Showing 159001 words to 162000 words out of 322641 words

Chapter 54 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6211

buga wayar, switch off



Tun tana daurewa tabar abin iya cikinta har takasa ta tunkari daddy da maganar don ko giyar wake tasha bazata ta6a nufar mummy da wannan maganar ba don haryanzu mummy bata sauka daga 6acin ran datake aciki ba


Koda ta fadama daddy abinda ke damunta dakuma fargabar kar ace ba lafiya ba sai shima ya damu yana jin Gaskiya ya kamata a bincika Hakan yasa ya qara aika bala unguwar tasu Deen don ganin ko sun dawo gidan


Amma daya dawo amsa daya ce haryanzu, gidan a kulle yake still da kwado kamar dai yadda ya ganshi jiya.


Sosai hankalin zee yaqara tashi.

To meya faru?

Ina suke?

Yaushe zasu dawo?

Dama sauran tambayoyi da dama keta kai kawo a qwalwarta wanda duk babu mai bata amsoshinsu.



Ganin yadda ta tashi hankalinta yasa shima daddy shiga damuwa sosai don shi yanzu baya qaunar abinda zai sakata a damuwa saboda maganar Dr dayayi akan a kiyayi barinta cikin damuwa, he can't afford to loose his only daughter just like that Hakan yasa yaita rarrashinta da kalamai na kwantar da hankali yana assuring dinta insha allah gobe zaije shima da kanshi yagani da kanshi.


Hakan yadan kwantar mata da hankali har tadan samu taci abinci kadan wanda shima tutturawa kawai tayi bawai don dadi ba don kwata2 rasa abinda ke mata dadi a duniya tayi ga wani fargaba ta musanmman data addabi zuciyarta



Mummy kau duk abinda suke ko kallo basu isheta ba don ita tun jiya zuciyarta ke cinkushe.


Tarasa ma a wane siga zata kalli wannan al'amarin

Qin zuwa sukayi da gangan koko akwai dai abinda ke faruwa?


Sosai ranta ke a dagule saboda wannan abin daya faru Saidai kuma haryanzu takasa dora laifin akan Deen ta kuma kasa yarda da abinda zuciyarta ke saqamata na kodai Deen yaudarar zee yake dama bawai auranta yake so yayi ba?

Da wannan tunanin yazo mata sai tayi saurin kawar dashi tana girgiza kai don Gaskiya Deen beyi kama da mayaudari ba kuma tana hangen soyayyar zee a idanunshi tsantsarta, to a ina matsalar take? Tabbas akwai lauje cikin nadi.



Washegari kamar yadda daddy yayi ma zee alqawari wajajen bayan 12pm na rana ya shirya tsaf don zuwa dubowa shima don tunda gari ya waye zee ta matsa mashi akan Hakan


Itadai mummy haryanzu batace uffan ba akan komai ba, yima takeyi kamar batasan sunayi ba.


Har parking space ta raka daddy din tana jin kamar tace zata bishi itama suje su dubo tare.


Saida taga fitarshi daga gidan sannan ta juyo a sanyaye tadawo falo ta zauna a kujerar da take facing kofar Shigowa ta raku6e ta zubama kofar idanu tana jiran ganin ta inda daddy zai dawo.


A lokacin idan kaga Zainab dole tabaka tausayi, tawani yi laushi ta sururuce, kallo daya zaka mata kasan tana cikin damuwa sosai.


Ta dade anan zaune tana counting down din seconds daya gota ma agogo tana jiran ganin dawowar daddy, deep down kuma addu'a kawai takeyi allah yasa adace don yanzu idan akwai labarin da zaisata cikin matuqar farinciki to na ganin Deen ne, kawai ita dai burinta aganshi a tabbatar da lafiyarshi lau.



Har 2pm ta gota daddy be dawo ba hakan yasa ta tashi don dole ta wuce sama don yin sallar zuhr.


Tana zaune akan sallaya ta gama sallah taji horn din mota a bakin gate


Aikau babu shiri ta tashi tsaye tanufi windon nan da sauri ta yaye labulen


Motar daddy ta hanga tashiga parking space.


Sakin labulen tayi ta juyo tanufi kofa da sauri.


Budewa tayi ta fita ta sauko stairs din tana tsallakesu da bibbiyu harta samu ta ida saukowa.


Daidai takai hannu a handle aka murda handle din daga waje aka turo kofar.


Jan burki daddy yayi da farko ganinta a bakin kofar saikuma ya Kamo hannunta ya maida kofar ya rufe ya shigo falon still jaye da hannunta

"daddy ka ganshi? Daddy sun dawo? Are they ok?" abinda take fada kenan tana Binshi har suka qaraso wajen wata kujera mai daukar mutum biyu ya zaunar daita.



"daddy ya akayi ka dade? Sun dawo ne? Nasan sun dawo ko?"


"shhh ya isa hakannan sweetheart kinji? Ya isa, now shaqi numfashi..."


Shaqa tayi yadda yace


"to fesar... Yauwa to qara Shaqa... To fesar...

Yauwa daughter na, ki daina magana babu ko sayawa numfashi kinji, it's not Good for the health"


"daddy... Deen" yadda tayi maganar yasa yaji jikinshi yayi sanyi sosai


"daddy please say something, ka gansu ko?" taqara fada tana kallonshi da gajiyayyun idanunta wadanda sukayi jaa sosai bawai don kuka ba sai don tashin hankali da rashin isashen barci



Cupping fuskarta daddy yayi a hannunshi Hakan yasa zee zubamashi idanu itama tana kallonshi


"dear, please calm down, banaso kina tada hankalinki"


Tunda yafara maganar tashiga Kada kai yana gamawa tace
"to daddy, to nabari, please tell me, where is he?"


Tausayinta yasake lullu6e daddy ganin kamar ma ba'a hayyacinta take ba.


Dagowa yayi ya kalli mummy da itama saukowarta kenan ta tsaya daidai bakin stairs itama tana kallonsu.


Maida kallonta yayi akan Zainab din daketa kallonshi itama tama kasa hadiye miyau don fargaba


Sake Cupping din fuskarta yayi ahankali sannan yace
"Zainab karki tashi hankalinki kinji? Please"


Banda Kada kai babu abinda takeyi cikin sauri tana kallonshi

"dear haryanzu basu dawo ba, gidan arufe da padlock kuma babu wanda yasan inda suka tafi da lokacin da suka tafi kawai wayan gari sukayi sukaga babu su a gidan, har mai gidan daya basu haya Saida aka hada ni dashi amma shima cewa yayi besan komai gameda tafiyarsu ba don bawai kudinsu ne yaqare ba Suna da kingin kudi harna wata 3 a wajenshi.


Abin dai da daure kai, bansaniba qila travelling sukayi garinsu ko something like that"



_wow! I love travelling!_


_nima zanso watarana nayi tafiya wani wuri_


Tunawa tayi da maganarsu ta kwanaki

To amma ina zasu tafi yanzu ana school, lokacin da ma exams keta matsowa?



"Daddy please ina zuwa, nima zanje nagani" tafada pleadingly

"Me zaki gani?" inji daddy

"gidan nasu, please bazan samu rest of mind ba idan ban gani ba"


"kina hauka ne?! Ina kika ta6a ganin anyi haka? Ace saurayi ya turo magabatanshi yaqi turowa kuma don rashin sanin ciwon kai sai budurwar tabi shi har gida?" inji mummy tana qarasowa dakin


Sadda kanta zee kawai tayi qasa not saying anything Saidai ita kadai tasan abinda zuciyarta keyimata


"kawai a kyalesu aga iya gudun ruwansu, ai zasu dawo kuma am betting you zasu zo har nan su fadamana komai" inji mummyn tana zama itama kan kujerar kusa dasu


Ganin yanayin zee yasa daddy cewa
"tashi ki shirya mutafi"

Saurin dagowa zee tayi ta kalleshi trying to believe what she heard

"haba Alhaji, ya zakace haka kuma?" inji mummy


"maimuna kinsan condition din yarinyar nan tunda dake akayi mana bayani, why zan bari najama kaina bala'i? Idan zuwan zai saka hankalinta ya kwanta, fine"


"to amma saboda allah Alhaji wannan ai xubar da qima ne"


Kallon zee da murnarta tafara komawa ciki daddy yayi yace
"jeki shirya ki sauko mutafi"


Aikau kamar akan qaya take dama tayi saurin miqewa ta wuce sama da sauri


Daddy ne ya kalli mummy
"please maimuna kabari taje tagani for herself, Hakan zaisa hankalinta kwanciya"



"amma Alhaji idan kukaje akayi daidaitoni sun dawo fa? Sai kawai suga kunje nemansu, suruki da budurwar da za'azo neman aurenta aka fasa sun biyo saurayi har gida? Wannan ai xubar da mutunci ne"


Dan murmushi daddy yayi sannan yace
"ni lafiyar diyata ta fiyemin komai, ina iyayin fiyeda Hakan ma saboda ita"


Daidai nan zee ta sauko daga sama ta chanza kayan jikinta zuwa blue black jallabiya


Tashi daddy yayi shima ya miqo mata hannu ta taho ta kama hannun tana avoiding idanun mummy


Tasan abinda takeyi ba girmanta bane kuma ba ajinta bane amma ya ta iya?


Abinda zuciyarta ke ingixata tayi kenan kuma a halin yanzu batada wani za6i sai na bin umarnin zuciyar tata don kwata2 a wannan fannin bata iya controlling dinta.


Ficewa sukayi daga falon mummy na binsu da kallo.


Parking space daddy ya nufa riqe da hannunta Hakan yasa bala dake can wajen security rugowa da gudu ya rigasu isa motar ya bude masu backseat.


Da daddy yaso yayi driving din sai kuma yafasa ganin balan duk sai suka shige backseat din ya rufo musu kofar sannan shima ya zagaya mazaunin driver ya bude yashiga.


Tada motar yayi sannan yayi reverse ya kama hanyar gate din da security yariga ya wangale musu suka fice daga gidan.




Tafe suke cikin normal speed motar tayi tsit bakajin komai sai alamun tana tafiya da zakaji


Zee a bangarenta a matuqar darare take, a qagare take su iso unguwar dukda yadda zuciyarta ke qara gudun bugu duk kusancinsu da unguwarsu Deen din.


Daddy daya lura da uneasiness dinta ya damqe hannunta acikin nashi Hakan yasa ta juyo ta kalleshi


Kada mata kai yayi alamun ta kwantar da hankalinta


Dry murmushi tadan yimashi tareda Kada mashi kai shima ta Janye idanunta ta maida kan glass din gefenta.



Basu qara jimawa suna tafiya ba suka qaraso unguwar tasu.


Bugun da zuciyarta keyi sai ya linka na dazu


Tanaji bala ya sauko daga motar sannan ya zagayo ya bude masu

Daddy shi yafara fita sannan ya miqo mata hannu.


Cikin sanyi itama ta miqa hannun nata ta kama nashi sannan tafito da taimakonshi.


Ganin Hakan yasa bala maida kofar ya rufe ya matsa gefe.


Dagowa zee tayi ta kalli kofar gidansu Deen din wanda kamar yadda masu zuwan ke fadi rufe take da qaton kwado


Qurawa kofar idanu tayi ko kyaftawa babu tana jin yadda zuciyarta ke bugawa sosai


"basu nan, tun wancan jiya din muma munzo siyan koko basunan" suka tsinkayi muryar yar yarinya tana fadin haka


Duk juyowa sukayi suka kalleta Hakan yasa yarinyar tasha jinin jikinta

Kafin wani cikinsu yayi magana harta juya ta arta a guje.


Binta da kallo duk sukayi ahakan sukaji muryar wani mutum nacewa

"A'a Alhaji, sake dawowa kayi?"


Sake juyowa sukayi kan mutumin (mallam Nasiru) daddy yace
"wlh kau ka ganmu munsake dawowa? Dawowa mukayi muga ko za'a dace da sun dawo"


"wlh kau Alhaji kaga dai basu dawo ba, abin da matuqar daure kai don wlh ranar daren da zamu wayi gari muga gidan a kulle tareda Deen din muka fito daga massalaci bayan sallar isha'i kuma Koda wasa be gayamin zasuyi tafiya ba bare inda zasu din abinda basu ta6a yiba don wlh kamar yan uwan juna haka muke komai namu sun sani suma haka, bansan ya akayi ba wannan karon" inji mallam Nasiru


"to ko wajen wasu danginsu suka je ko yan uwa haka? Kasan inda wasu nasu haka suke?" inji daddy


Girgiza kai mallam Nasiru yayi
"Gaskiya A'a don tun Zuwansu nan unguwar duk kusancinmu bata ta6a nuna mana wani nasu ba ko yan uwansu bare akai ga maganar inda suke kuma bamu ta6a ganin wasu nasu sun kawo masu ziyara ba"


Shiru wajen ya dan dauka

"to sun kai shekaru nawa da dawowa nan?" inji daddy


"Ca6! Gaskiya sun dade sosai don aqalla sunkai shekaru goma sha biyu a nan lokacin tun banma dade da aure ba"

"kuma ace duk lokacin babu wani nasu daya ta6a zuwa masu?" inji daddy cikin alhini


"to banace ba Alhaji tunda qila suna zuwa ko su sukan je mune bamu sani ba Amma dai bata ta6a gwadamana wani ko wata a matsayin yan uwansu ba"


Daidai nan wani saurayi ya qaraso wajen yana masu sallama


Duk juyowa sukayi wajenshi suna amsa sallamar

"A'a salmanu kaine?" inji mallam Nasiru

Cikin murmushi ya amsa da eh sannan yashiga gaidasu sukuma suna amsawa


"dama yanzu ina gida zan fita qanwata rahma tashigo gida aguje wai ga wasu masu mota can kofar gidansu Deen shine nace bari nazo qila kune wadanda nake nema"


Duk maida hankalinsu sukayi akanshi gabadaya


Kallon zee salmanu yayi yace
"kece Zainab?"


Gaban zee ne ya fadi

Kasa amsawa zee tayi sai kallon daddy datayi tasake maido kallonta akan salmanun


"eh itace dan samari, fatan dai lfy?" inji daddy


"eh lafiya lau, dama Deen ne yabani saqo wai idan wata Zainab tazo inbata"


Gaban zee yaqara yankewa ya fadi tanajin zuciyarta na qara speed


Karkatawa yayi ya zura hannu aljihu yana cewa
"wlh ranar talata da daddare yabani bayan mun fito daga massalaci wai don Allah wata Zainab zatazo wai inbata dana tambayeshi shi me zai hana yabata sai cewa yayi ai tana iya zuwa shikuma a lokacin yatafi school gashi saqon nada matuqar muhinmmanci bazai yiwu taje ta dawo ba

To tun lokacin na amsa sai kuma aka wayi gari gidansu a kulle.

Haka na wuni ranar ko aiki banje ba don gudun kar natafi yarinyar kuma tazo gashi yace saqon nada matuqar muhinmmanci, to amma shiru har dare banga wulgin kowa anan ba

To shine naketa ajiya kuma ina dan zagayowa ina kuma sa qannena suna dubamin ko wata zatazo nemanshi.

To yanzu ma na dawo gida ne naci abinci ina shirin fita rahma tashigo aguje wai ga wasu masu mota can kofar gidansu Deen shine nace bari nazo nagani ko za'a dace" ya qarashe zancen yana Miqama zee wani brown envelope daya zaro daga aljihun wandonshi

"ki duba kigani ko naki dinne" yafada yana sake miqa mata


Kasa amsa tayi sai kafe envelope din datayi da idanu Tanajin kamar zuciyarta zata faso qirji saboda bugu


"dear ki amsa ki duba" inji daddy cikin sanya qwarin gwiwa


Kallon daddyn tayi sannan taqara kallon wasiqar, sannan ahankali ta dago hannunta dake rawa rawa ta amshi envelope din.

Jujjuya envelope din take a hannunta tana fargabar budewa

Dafa kafadarta daddy yayi Hakan yasa taqara Dagowa ta kalleshi

Kada mata kai yayi cikin qarfafa gwiwa Hakan yasa ta sauke wata nannauyar Ajiyar zuciya sannan ahankali hannu na rawa ta farke envelope din taga wata ninkakkiyar farar takarda ta bayyana


Gabanta ne yasake tsinkewa

Duk ita mutanen wajen suka zubama ido in curiosity suma


Zare takarda tayi tasaki yagaggen envelope din aqasa


Ahankali ta shiga warware takardar hannunta hannunta na rawa, zuciyarta na rawa kai komai ma nata rawa yakeyi da za'a auna jininta a lokacin da ta tabbatar da za'a ga yakai maqurar hawa.


Unique handwriting din da shikadai tasani dashi yafara yima idanuwanta maraba


Ahankali tafara bin abinda yake cikin takardar tana karantawa


_*Nasan lokacin da wannan takardar zatazo miki na riga nayi nisa.*_


_*Bansan me zance maki ba, bansan ta ina zanfara ba, bansan da wadanne kalamai zanyi amfani dasu ba*_

_*daren ranar danake rubuta wannan takardar shine mafarin duhun rayuwata, Koda gari ya waye wa kowa ni bazai waye min ba, ba yanzu ba kuma bana jin lokacin zai ta6a zuwa*_


_*zan cigaba da kasancewa a duhun ne qila har ahada, Domin nariga nayi nisa da hasken dazai haskaka min rayuwata*_


_*ina sonki*_

_*nasan yanzu ba lallai bane ki yarda da Hakan ba kuma nima ban cancanci na fadamiki Hakan ba*_


_*amma that's the pure truth.. Ina sonki, zan cigaba da sonki, wataqila ma sonki ne ajali na*_


_*am sorry... For every thing.. Da abubbuwan danasaki fuskanta da wanda zan saki fuskanta*_


_*kin dauki zuciyarki dunqullala kin bani amana nikuma na raratsata ta zuba a plate na maido miki*_


_*ban cancanci yafiyarki ba zee, ban cancanci gafararki ba Amma Hakan bazai hanani neman gafararki ba*_


_*ki yafemin Zainab... Don Allah.. Ba don niba.. Don girman allahπŸ‘πŸ˜­*_


_*natafi.. Am gone.. Maybe forever maybe not*_


_*I LOVE YOU*_



Ahankali takardar ta sulale daga hannunta

"daughter!!" taji muryar daddy na cewa haka da qarfi sai kuma taji an riqota gamm


"innallilahi waina ilaihi rajiun! Zainab! Ki bude idanunki ki kalleni, please don't do this" tasake jin muryar daddy sama sama ana dan bubbuga mata kumatu

Amma the more takeson bude idanun the more yake qara rufewa

"Zainab!! Innallilahi waina ilaihi rajiun! Jama'a ku taimaka min! Zainab!!"


"DEEN..."

Kalmarta ta qarshe kenan idanun suka rufe ruff... ✍️




Ummin fasihu πŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:39 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEEN πŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*







*052*






*HEARTBREAK πŸ’”*




_jiya kasa yiwa kowa reply nayi_


_Everyone is saying why? Why? Why?_


_that's destiny kuma komai yanada reason na faruwarshi kuma idan akasa hqr ahankali ahankali komai zai warware_

_dama tun farko nariga na fada cewa wannan story din ya qumshi, true love, heartbreak da sadaukarwa. Don haka sai kuyi hqr don yanzu muka fara zuwa inda na dade inason muzo, insha allah komai zai warware and Gaskiya zatayi halinta sooner or later_

_sorry for the heartbreak 😞_

_Hajiya am'ash mai jiran sai komai ya warware sannan ta cigaba da karatu, comgratulations, qila sai munzo semi-final zakiyi joining dinmu πŸ˜†_






Dagudu security din gate din asibitin ya qarasa gate din ya shiga wangale masu gate din.


A tsiyace motar tashigo harabar asibitin, maimakon tayi parking space sai tayi hanyar entrance din hospital din ta tsaya few feet da tudunkar entrance din.


Already su likitoci da nurses duk sun fito nurses din riqe da dan gadon nan na gurgura marassa lafiya


Kofar baya aka bude sannan daddy yafara qoqarin tattarota ya dauketa amma yakasa saboda rawar da jikinshi yakeyi


Ganin Hakan yasa su likitoci matsowa suma da taimakonsu aka fiddo zee da komai nata yasaki kamar gawa don idan bama lura kayi ba sai kace ma bata numfashi kwata2


Akan gadon aka dorata sannan duk aka shiga turata dagudu aka nufi cikin hospital din






Duk inda suka wuce sai mutanen dake kai kawo wajen sun tsaya suna kallonsu don ganin yadda ake gurguro gadon da mutanen dake Binshi dagudu ya isa ya nuna cewa koma wa ke saman gadon yana cikin very critical condition.


Emergency room suka nufa, tun kafin su qaraso aka bude masu kofa kuma suna shiga aka rufo kofar wanda Hakan yasa su daddy da bala jan burki bakin kofar.


Dafe kanshi daddy yayi ya juya yashiga yin safa da marwa cikin mugun tashin hankali.


Shima bala was restless, shima tashin hankaline rubuce koina a fuskarshi.



Acan kau a wani daki aka shigar daita akayi transferring dinta daga gadon mai taya zuwa na cikin dakin.


Nan take likitocin guda uku suka rufa akanta suka fara baje basirarsu wajen ganin sun shawo kan matsalar


Na farko numfashinta dayayi mugun qasa suka shiga qoqarin jawoshi su daidaitashi.


Sosai suke aikin babu kama hannun yaro suna iya bakin qoqarinsu na ganin sunyi saving life dinta don ahalin yanzu tana cikin very critical condition.





Daddy kau kasa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login