Showing 162001 words to 165000 words out of 322641 words

Chapter 55 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4328

tsayawa wuri guda yayi, safa da marwa kawai yakeyi cikin tsananin tashin hankali, idan ya kalli kofar da aka shiga da zee sai yaji kamar yaje ya 6allata yashiga yaga wane hali take ciki.


Babban tsoronshi shine kar ciwon ta ya tashi wanda Dr yafada musu wancan karon, he's scared, bazai iya musalta rayuwa babu sanyin idanunshi Zainab

"Hasbunallah wa ni'imal waqeel! Innallilahi waina ilaihi rajiun! Innallilahi waina ilaihi rajiun! Ya allah help me, don’t take her away From me now, not now please, I can't take it" yafada cikin tsananin tashin hankali still yana zirga zirganshi


"Alhaji kayi hqr, insha allah zata tashi, insha allah allah zai tashi kafadunta" inji bala cikin tausayawa da son qarfafa mashi gwiwa



Ko kallo be isheshi ba ya cigaba da zirga zirganshi yana cigaba da sambatunshi




Sosai likitocin suka jigatu kafin su samu su daidaita numfashinta don dole suka maqalamata abin oxygen a hanci wanda zai taimaka mata wajen numfashi


Sosai jikin family Dr dinsu yayi sanyi liqis don qaryar dasukayi wancan karon itace ta tabbata

Jinin zee yayi mugun hawa, hawan da ba'aso saboda hadarinshi.


Saida suka shafe fin awa sannan suka samu komai yadawo daidai suka fito kowannensu na sharce zufa



Daddy na ganin sun fito ya nufosu da sauri kamar zai kifa qasa

"Dr ya ake ciki? How's my daughter?" yafada ajere


Daya daga cikin doctors din yace
"calm down Alhaji, komai yadawo normal yanzu insha allah"


"to muje naganta, I want to see her" yafada zaiyi hanyar dakin da aka kwantar da ita din

Taroshi ainahin Dr dinsu yayi yana cewa
"A'a sir, not now yanzu ba'ason kowa yashiga wurinta, ka kwantar da hankalinka insha allah she's safe now, muje office mu tattauna"


Dakyar suka samu ya haqura da shiga din yabisu office din don tattaunawar kamar yadda sukace.




***


"inajinku Dr(s), don Allah karku fadi abinda zai bugarmin da zuciya" inji daddy da kallo daya zakamashi kasan yana cikin tension sosai


Daya daga cikin likitocin ya sauke Ajiyar zuciya yace
"Alhaji ka kwantar da hankalinka kuma kasa aranka dik abinda yasamu mutum jarabtace daga allah, da lafiya da rashinta dik na allah ne..."


"Duk nasan da wadannan Dr, basu na tambaya ba, lafiyar diyata nakeson ji" inji daddy cikin qosawa


Dayan likitan yace
"alhamdullilah Alhaji, yanzu mun samu mun shawo kan komai, dama jininta ne yayi mugun hawa, hawan lokaci daya wanda Hakan keda matuqar hadari don a wasu unlucky case din sai kaga mutum ya fadi sanadiyar Hakan ya tashi da mutuwar 6arin jiki amma alhamdullilah nata yazo da matuqar sauki plus ankawota asibiti da wuri an takama abin burki cikin gaggawa, saikuma numfashinta dayayi qasa sosai yana neman seizing shima mun samu shawo kan Hakan yanzu Hakan tanacan maqale da abin oxygen wanda ke taimaka mata wajen daidaita mata numfashinta"



Dafe kai daddy yayi yana kallon saman desk din gabanshi not saying anything, shi kadai yasan halin dayake ciki


"kayi hqr Alhaji, insha allah all will be well" inji wanda yagama bayanin yanzu


"to yanzu ina iya ganinta please" inji daddy


"No Alhaji, kayi hqr don Hakan sa6ama doka ne, tana intensive care yanzu babu mai shiga wajenta yanzu sai doctors"

"Koda ba ciki ba, Koda tawaje zan hango ta ina dai son ganin halin datake aciki ne" inji daddy


Kallon juna likitocin sukayi sai family Dr dinsu yayi Ajiyar zuciya yace
"muje Alhaji"


Jin Hakan yasa Alhaji miqewa da sauri Dr din yayi gaba shikuma Alhajin yabishi abaya suka fice daga office din


Kamar yadda sukayi lokacin da aka kwantar da Deen a asibitin haka akayi wannan karon ma



Recording room suka wuce inda anan aka haskoma daddy dakin da zee ke Kwance


Ganin zee Kwance kamar bata numfashi maqale da wannan abin a hanci ba qaramin girgiza zuciyar daddy yayi ba



Qurawa Mafi soyuwar diyarshi ido yayi yana jin kamar ya dauke mata ciwon ya maido jikinshi.


Idanunshi daya quramata sun kada sosai zuciyarshi banda zafi babu abinda takeyi


Juyawa yayi don bazai jure kallonta a wannan halin for a long time ba


Bude kofar wajen yayi ya fita.


Bala dake zaune Tundazu ganin daddy ya fito yana tafiya kamar wanda zai tashi sama yasashi saurin miqewa tsaye


Ganin waje ya nufa yasa shima yin saurin take mashi baya.


Dagudu ya rigashi isa motar ya budemashi.

Shigewa yayi batareda ya kalleshi ba yana daddana wayarshi at the same time.

Rufo mashi bala yayi ya zagaya dagudu gaban motar ya bude yashige shima

Tada motar yayi daidai lokacin dayaji daddy na cewa

"wlh bazan bar yaronnan ba, duk inda yashiga sai an nemoshi kuma wlh wani abu yasaki yasamu diyata just hold yourself responsible tunda harda hadin bakinki wajen cutar ta!"

Kana jin yanayin yadda yake magana zakasan ranshi a matuqar 6ace yake

"just shut up! Duk ba ke kikafi bada gudunmawa a komai ba?! Dama ni tun farko ban yarda dashi ba Amma kika nace, kuka nace! To gatacan ya kasheta, ga gawarta can hospital saiki zuba ruwa qasa kisha, dama ai ba sonta kike ba! Mtcheew"

Ya katse kiran cikin qunar zuciya yana huci


Kallon bala dake driving yayi sai ya daka mashi tsawar da yakusan sawa ya saki sterring din


"gidan ubanwa zaka kaini! C'mmon kaini police station! wlh zai san ya ta6a jinina! Saisan Jinin dan faranshi ya ta6a!"


Shidai bala daya samu ya iya ruqo sterring din daga kufcewar dayaso yi yayi u-turn ya kama hanyar nearest police station kamar yadda ya buqata




Sosai hankalin mummy ya dugunzuma ya tashi

Babu abinda ta fahimta a magangganunshi sai gatacan ya kasheta, ga gawarta can hospital

Gawar wa?

_wa suka fita tareda shi?_ zuciyarta ta tambayeta

_Zainab?!_


Babu shiri ta bude daya daga cikin locker dinta ta zari makullai ta Ciro na mota aciki ta figi gyallenta ta yafa ta fice daga dakin hankali tashe



Saukowa tayi qasa ta wuce kofar fita cikin sauri ta bude ta fita ta maido ta rufo


Parking space ta nufa ta danna remote din car key din don rikicewa ma ta hana tasan makullin wace mota ta dauko


Motar dataji tayi tsuwa ta nufa ta bude mazaunin driver tashiga sannan ta maida ta rufe sannan ta tada motar tafito daga parking space din tazo tawuce security din daya bude mata gate din ta fice in speed.




A bangaren daddy kau suna isa police station ya sauko ya shiga ciki kamar zai tashi sama


Kasancewarshi na babban mutum kuma shahararre yasa babu 6ata lokaci aka hada shi da d.p.o kamar yadda ya buqata.


Anan ne yayi stating qarar Deen daya kawo ya hada da qarya da Gaskiya ya fada aka rubuta


Sannan yasa a nemoshi duk fadin Katsina dama kewayenta yakuma yimasu albishir din kyauta mai tsoka muddin suka samo mashi shi.


Abinka da abin manya nan da nan aka bazama neman Deen, aka bugamashi tambarin *WANTED.*



Ganin komai ya tafi yadda yakeso saiya baro police station din yadawo asibitin


Suna yin parking ya bude kofar motar yafito batareda ya jira bala ya zagayo ya budemashi ba.


Direct emergency ya nufa ya kama hanyar ward din zee.


Tun daga nesa ya hango mummy zaune akan bencin dake kofar ward din


Ranshi ne yaqara 6aci Hakan yasa ya qara tamke fuskar kamar hadari


Dagowa mummy tayi da idanunta dasukayi jajur wanda da alama itama kukan tayi ta kalli daddy daya qaraso wajen.


Kasa yimata masifar dayayi niyyar yimata yayi sai kawai ya cigaba da binta da mugun kallo mai cike da haushi da takaici


Sauke kanta tayi qasa itama tana share hawayen dasuka sake gangaromata.



Juyawa yayi kawai ya kalli gefe yana jin 6acin rai har lokacin

Haka yaita tsayuwa yana kallon gefe itakuma tana zaune kanta a qasa babu mai cewa uffan


Can dai daya gaji da tsayuwar saiya wuce ya kama hanyar dazata sadashi da office din Dr din nasu.



Cikin gari kau neman Deen ake takoina, bincike akeyi babu kama hannun yaro yadda kasan wani kasurgumin 6arawon daya kufce suke nema.


Har school Saida yansandan sukaje bincike aka dauko masu file dinshi inda anan dinma basu samu wani gamsashen information dazai basu hint din inda yake

Acan unguwarsu ma akwai yansandan da aka tura can

Inda anan aka kirawo mai gidan da suke zaman hayan gidanshi


Tambayoyi harna innanaha Saida sukayi ma mutumin sai abinma yayi kamar zai juye kanshi don sai tuhumarshi suke wai ya za'ayi yaba wadanda besaniba kuma besan kowa nasu ba haya?

Haka aka taru a kofar gidansu Deen din anata abu guda inda shima mallam Nasiru akaso shafa mashi shima wai ai shima yanada kusanci sosai dasu don haka dole yasan wani abu gameda guduwansu.


Abu dai ya cakule ya rikice don tuni unguwar ta dauki shelar ashe su Deen yan danfara ne? Danfara sukayi suka gudu gashi anzo ana nemansu ruwa ajallo


Kan kace me? Maganar tayi spreading kamar gobara a busassun ciyayi, inda Mafi yawancin mutane suka yarda suna allah wadai dasu, qalilan kuma basu yarda ba Suna cewa sharri ne ciki harda baaba abu data yini kuka.


Daga baya dai 6alle kofar akayi aka shiga gidan aka bincikeshi kaff


Komai na gidan na nan except kayan sawansu Hakan yasa aka maida aka kulle akan zasu dinga dawowa akai akai don bincike suka kuma sanar duk wanda yaga wulginsu yayi maza ya sanar dasu don cafkesu.

Sosai jikin mallam Nasiru yayi sanyi dama mutanen unguwar gabaki daya.

Matar mallam Nasiru kau itama kuka taitayi tana rantse rantse akan wlh qazafi ake musu babu yadda xa'ayi Deen ya iya danfaran mutum.

Haka dai unguwar nan ta Wuni da zancen bayin allah nan a bakunan mutanen unguwar, abu dai babu dadi






A bangaren zee kau har dare bata farfado ba


Da farko likitocin cewa sukayi suna iya tafiya basai an kwanan mata ba Amma cikin daddy da mummy aka rasa wanda zai yi yadda suka ce din


Anyi rarrashi anyi komai amma ko motsawa daga inda suke basuyi ba hakan yasa aka kyalesu kawai aka basu wani ward din dake gefen na zee don suyi spending dare aciki.


Haka suka kwana a asibitin ko kalma daya bata shiga tsakanin mummy da daddy ba.


Shi daddy najin haushin mummy don gani yake duk itace silar komai itakuma mummy damuwar datake cikima ya isheta kaya.

Haka sukayi kwanan zaune duk babu wanda ya iya barcin kirki ita mummy daga baya ma wajajen 4am ta tashi tafara nafilfilu har asuba tayi ta dora da sallar asuba shikuma daddy ya fice massallaci.



A taqaice dai Saida zee ta kwana biyu a wannan dakin da ba'a shiga ganinta a kwana na uku aka chanza mata ward inda lafiya lau ana iya zuwa ganinta Saidai shima banda hayaniya izuwa lokacin anriga ancire mata abin oxygen din hancinta don tana iya breathing da kanta


Izuwa lokacin duk yan uwa da abokan arziqin su mummy da daddy sun sani

Yan Ruma dama yan uban su daddy labari yakai musu Hakan yasa sai tururuwar zuwa ganinta akeyi.


Daddy su biyu mahaifiyarshi ta haifa dashi da qanwarshi Ummu batool sannan tafita daga gidan inda anan tabar daddy wanda yasha wahalar matar uba da yaranta sosai.

Be samu sauqinsu ba Saida yashiga secondary school aka sakashi boarding, to tun lokacin yaja baya Sosai da yan uban nashi dama gidan uban nashi gabadaya don ko hutu akayi gidan da mahaifiyarshi ke aure nan yake zuwa ko kuma yayi hutunshi a school din.


Ana haka allah yayiwa babbansu rasuwa lokacin yana S.S 2

To rashin mahaifin nashi a gidan yasa ya ida qauracewa gidan don Koda aka raba gado ya tsira da daki daya acikin gidan siyarwa yayi ga babban wansu don a lokacin idan akwai abinda ya tsana to gidan ne da ahalin ciki.


To ahaka daddy ya cigaba da karatunshi mahaifiyarshi na taimaka mashi da mijinta shima kuma yana yan buga buganshi har yasamu ya qare secondary school din ya shiga jami'a inda yashiga course din business saikuma ya hada karatun da zuwa kasuwa inda ya kasance yaron shagon wani babban dan kasuwa a kasuwar garin nasu.


Ahaka ahaka har yayi graduating lokacin ya goge sosai a harkar business shiyasa Koda shima yafara cikin qanqanin lokaci abin ya bunqasa allah yasamashi albarka a harkar, abin yaita gaba gaba har yakai matsayin dayake aciki yanzu.

Shekara daya da yin auren daddy da mummy allah yayiwa mahaifiyar daddy da mijinta rasuwa a wani hadarin mota dasukayi a lokacin zasu kai ziyara garinsu mijin.

Shiyasa yanzu bayada dan uwa makusanci sosai kamar Ummu batool wanda ke aure Dubai tanada 'ya'ya biyu, namiji da mace
Namijin mai suna Abubakar sadeeq amma kasancewar sunan uban mijin Ummu batool ne dashi sai aka sakaya sunan ana kiranshi da *Aymaan* ita kuma macen sunanta Fatima amma itama ana kiranta da *Batool*



Tsakanin daddy da yan ubanshi babu yabo babu fallasa ana dan zuminci sama sama kuma dama suma mahaifiyarsu ta dade da rasuwa kuma duk yawancinsu ba agarin suke ba musanmman matan wadanda aure ya kaisu wasu wuraren.

Bama cika sanin halin da junansu suke cikiba inba ta kama ba don sosai zumincinsu keda rauni bama zaka ta6a cewa sun hada uba ba.


To a wannan case din yarasa wanda ya gayamasu ma don shidai be gayamasu ba Saidai kawai yaga wasunsu sunzo dubiya.


A bangaren abokan aikinshi ma duk sun zozzo inda amininshi baban asaad shine gaba akan komai don shima sosai ya nuna damuwarshi akan hakan don yama kusan fin daddy nuna damuwa.


Suma yan Ruma sun zozzo ganinta inda duk yawancin wanda yaji labarin abinda yafaru sai ya jajanta inda mafiyancinsu ke xagin Deen dama yima samari gabadaya kudin goro acewarsu dama samarin yanzu duk tarin mayaudara ne da wuya kasamu mai so don Allah


A bangaren yansanda kau haryanzu neman Deen suke Saidai cikin kwanakinnan ko mai kama dashi basu gani ba kuma har lokacin basu samu wani kwakwaron hint ba na inda zasu ganshi



Kwanan zee biyar a asibitin a daren kwana na biyar din ta farka.


Lokacin mummy nakan sallaya ta idar da sallar isha'i kenan kamar ance ta juyo sai gani tayi tanata marr marr da idanu alamun sotake ta budesu



Ganin Hakan yasa ta tashi da sauri tazo bakin gadon tana kallonta.

"Zainab" ta kira sunanta

Cigaba da qoqarin bude idanun zee tayi Hakan yasa mummy ta juya ta fita daga dakin don kiran doctor


Fitar mummy keda wuya idanunta suka bude ahankali.

Hasken dakin daya haske mata idanu yasa taqara maidasu ta rufe can kuma taqara budesu ahankali tana jin yadda sukeyi mata wani yaji yaji.


Ahankali take wurwurga idanun nata don tantance inda take.


Bata ida tantancewa ba mummy da doctorn dataje kirawowa suka shige shigo dakin.


Saurin Qarasowa bakin gadon sukayi gabadaya suna kallonta itama tana kallonsu kamar mai son karantar wani abu a fuskokinsu

Babu 6ata lokaci Dr yashiga dubata ita kuma zee ta maida idanunta ta rufe trying very hard wajen son tuno abinda yafaru


_gobe ne_

Ta tuna Maganarshi ta last call dinsu dasukayi a daren ranar introduction


_I LOVE YOU_
ta tuno kalmar qarshe data karanta a wannan takardar


_natafi... Am gone... Maybe forever.. Maybe not_



Ahankali ta bude idanunta lokaci guda dukkanin abubbuwan dasuka faru suna rushing back a kwalwarta


_I LOVE YOU_
itace kalmar qarshe data karanta daga haka batasan abinda yasake faruwa ba sai yanzu data bude idanunta


And then she realize, she realize cewa yafadi Gaskiya.. Yafadi Gaskiya dayace ya rarratsa zuciyarta into pieces don yanzu haka abinda takeji kenan

Jin zuciyarta take kamar glass din da ake rarratsewa into tiny tiny particles


Zuciyarta taji rauni, mummunar rauni don yanzu haka bleeding take, unstoppable bleeding


Kuma the worst thing shine wanda duk duniya tafi so tafi bama yarda shine silar wannan raunin

Shine ya luma mata kaikaifan wuqa a qahon zuciya ya barta aciki yayi tafiyarshi


_*DEEN*_.... ✍️






Ummin fasihu 🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:39 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?*








*053*






*INCOMPLETE*






Ahankali ta maida idanun ta lumshe tana hadiye yawu ahankali.


Zafi takeji, zafi mai mugun radadi a zuciyarta, jitake kamar ana gasa mata zuciyar ne a oven kuma ana tarfa mata narkakkiyar darma.


Abinda takeji bazai iya musaltuwa ba koda zata musalta bazaka ganeba inba kaima tsintar kanka kayi aciki irin halin datake ciki kayi ba wanda bata fatan ko maqiyinta yashiga irin halin data shiga


"sannu Zainab" inji Dr yana kallonta


Bata bude idanunta ba Haka ma bata motsa ba bare asa ran zata amsa


"Me kike ji yanzu? Kina jin wani ciwo?" inji Dr din again yana kallonta keenly


Nan ma ko motsawa batayi ba


"Zainab.." taji tender voice din mummy


Ahankali ta bude lumssasun idanun nata ta dagasu ta zubama mummy din


Wani irin tausayinta ya tsirgama mummy ganin irin kallon datake mata, a very painful look


Sanin abinda tafi buqata yanzu yasata Qarasowa ta zauna gefen gadon ta kama hannun zee dake daure sa cannula tana kallonta

Itama zee ita take kallo babu ko kyaftawa

Ahankali mummy ta jawota jikinta tabata warmly mother's hug wanda ta rabu da yimata


Wani nannauyan Ajiyar zuciya zee ta sauke tana qara cusa kanta a wuyan mummy

Lumshe soyayyun idanunta tayi tasake budewa


Da ada ne da yanzu tafara hawaye ko kuka amma yanzu shiru kakeji, sotake tayi amma ya gagara, idanunta sun bushe, zuciyarta ta soye, kukan is nowhere to be found


Dagota mummy tasakeyi tana kallonta, lumshe idanu zee taqarayi ta bude su akan fuskarta itama

"Are you ok dear?" inji mummy tana kallonta cikin kulawa


Wani dan murmushi ya kufce mata wanda kallo daya zakamashi kasan murmushi ne mai ciwo


Ji mummy tayi kamar tayi mata kuka, dukda bazata iya cewa tasan exactly abinda zee keji a zuciya ba Amma tasan dole yanzu she's in pain


"meke yimaki ciwo? Kifada kinga sai Dr ya dubaki" inji mummy tenderly


Kama hannun mummy zee tayi ahankali sannan ta dora saitin zuciyarta daketa halbawa in speed


Saurin kauda kai Mummy tayi sanadiyar hawayen dasuka kuftomata sai kuma tajuyo tajawo Zainab a jiki ta rungume qamm

Qara cusa kanta zee tayi a wuyan mummy ta maida idanunta ta lumshe tana sauraron sheshekar mummy tana jin dama ita allah zaiba damar yin irin wannan kukan ko ba komai zata hawayen zai wanko kadan daga cikin raunin dake zuciyarta


Dr din ma kallonsu yake cikin tsananin tausayawa, jikinshi duk yayi sanyi


Saida mummy ta share hawayenta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login