Showing 267001 words to 270000 words out of 322641 words

Chapter 90 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6179

yaiwa mutane?"

"ai dama kai ba sonshi ba kake"

"ni ai naga yana sona, Kawai.ku manta dashi kuyi proceeding plan dinku, wayasani ma ko hakan zaifi"

Ajiyar zuciya Ahmad yayi saidai still fuskarshi na nuna alamun rashin jindadi

furzar da huci yayi sannan yace
"ok, bari na lalubo Deen din"

daga kafadu Kawai aymaan yayi yacigaba da danne dannenshi shikuma Ahmad yazaro waya zai lalubo Deen din




***



Kamar yadda batool tayi hasashe tun bayan asr Aysha ta diro gidan

sosai sukayi murnar ganin juna nan suka rungume juna suna murna

bayan sungama suka baje adakinsu batool suna fira Inda anan itama Aysha din tabata birthday gift din data kawomata Inda xee tanuna jindadinta sosai takuma yimata godiya


adakin sukayi zamansu sunata firarsu Inda acan waje Kuma ake decorating garden din daza'ayi dan taron daza'ayi anjima.







*8:00pm*








Ahankali take nada mata veil din cikin qwarewa irin nadinsu na larabawa

saida tagama sannan tadauko turaren dake kan mirror din (aymaan's gift) tashiga feffesamata shi ajiki, nan take dakin yadauki wani qamshi mai sanyin dadi

"wow! gaskiya turarenan yayi, I love the scent" inji Aysha tana ida gyagyaramata Inda beyiba

murmushi Kawai zee tayi

kaucewa Aysha tayi yadda zee zata samu damar ganin kanta a jikin mirron

"now, here you go" Aysha tafada tana murmushi

dagowa zee tayi ta kalli kanta ajikin qaton madubin nan take tawara idanu tana kallon kanta without blinking

dariya Aysha tayi ganin yadda zee ke kallon kanta ta mirror Babu ko kyaftawa sai tace
"to ya?"

cikin wara idanu zee tace
"wai.. dagaske nice anan?"

dariya Aysha tasakeyi tana xagayawa bayanta ta dafa kafadunta ta sunkuyo yadda zasu dinga kallon kansu ta mirror tace
"ga zahiri?"

"wow! this is...amazing! tayaya kikayi transforming dina haka?" inji zee cikin murna

"bani nayi transforming dinki ba, dama ke kyakyawace gakuma kyawawan kaya dole ki chanza... now time for selfie" inji Aysha tana zaro wayarta sukayi posing ta daukesu

daidai nan aka bude kofa batool tashigo

"wai wannan wane irin shiriritane? kunsan lokaci yayi amma kuntsaya kuna..." maqalewa a iska kingin maganarta tayi datayi tozali da zee

wara idanu tayi cikin mammaki tana kallon zee baki bude

"who is this?" inji batool idanunta still akan zee

harararta zee tayi ta kauda kai tana murmushi

"wow! wow! wow!!" tafada tana qarasowa wajensu itadai Aysha banda murmushi Babu Abinda takeyi

"zankad'aziya kenan, wai zee kin ganki kuwa?" tafada tana bin koina na jikin zee da kallo

fari zee tayi da idanu tana tsuke baki
"ya nakoma?"

"kai aradu dafarko nakasa.ganeki, kinga wai yadda rigar tayi maki? kai dole mukashe selfie, tashi tashi" tafada tana zaro wayarta

Nan fa suka samu abin yi sukaita daukar kansu selfie dukkansu suna styles kala2

ahaka har aka sake bude kofar

"wai wannan shirun na lafiya ne? kufa kadai ake jira" inji ummy data leqo

idanunta ne suka sauka kan zee

"kai kai kai masha allah, diyar tawa takoma haka?" inji ummy tana qarasa shigowa dakin

murmushin kunya zee tayi

"kai masha allah, gaskiya kinyi kyau daughter, allah yayi albarka yaqaro shekaru lodi lodi masu albarka"

duk da amin suka amsa harda Aysha Kasancewar duk da turanci suke maganar

"yanzu kuyi sauri inajin ai kungama ko? ku kadai ake jira"

"eh mungama ummy" inji Aysha

"to mutafi, kowa ya hallara ku kadai ake jira"

"ummy baqin sun iso" inji batool cikin zumudin

"idan kika kin gani" inji mummy tana doroma zee hular Abayar bisa kai wanda keda jela jelar zarruruwa wadanda suka dan karemata fuska

kama hannunta ummy tayi sukayi waje su Aysha na maramasu baya



koina tarr yake da haske dukda Kasancewar dare ne, daukar hanyar garden din sukayi suna tafe Aysha na gyarama zee rigarta dake dan jan qasa abaya

Garden din shima tarr yake da haske dake haskowa daga both kwayaye masu haske da masu kaloli

anyi decorating garden din gwanin sha'awa ga fararen plastic kujerun da mutanen da aka gayyata duk suka zazzauna akai

daga gaban mutanen Kuma wata royal blue kujera ce mai kyau sosai sai dan qaramin glass table daga gabanta wanda ke dauke da dan madaidaicin cake dake dauke da burning candles masu kaloli akai.

mutanen wajen basuda wani yawa

daga su Abbu sai su mummy sai su aymaan da Ahmad dakuma iyayen Ahmad din

Ahankali suka qaraso garden din suna tafe fuskokinsu dauke da murmushi

sosai kallo yadawo kan zee wadda taxama kamar tauraruwa acikinsu

Ahankali take tafiya hannunta cikin na ummy dake janta fuskarta dauke da murmushi

dukda bata ganin mutanen wajen sosai saboda baza bazan hularta dasuka dan karemata gani taga alamun mutanen dai nada dan yawa

sautin 'masha allah' keta tashi daga bakunan mutanen wajen cikin yaba irin kyawun datayi wanda hakan kesata murmushin kunya tana qara sinne kai

acan na hango aymaan dake sanye cikin wani danyen tsaddaden yadi kalar madara yaci gayunshi Inda yayi shigar milk and brown

tun lokacin dasuka shigo garden din idanunshi ke kanta ya kafeta dasu babu kyaftawa

dukda baduka fuskar tata yake gani ba yana hango karan hancinta da guntun bakinta dake shining saboda lipgloss datasa, yana ganin yadda yake curving beautifully idan tana murmushi


da kallo yarakasu har ummy ta qarasa daita wajen da aka tanada mata don zama

koda suka isa wajen bata zauna ba sai qarasowa da mutanen wajen sukayi wajenta suka fara gaisawa

akunyace zee keta gaidasu don duk saitaji kanta yayi girma ganin itace centre of attraction din wajen


aymaan dai yakasa ko kyafta idanu akanta duk motsinta saiyabishi da Hazel eyes dinshi

jiyayi an zungureshi hakan yasashi waigowa yana dawowa daga duniyar kallonta

"kallatu ance mutaso mu yanka cake" inji Ahmad cikin tsokana

harararshi aymaan yayi sannan ya tashi suka qarasa wajen mutanen daduk sun koma gaban wajen ana shirin yanka cake din

hada idanu Aysha tayi da aymaan yawani hade rai tareda kauda kai

binshi da kallo tayi saikuma ta ta6e baki itama ta kauda kai

waqar birthday suka shiga yimata suna tafi sannan da taimakon mutanen wajen ta yanka cake din


tafi wajen yadauka sosai ana dariyar farinciki

anan zee tashiga ciyar da makusantanta suna ramawa suma

ciro wani guntun tayi tanufi bakin Aysha dake kusada ita tanata murmushi

cikin murmushi Aysha ta bude bakinta tasaka mata nan ma aka dau tafi

itama Aysha guntun ta dauke ta bata tana lakuta mata sauran akumatu

dariya duk aka dauka ganin Abinda tayi

kamar ance Aysha tadago sai suka qara hada idanu da aymaan

wani mugun kallo ta jefeshi dashi ta kauda kai

Dan buda idanu aymaan yayi yana kallonta saikuma ya kauda kai yana kwafa acikin zuciyarshi


bayan sungama kowa yakoma mazauninshi ya zauna Inda akabar zee kadai gaban wajen zaune a maxauninta

anan ne Ahmad daya ari aikin m.c yafara gabatar da mawaqin dazai danyi entertaining dinsu

be ambaci suna ba Kawai dai gabatarwa yayi mashi yakuma buqaci atafa mashi

tafi din kau aka dauka wanda yayi daidai da shigowar mawaqin filin

sanye yake cikin wani ratsatsen suit fari Inda yayi shigar mai combination din fari da jaa

farin wando sai jar shirt yadora coat fari asama, wuyanshi sanye da jan necktie guntu, kaffafunshi sanye da fararen half cover, yar saisayyayar sumar kanshi sai shining take

abayanshi kuma managern shine kuma mai sakarmashi kida shima cikin shigar suit saidai nashi baqaqe ne

da wannan kyakyawan murmushin yaqarasa shigowa wajen yana kallon mutanen wajen dake tafamashi kowa idanunshi akanshi

ahankali yadanyi bowing alamun godiya still murmushi afuskarshi

habeeb kau tuni yanufi wurin setting dinsu Inda zai dinga sakarmasu kida

musabaha Deen yayi da Ahmad dake gaban stage din sai washe baki yake

mic din hannunshi Ahmad yabashi ya amsa yana godiya sannan yajuyo yana kallon audience din

tun shigowarshi bugun zuciyoyin mutane biyu suka chanza, zee da Aysha

Aysha binshi Kawai takeyi da kallo cikin mammaki da bugawan zuciya

mammaki take yaushe yayanta yadawo daga tafiyar harya zo nan din, saidai kuma sai take ganin kamar bashi ba duba da wasu dabi'u dayakeyi wanda kamar banashi ba, ga sumarshi yar kadan sa6anin ta yayanta dakeda yawa kuma a kwance luff

zee kau bata ganshi ba don yana daga can gefe ne kuma yana facing mutane saidai zuciyarta wani irin bugu take kamar zata faso qirjinta, sosai takejinta awani yanayin da bazata iya musaltashi

ahankali Deen yayi gyaran murya sannan cikin harshen turanci ya gaida mutanen wajen yakuma gabatar da kanshi ta hanyar amfani dasunan da akafi sani dashi wato *Balarabe*

sannan yatayasu murnar wannan taron dasuke na zagayowar ranar haihuwar diyarsu yana kuma yin fatan allah ya maimaita

Tunda yafara magana zee taqame a kujerar datake zaune

kwalwarta ke birgita mata cikin kai tana jin kamar bamaa duniyar ba take

wannan muryar...

waye mai wannan muryar?


ahankali Deen yayima habeeb alamun suje zuwa, nan take habeeb yashiga aikinshi Inda ya sakarmasu wani cool kida mai dadin gaske


lumshe idanunshi Deen cikin son daidaita nutsuwarshi daya rasa Inda ta fece

tun shigowarshi wannan wurin yanemi duk wata nutsuwarshi yarasa, Abinda besaba faruwa dashi ba

yasaba hallarta taron daya linka wannan jama'a linki ba linki amma beta6a tsintar kanshi a irin wannan yanayin ba sai wannan karon, meyasa?


Ajiyar zuciya yasauke ahankali yana iyakar bakin qoqarinshi wurin cooling down

humming yafarayi cikin cool voice dinshi yana lumshe idanunshi


ahankali yafara rero waqar birthday dayayi composing saboda taron


sosai waqar ke tafiya cikin wata iriyar salo mai narka zuciya

tsit wajen ya dauka kowa hankalinshi akanshi suna sauraron yadda yake rairo baitukan waqar cikin qwarewa da salo na daban

kasa ko kyafta idanu Aysha tayi akan Deen, kallonshi Kawai take kamar tana kallon wani hallita daban

yaushe akhie yazama mawaqi?



Tunda yafara waqar zee tarasa awane duniyar take ciki, komai ya burkuce mata, zuciyarta, kwalwarta, ruhinta suka shiga harmutsawa takasa gane takaimaiman Abinda ke faruwa akewayenta Kawai Abinda take iya ji shine wannan muryar

Deen kau a bangarenshi shima bugawar da zuciyarshi keyi yafara affecting waqarshi don sai sarqewa yakeyi akai akai duk iyakar bakin qoqarinshi naganin ya daidaita nutsuwarshi abin ya faskara, jiyake kamar zuciyarshi zata tsinke saboda gudu

habeeb dake gefe yana playing piano yana lura da yanayin Deen dukda bakowa zaiyi saurin fahimtar uneasiness din nashi ba amma shi yagane don yasan Deen yasan yadda yake aikinshi, dole akwai Abinda yake damunshi


dukda Deen nadan kallon gefen zee saidai baya wani tsayawa kallonta don shi kanshi ba Acikin nutsuwa yake ba bare har yatsaya kallon wani abin

aymaan duk Abinda ake idanunshi nakan zee yana lura da halin data shiga

ahankali yaga tamiqe tsaye daga kujerarta tana kallon Deen daya juya mata baya

shima Deen sai akayi daidaitoni ya juyo side dinta cikin waqar yana ambaton birthday girl

sauke idanunshi yayi kanta tana atsaye tana kallonshi shima

wani irin bugu zuciyoyinsu sukayi lokaci guda dukda basu tantance juna ba don zee bata hangenshi sosai saboda hular kanta shima bega fuskarta ba sosai saboda boye rabin fuskar da hular tayi

ahankali ya cigaba da waqar yana kallonta zuciyarshi na lugude


_Happy Happy birthday... to... you..._

yaqarashe baitin da daddaya lokacin da zee tasa hannu tazame hular kanta tafada baya


cak numfashin su biyu ya dauke na wucin gadi

kallon juna suke kamar idanunsu zasu fado Babu mai iya kwakwarar motsi acikinsu

tsit wajen ya dauka kowa idanunshi akansu

jikin Deen ne yafara rawa yadago hannu yana nuna zee da yatsarshi dake rawa lips dinshi ma na rawa as well

"Z... Zainab?.." yafada cikin wata iriyar murya


ko motsi zee batayi ba Kuma ko kyaftawa idanunta dake kanshi basayi

ahankali yafara kusantota still yana nunata jikinshi na rawa har lokacin

"Zainab.."

ahankali kowa yafara tashi daga saman seat dinshi kowanne idanunshi akansu harda habeeb shima da besan meke faruwa ba


ahankali zee tafara takawa tanayin baya baya ganin yana kusantota

kallo daya zakayiwa su biyun kasan babu wanda kecikin hayyacinshi

"Zainab.. stop, please" yafada ganin tana qara nisantarshi

"stop!" yafada yana nufota da sauri kamar mahaukaci

saurin juyawa tayi kamar wanda abin tsoro yabiyo tana tattare rigarta tayi hanyar barin garden

"No! Zainab!" inji Deen yana maramata baya

"Balarabe!" inji habeeb yana takema Deen baya shima


------


saukowa yayi daga cikin motar ya maida kofar yarufe

hannu yasa ya gyara red guntun necktie dinshi sannan ya zagayo ta dayar 6aren motar

bude back seat yayi yadan zira jikinshi ciki can saigashi yafito riqeda abu ahannunshi

maida kofar yayi yarufe yama kulle motar gabadaya sannan yajuyo

dago abin hannunshi yayi yana kallo

qaton bunch of flowers ne mai glass vase daga qasa wajen mariqinshi

misalta kyawun flowern 6ata bakine saidai masu karatu suyi hasashe da kansu saidai kallo daya xakayi mata kasan tsaddadiyace ta qarshe

murmushinshi na gefen baki ya su6ucemashi lokacin dayakai hancinshi jikin flower din ya sinsina

qara riqeta yayi dakyau sannan yafara takawa cikin takunshi ta qasaita ya nufi Inda yake kyautata zaton nan ake taron

tafe yake yana saqe saqen yadda zata kaya tsakaninsu don yasan akwai chakwakiya agaba

yana cikin saqe saqenshi yaji kamar hayaniya na kusantoshi

dagowa yayi wanda yayi daidai da bangajeshi da akayi

baya baya yayi cikin ikon allah kuma yasamu ya tsayar da kanshi

saurin juyawa yayi yabi figure din daya wuce dagudu da kallo

dukda wulgin mutum Kawai yagani amma yagane itace

juyowa yayi yaga meya biyota saidai kafin yayi hakan yaji anqara bangajeshi again wanda hakan yayi sanadiyar su6ucewar flowern hannunshi ta fadi aqasa jikake tassss! tayi qarar fashewa

cikin zafin nama ya damqi gefen rigar wanda ya bangajeshin ya maidoshi baya daqarfi daga yunqurin yin gaba dayakeyi


dagowa sukayi atare suka kalli juna lokaci guda oily eyes dinsu na sarqewa ana juna....✍?



*please masu kirana ina typing kuna maidomin aiki baya, koyaya nadaga kafin nagama wayar Abinda narubuta ya fece shiyasa ma bana dagawa, please ku dinga yin haquri tunda ku ma kunsan inamuku iya qoqarina*



Ummin Fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*











*084*








*THE REUNION*







wani irin jada baya su biyun sukayi kamar wadanda aka tura da force mai qarfi


alokaci daya suka sake wara oily eyes dinsu akan juna suna kallon juna kamar suna ganin wata hallita daban ne ba mutum ba

wani irin rawa inner part dinsu ya dauka zuciyoyinsu na wata iriyar halbawa kamar zata faso qirjinsu


habeeb ne yafara qarasowa wajen saidai babu shiri yaja wani irin mugun burki lokacin dayayi tozali da Deen guda biyu suna kallon juna


dauke numfashinshi yayi yana wani irin kwalalo idanu waje kamar zasu fado daga socket dinsu

daidai nan kingin jama'ar suka qaraso wajen Inda suma sukaci karo da the same scene

suma anan suka taka burki suna kallonsu kowanne speechless

wani irin gasping Aysha tayi mai sauti tana yin baya baya

aymaan dake bayanta yayi saurin tarota daga faduwar datayi niyyar yi tafado jikinshi

"Hey.." inji aymaan yana kallon yadda take farfar da idanu

mummy ce data lura dasu tayi saurin qarasowa wajensu itama takama Aysha din da kejin kanta na juyamata

ganin hakan yasa itama umman Ahmad matsowa sai aymaan ya sakarmasu ita


ahankali Mussadiq yaqara jabaya still idanunshi dasuka fara sauya launi akan Deen, komai na jikinshi rawa yake ga jijjiyoyin kanshi dasuka fito rad'o rad'o


cikin kidima da fitar hayyaci yasa hannu yazaro wata qaramar pistol from nowhere ya nuna Deen da haryanzu yakasa motsi daita


yadda jikinshi ke rawa haka hannunshi dake riqeda bindigar keyi don saima yitake kamar zata silale dukda iyakar qoqarin dayakeyi na riqeta sosai


"w..who are you?" yafada cikin wata iriyar murya dake rawa sosai

duk buda idanu mutanen wajen sukayi suna kallonsu cikin kidima

"speak or I shoot!" inji Mussadiq cikin qaraji jikinshi na rawa sosai yana qara nuna Deen da bindigar, kallo daya zakamashi kasan baya cikin hayyacinshi don ko cewa akayi ya danna kunamar bindigar baya iyawa saboda rawan da ilahirin jikinshi keyi

shikau har lokacin Deen kasa ko kwakwarar motsi yayi Kawai yana tsaye ne yana kallonshi kamar gunki

rolling idanu aymaan yayi cikin zuciyarshi yana cewa
'ai dama nace wannan mutumin mahaukaci ne'


"mu..Mussadiq"

"speak!" Mussadiq ya katse Ahmad daya fara magana

"Mussadiq calm down.."

"go away!" yafada yana maida akalar bindigar kan Ahmad

"listen son.."

"who are you? kusu wanene!"
yaqara fada yana pointing dinsu duka yana jabaya, sosai alamun gigita ta bayyana ajikinshi


ahankali bindigar ta su6uce a hannunshi dake karkarwa ya cigaba da kallon Deen yana haki

"calm down son.. calm down, this is your twin.. Mujaheed" inji Abbu dake qoqarin calming dinshi down

dago rinnanun idanunshi yayi ya kalli abbu

"yes, Mujaheed.. your lost brother"

"No.." inji Mussadiq cikin muryar mai kama da rad'a

"yes.."

"he's dead" yaqara fada

"he's alive"

"No"

"calm down"

"No.. No!" yafada yana dafe kai

"Mussadiq.." inji Abbu again yana qoqarin kusantoshi

"No, don't come closer.. don't" yafada yana jada baya

duk tsayawa sukayi suna kallonshi

saurin juyawa yayi cikin sassarfa zai bar wajen sai gani sukayi timm yafadi aqasa


gasping mutanen wajen sukayi sukayi saurin nufarshi

dagoshi sukayi sukaga kamar ma baya motsi

"aymaan quick kawo mota" inji Abbu

juyawa aymaan da be motsa daga Inda yakeba tundazu yayi yanufi parking space Ahmad kuma yanufi Deen dahar lokacin baya motsi kamar wanda aka dasa

"Deen" yafada yana ta6a kafadarshi saidai beko dago bayan bare ya kalleshi, idanunshi nanan kyar akan Mussadiq

habeeb ma yana daga baya kusan shima suman tsayen yayi don yakasa motsawa daga Inda yake saidai ya kalli wannan ya kalli wannan atsakanin Deen da Mussadiq


aymaan ne ya qaraso da motar wajen yafito da taimakonshi aka daga Mussadiq aka sakashi abayan mota tareda Aysha da itama tuni tasuma

aymaan yashiga front seat dashi da Abbu

yayinda Ahmad yaja hannun Deen suka nufi motarshi shima yasakashi a front seat habeeb yayi saurin binsu yashiga backseat shikuma Ahmad yazagaya mazaunin driver

ganin hakan yasa su kingin suka shiga wata motar Inda akabar ummy datace zata tsaya tareda zee agidan

ajere motocin suka fita daga gidan suka halba titi


***


dagudu zee tayi hanyar stairs tana hayewa da bibbiyu bibbiyu

ba don allah ya tsareba data sha qasa yadda rigar keta tadeta tana kawo mata tirjiya a gudun nata

bata ja burki akoina ba sai dakinsu Inda tashiga ta maido kofar tarufe ta danna sakata sannan tanufi toilet dagudu shima tabude tashige tarufo harda murza makulli.


komawa tayi ta jingina da kofar tana maida numfashin gudun datayi

_Deen_

_Deen dinta tagani_

_Deen dinta_

hannu bibbiyu tasa ta toshe bakinta dasu tareda silalewa qasan tiles

wani irin kuka yazo mata mai tsuma zuciya tashigayi hannunta toshe da baki dukkan ilahirin jikinta na gab gab


kuka take da dukkanin zuciyarta jikinta na rawa sosai, she can't believe yau idanuwanta Deen suka gani, Deen dinta, her timid, silly boyfriend. wanda ta yanke qauna dasake sakashi a ido.

zuciyarta takasa yarda, kwakwalwarta takasa dauka.

bugun kofar dataji ne yasata dan tsagaitawa daga kukan datake

kofar dakin ake bubbugawa ana kiran sunanta

data saurara saitaji muryar ummy ce

sosai take bubbuga kofar tana kiranta tazo ta bude

maida kanta zee tayi jikin kofar ta lumshe idanu wasu hawaye nasake gangaro mata

tanajin ummy nata haukan bubbuga kofar da kiran sunanta amma takasa koda motsi ne bare ta iya tashi ta budemata







***



tsaye yake yana kallon Mussadiq dake kwance bisa gado ta glass kofar dakin a gefe guda kuma yana sauraron Dr dakemusu bayyanin cewa yanzu komai normal dama shock ne kuma lokacin dazai farka zai sakeshi komai zai koma daidai

haka ya tsaya yana kallon photocopy dinshi dake kwance ko kyaftawa babu kwakwalwarshi ta hargitse ta yamitse yarasa wane tunani ma zaiyi

"Balarabe" muryar habeeb tadawo dashi daga duniyar kallon Mussadiq

dagowa yayi ya kalleshi saikuma ya maida kallonshi akan mutanen wajen yana binsu da kallo


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login