe

Saurin dawowa wajenta yayi yana cewa
"Zainab, menene? Gayamin how are you feeling? Ina ke miki ciwo?"


Hawaye ne suka gangaro daga ruffafun idanunta

"sorry ok, zaki samu sauqi, ko nakira daddy?"


Ahankali ta girgiza kanta still idanunta a rufe sai kuma tashiga motsi da baki Hakan yasa yayi saurin duqowa don yaji me zatace

"z..zan mutu"

"bazaki mutu ba Zainab, insha zakiji sauqi, kinji?"


Girgiza kanta tayi ahankali wasu hawayen nasake gangarowa

"zan mutu ne, zan mutu idan baka taimaka min ba" tafada cikin dashashiyar muryarta

"zan taimaka miki, kinga ma gashi nan ina taimaka miki ko? Kiyi hqr zakiji sauqi, be strong"


Sai a lokacin ta bude jajjayen gajiyyayun idanunta da har lokacin ke zubda hawaye

"zan rayu ne idan ka taimaka min, ina neman alfarma awajenka Dr, please"

Tsayawa Dr din yayi yana kallonta na wani lokaci sannan yace
"Alfarmar me Zainab"

Hadiye wasu yawu tayi ahankali sannan tace
"kacemasu daddy jinina ya hau, hawan da zai iya bugar da zuciyata, kacemasu zan rasa rayuwata, kacemasu zuciyata takusan bugawa, kace muddin basu bani abinda nake so ba zasu rasani" Sai kuma tafashe da kuka


Tsayawa Dr yayi yana kallonta kawai yakasa cewa komai

"Duk wadannan abubbuwan dana lissafa zasu faru dani soon Dr, zan iya rasa rayuwata soon, ba hakan nakeji ba, wahalar dazani sha nake tsoro, don Allah ka taimakeni, ka ceci rayuwata, ka fadamasu Hakan ko zasu tausaya min su bani abinda nake so"


Sosai jikin Dr yayi laqwas sai kallonta yake cikin tausayawa

Qara kallonshi tayi
"don Allah kar kace A'a Dr, don Allah"






â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸






Safa da marwa daddy ketayi tsakanin farkon ward din zuwa qarshen shi Yayinda mummy ke zaune kamar akan qaya ta buga tagumi kowannensu jini akan akaifa.


Jin budewar kofa yasasu saurin dagowa gabadaya


Ganin fitowar Dr yasasu saurin tahowa wajenshi da sauri

"Dr ya? Ya take yanzu?" inji daddy cikin rikicewa

"karku damu, calm down please, komai zai tafi normal" inji Dr cikin sigar kwantar masu da hankali


"yanzu yaya take aciki Dr, don Allah ka gayamana"


"zan gayamaku yanzu ma kuwa, but mutafi office tukkuna" yafada yana nuna musu hanya nan duk suka rankaya suka nufi office dinshi

Zama yayi a kujerar shi suma suka zazzauna a kujerun dake facing desk dinshi suka zuba mashi idanu cikin neman qarin bayani


Gyaran murya Dr yayi sannan ya zare glasses din idanunta yana kallonsu

"meke damun Zainab ne?" inji Dr


Kallon juna mummy da daddy sukayi sannan suka sake kallonshi

"kamar yaya? Abinda ke damunta ai kai zamu tambaya tunda kai ka dubata" inji mummy


Ajiyar zuciya Dr ya sauke sannan ya koma ya jingina da kujera yace
"abinda yasa na tambayi Hakan saboda naga alamun tana tattare da damuwa ne sosai wanda Hakan ke barazana ga lafiyarta"


"Me Hakan ke nufi Dr?"


Tasowa Dr yayi yayo gaba ya dora hannuwa akan desk dinshi yace
"am sorry amma diyarku tana cikin tsananin damuwa wanda Hakan ya ta6a lafiyarta sosai don a halin yanzu jininta ya hau fiyeda qima wanda Hakan barazana ce ga lafiyarta sosai, zuciyarta na cikin matsala don ba don kun kawota dawuri ba da komai na iya faruwa"


Rufe baki mummy tayi da hannu tana gasping Yayinda daddy yaita maimaita kalmar innallilahi


Ganin yadda suka rikice yasashi cigaba da cewa
"yanzu haka Dakyar nasamu nashawo kan al'amarin, yanzu nayimata allurar barci don tasamu peace of mind yadda zamu samu jinin ya dan sauka"


"innallilahi waina ilaihi rajiun"inji daddy cikin tashin hankali


"ka gani ko? Kaga irin ta Ko? Ai shikenan, saika kasheta kowama ya huta" inji mummy cikin kuka sai kuma ta tashi ta fice daga dakin da sauri



Binta da kallo duk sukayi sai kuma daddy ya dafe kai yana sake ambaton sunan allah


Shidai Dr cigaba da bashi hqr yayi da kwantar mashi da hankali.


Dagowa daddy yayi da idanunshi dasuka Kada ya kalli Dr yace
"meye mafita Dr? Banason rasata, she's the only child I got" inji daddy cikin tsananin damuwa


"ka kwantar da hankalinka Alhaji, insha allah bazamu rasata ba, insha allah zata warke sumul kamar bata ta6a ciwo ba Amma fa kuma Saida taimakon ku, idan har ana son komai ya daidaita jininta ya sauka dole sai an magance matsalar Dake damunta don damuwa da tunani duk suka jawo wannan abin, dole a guji abinda zai qara sata damuwa har hakan yasake tasiri a zuciyarta don akwai matsala sosai"


Furzar da huci daddy yayi daga bakinshi yana lumshe idanu



Ya dade ahakan batareda yace komai ba sai kuma can ya miqe tsaye yana cewa
"shikenan Dr, muna iya ganinta?"


Shima Dr miqewa yayi
"sure, amma kamar yadda nace maka nayimata allurar barci yanzu haka ma barcin take"


"ok babu matsala muje mu ganta din"


Atare suka fito suka sake nufar ward din da zee ke Kwance.


Iske mummy sukayi aciki zaune gefen gadon da zee ke Kwance ta riqe hannunta daya tana kallonta


Tunda tajuyo tayimasu kallo daya bata qara kallonsu ba.


Qarasowa sukayi suma bakin gadon suka tsaya

Kallon zee da idanunta ke arufe daddy yayi cikin wani yanayi yana hango ramar datayi acikin yan kwanakinnan.


Sun dade a tsaye babu mai cewa uffan acikinsu can sai daddy ya juya ga Dr din yace
"Dr please take care of her, abata duk kulawar datake buqata"


"insha allah Alhaji, it's my duty though"

Kada kai daddy yayi sukayi musabaha sannan yajuya yafita.


Saida Dr yaqara dubata ya duba yadda drip din ke tafiya yaga komai normal sannan ya juyo kan mummy dake zaune jigum Tundazu


Rarrashinta da kwantar mata da hankali yaitayi yana assuring dinta komai zai daidaita sannan yafita yabarta da zee din a dakin.




Tunda daddy ya fita be sake dawowa ba sai wajajen 1 na rana kuma har lokacin bata farka ba.

Wannan karon ma ko gefen daddy mummy bata kalla ba har yagaji da tsayuwarshi yasake fita.


Wajajen 2pm wata maid takawo masu abinci asibitin bisa umarnin mummy.

Wajajen uku saura mummy na zaune gefen gadon zee tayi nisa a tunani sai jitayi kamar ana motsi


Saurin maida kallonta tayi ga zee taga itace ke motsin sai qoqarin bude idanunta takeyi


Saurin matsowa kusa mummy tayi tana Kamo hannunta

"daughter?" tafada cikin doqi


Ahankali zee taita kyafta idon gabadaya kafin daga bisani ta ida budesu ahankali


Ganin mummy tayi akanta tana kallonta tana murmushin murna

"Zainab kin farka?"


Batace komai ba sai lumshe idanunta datayi tasake budewa tanajin jikinta so weak


"bari na kira Dr kinji? 1 minute"

Daga haka saita juya ta fice daga ward din


Sake maida idanun tayi ta lumshe tana inhaling da exhaling ahankali.



Ba jimawa mummy tadawo tareda doctor

Babu 6ata lokaci yashiga duddubata


Saida yayi making sure komai is ok sannan ya kalli mummy yace tayi mata brush abata liquid abu mai dumi sai tasha magani.


Da to mummy ta amsa ta tashi shikuma Dr yafita


Da taimakon mummy zee tayi brush sannan tadawo ta hada mata kakkauran tea tana bata cikin kulawa


Sosai zee taji sanyi ganin yadda mummy ke nuna kulawa sosai gareta abinda ta manta rabon da tayi mata ko dayake bata Sakin jiki daita bare tasamu kulawar kullum daddy daddy ko mummy tayi yunqurin yin wani abin sai taqi Sakin jikinta kamar tana tareda wata bare amma yanzu gashi da aka 6ata da daddyn dole aka dawomata.


Saida tashanye tea din sannan mummy tasake kiran doctor din don yabata maganin

Tana cikin shan maganin daddy yashigo dakin.


Tunda taji muryashi ta sunkuyar dakai takasa dagowa ta kalleshi dukda wani feeling datakeji na daban ajikinta


Qarasowa daddy yayi cikin murna yanata hamdala dakuma godewa Dr sannan ya matso kusada zee da har lokacin kanta na a sunkuye

"daughter na?" ya kirata a tausashe

Sai jitayi hawaye sun kawomata a idanu

She missed him, so very much, batasan dahaka ba sai yanzu

"ya jikin?" yafada yana dafa kanta

Kada kai kawai tayi alamun da sauqi batareda ta dago ba don batason yaga hawayenta

Zama daddy yayi gefen gadon shima yana facing dinta ya kafeta da idanu while ita kuma ta kafe yatsun hannunta da idanu


Kamo hannun nata yayi ya riqe yace
"daughter na? Fushi kike da daddyn ki?"


Hawayen datake ta riqewa ne suka 6alle mata batareda ta shirya ba

Jawota yayi jikinshi ya rungumeta Hakan yasa tafara shesheka

"am sorry, am so sorry kinji, am sorry I hurt you, please forgive me" yafada yana patting bayanta itakuma tana cigaba da kukanta

Dago fuskarta yayi yayi kissing goshinta

"ina sonki daughter, bazan iya gangancin dazai sa na rasaki ba don idan narasaki kamar nima na rasa kaina ne, zan qara wata sadaukarwar daughter, zan sadaukar da farincikina Domin naki kamar yadda nasaba.

Na amince, na amince daughter, you can have Deen, allah yasa Hakan shiyafi alhairi"


Batasan lokacin da ta kwace kanta daga rungumar da daddy yayi mata ba tana kallonshi mouth agape


Itama mummy kallon daddy take idanu waje kamar zasu fado daga socket dinsu


Kada mata kai daddy yayi yana murmushi sweetly sannan ya kamo hannunta ya riqe

"ina iya bayar da komai saboda ke amma bazan iya bada ke ba saboda koma menene.

Bazan ta6a yafewa kaina ba idan na rasaki ta dalilin selfishness dina

Bazan ta6a rayuwa cikin farinciki idan babu ke acikinta ba


Kiyi hqr my daughter, I was selfish, I hurted you fiyeda tunani na

Nida ya kamata na kareki daga cutarwa da dukkan rayuwata saiya kasance nike cutar dake, am sorry, forgive your daddy"


Fadawa jikinshi zee tayi tana kuka sosai tana girgiza kai, she can't believe abinda Kunnuwanta ke jiyemata, kodai mafarki takeyi?


Bubbuga bayanta daddy yashiga yi yana rarrashinta sannan ya dagota yayi cupping fuskarta

"ya isa hakanan zee, Deen is now yours" yafada cikin murmushi

"D..dagaske?"


"bari kigani"

Saiya kalli kofa yace
"son!! Bismillah son!"


Duk maida kallonsu sukayi ga bakin kofar zee na jin yadda zuciyarta ke bugawa kamar zata faso qirji


Gani sukayi an murda handle din daga waje sai aka fara turo kofar ahankali

"Assalamu alaikum..." taji cool voice dinshi ya daki Kunnuwanta


Lumshe idanu tayi tasake budewa daidai shima ya ida


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login