Showing 270001 words to 273000 words out of 322641 words

Chapter 91 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6129

one after the other

mutane biyu Kawai ya iya shaidawa acikinsu, daddy da mummy

yarasa meke faruwa, meyasa yake gane gane, wane irin mafarki ne wannan harmutsatse?

dafarko yaga Zainab, macen da yasan qila harya mutu bazai qara ganinta ba

yazo kuma yaga wani mai irin kammaninshi sak yadda kasan kanshi yake kallo a madubi

yanzu kuma mummy da daddy wadanda shidai a Nigeria yasansu, to meke faruwa ne? wannan wane irin birkittacen mafarki ne mai dogon zango? yaushe zai farka? yakamata mafarkinnan yaqare hakanan tunkafin kwalwarshi tayi bursting

suma shi suke kallo cikin tausayawa halin dayake aciki don kallo daya zaka mashi kasan tsabar taurin rai ne Kawai yakeyi

mammaki ma suke yadda shi ya iya jurewa be suma ba, idanma sumar ne aishi ya cancanci yayita tunda shi kwata2 besan komai ba, everything just came at sudden ne, besan yanada yan uwa ba, besan shi twin bane, besan yanada iyaye bayan wadanda yasan sun rasu ba sa6anin su Mussadiq dasuka san dashi

maida kallonshi akan habeeb dake kallonshi

yasan mafarki be dakatuwa harsai yaqare amma bazai iya dauka ba kuma soyake ya farka ko ya bar wannan page din na mafarkin

ahankali ya matsa kusada habeeb yakama hannunshi yariqe gamm yana kallonshi

"habeeb ka fiddani daga nan, ka kaini wajen kaka"
shike maganar amma saiyaji kamar bashi ke motsa bakin ba, ganin komai yake amafarki

shiru habeeb yayi yana kallonshi yama rasa Abinda zaice mashi

"habeeb wani irin mafarki nakeyi, don allah ka tasheni ko ka fiddani daga nan" tasake fada yana Jin kanshi soo empty

wani irin tausayinshi ya tsirgama mutanen wajen suna kallonshi cikeda tausayawa

"nima mafarkin nake Balarabe, wai ka rabe gida biyu" inji habeeb cikin yin qasa da murya, kallo daya zakamasu kasan they're totally confused


"nima, nima naganni agabana, gani tsaye gakuma wani nidin agabana, kuma.. kuma naga Zainab.. Zainab dita, mubar nan habeeb... kwalwata zata fashe"


"Kamal" muryar mummy ta katseshi

juyowa sukayi suna kallonta babu ko kyaftawa harta qaraso gabansu

idanunta sun duri ruwa sosai tausayinshi ke tsuma zuciyarta

"Kamal ba mafarki ba kake, this is real"tafada tenderly


kallonta yakeyi Babu ko kyaftawa

"mummy?" yafada ahankali kamar maison jingina dagaske ita dince

kada mashi kai tayi hawayenta na gangarowa

"eh son, mummy ce. mummyn Zainab. it's real...taho taho ka zauna" tafada tana jan hannunshi tanufi kujera

binta yashigayi kamar rakumi da akala har ta zaunar dashi sai binta da ido yake

"Kamal this is real, ba mafarki bane, nice.. mummyn Zainab, wancan kuma daddy, ka tuna? kuma dagaske kaga Zainab kuma dagaske ku biyu ne masu irin kammaninka, kai tagwaye ne"

kafeta yayi Kawai da idanunshi yana kallonta confused

"iyayenka basu rasu ba, mahaifinka ne Kawai yarasu amma mahaifiyarka nanan, tana nan da ranta, wancan kuma twin dinka ne, kaine Hassan shine Hussain, bayanshi kuma kanada qanwa Aysha duk suna nan Dubai ne, kaima saceka akayi tun kana qarami aka kaika Nigeria amma kai ba dan Nigeria bane, kai Balarabe ne, Dan saudia, mahaifinka mutumin saudiya ne mahaifiyarka kuma yar misra, Kaka ba kakarka bace bakada alaqa daita, ga danginka nan suna nan, saceka akayi.."

kuka ne yaci qarfin mummy tashigayi da dukkanin zuciyarta

bama ita kadai ba babu wanda babu kwalla a idanunshi idan ka cire Deen daketa kallon bakin mummy tunda tafara magana

cikin kuka mummy tace
"Deen ba sunanka Kamaldeen ba sunanka Mujaheed.. Mujaheed Al-hassan shikuma twin dinka Mussadiq Al-hassan, kai Balarabe cikkaken Balarabe ne Kamal"


batool datakasa jurewa ta rungume umman Ahmad dake kusada ita batareda tasani ba ta cigaba da rusa kukanta kamar ranta zai fita

"eh Deen, kai asalinka Balaraben saudiya ne, duk acan mahaifanka suke, acan aka haifeka dakai da Dan uwanka Mussadiq saidai shekararka uku aka saceka aka kasheka ashe baka mutu ba, qila Kawai wucewa dakai akayi aka nuna an kasheka saigashi ankaika Nigeria. mahaifinka yarasu amma mahaifiyarka nanan tana cikin garin nan yanzu haka" inji Abbu shima cikin kwantar da murya

bin Abbu shima Deen yake da ido Kawai becewa komai Kawai kallon motsin bakinshi yakeyi

"daga baya muka gane hakan, wannan dalilin yasa muka quduri aniyar hadaka da danginka, shine ma dalilin zuwanmu Nigeria lokacin daka fara ganinmu, babu wani aikin daya kaimu, kai ka kaimu Deen kuma bawai saboda aiki yasa muka gayyatoka nan ba mun gayyatoka ne don hadaka da ahalinka da bakasan dasu ba" inji Ahmad da shima idanunshi suka rine

aymaan sai kallon Deen yake shima da jajjayen idanunshi yakasa cewa komai

saida Deen yagama sauraronsu tsab sannan ya maida kallonshi kan mummy da har lokacin hawayen idanunta sukaqi tsayawa

"Kaka..." yafada ahankali kamar mai rad'a

"ku kaini wajen Kaka don allah" yafada yana kallonsu cikin wani yanayi

hawayen mutanen yakasa tsayawa ganin yadda yake magana so confused kamar dan shekara biyun daya 6ata tsakiyar hanya yana gantali

Abbu zaiyi magana aymaan ya katseshi

"No Abbu.. zaku fasamashi kwalwa, don't stress his brain futher, yana buqatar hutu, idan kuka takura za'a samu matsala"

saikuma ya kalli Deen

"kanason zuwa wajen Kaka?"

saurin kadamashi kai Deen yayi kamar qaramin yaro

"taso to, taso nakaika" yafada yana miqamashi hannu

Dan tsayawa yayi yana kallonshi saikuma ya miqamashi hannu ya tadashi aymaan yayi gaba jaye da hannunshi suka fice daga wajen

wani kukan batool taqara rushewa dashi, bama ita kadai ba harda sauran matan dakin, mazan nema masu dan tauri taurin rai iyakarsu hawaye kowa jikinshi yayi sanyi lakwas

jikin daddy yafi nakowa yin sanyi, ganin Deen a irin wannan yanayin ba qaramin sanyayamashi jiki yayi ba, yarasa Inda zai tsoma ranshi yaji sanyi


habeeb dai haryanzu bece komai ba saidai alamu sun nuna shi ya gamsu da bayyanansu don they make sense to him don shima yadade yana zargin Deen ba bahaushe bane, komai nashi sak na larabawa dukda hasken fatarshi ba irin fauu dinnan bane irin na kajin jikin kajin turawa amma dai daka ganshi kaga ruwan Arab


haka suka zauna jigum har aymaan yadawo

duk dagowa sukayi suka kalleshi

"anyi mishi allurar barci to settle his brain" Abinda Kawai ya iya fadamasu kenan

duk Ajiyar zuciya suka sauke kowa najin zuciyarshi da ruhinshi badadi


daga baya ne suka yanke shawarar yakamata wasu sukoma gida wajensu ummy


Abbu da umman Ahmad da abban Ahmad suka tafi sukabar mummy, daddy, batool data maqale sai aymaan da Ahmad suka kwana a asibitin.




πŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œπŸ’œ






ahankali yafara bude idanunshi dasukayi mashi mugun nauyi

dafarko biji biji yafara gani kafin daga baya ganinshi yafara yin clear


ahankali yake bin dakin da kallo cikin son tuna inane wajen

shikadai ne kwance adakin, ganin yanayin dakin yasashi gane a asibiti yake

ahankali yakai hannu yadafa kanshi dake mishi ciwo

ahaka yasamu ya lalla6a yamiqe zaune

cigaba da bin dakin yake da kallo cikin son tuno Abinda yafaru

ahankali abubbuwan dasuka faru jiya suka shiga dawomashi tiryan2

shiru yayi confused, abin tambaya anan shine dukkan wadannan abubbuwan mafarkine ko dagaske yafaru, idan mafarkine meya kawoshi asibiti harya kwanta?


yana cikin wannan saqe saqen aka bude kofa aka shigo

dagowa yayi ya kalli kofar sai suka hada idanu da mummy

wani sanyayyan murmushi ta sakarmashi tana qarasowa ciki nan kingin mutanen suka ida shigowa

da daddaya yake binsu da kallo yaga duk mutanen jiya ne, kenan hakan na nufin ba mafarki ba yake?

"sannu.. ya jikin?" inji mummy tana masa murmushi tenderly

shima murmushinshi yayimata asanyaye sannan ahankali yace
"alhamdulillah"

aymaan ne yashigo Ahmad biye dashi sai habeeb abayansu

duk da idanu yabisu yana tuna every bit of conversation dinsu na jiya

saurin qarasowa wajenshi habeeb yayi cikin murnar ganin ya farka

"Balarabe" yafada yana kallonshi

Dan murmushi Deen yayimashi shima yana kallonshi

"ya jikin?" ya tambaya

"alhamdulillah" ya amsa mashi shima asanyaye


qarasowa aymaan yayi wajenshi shima

"sannu..akwai Abinda ke damunka ko kemaka ciwo"

ahankali ya girgiza kai
"No, just a slight headache"

"sannu.. zai daina insha allah..mummy adan bashi wani abu" inji aymaan


da to mummy ta amsa nan da tashiga hadamashi tea

duk shi suke kallo kamar t.v harta gama hadawa tabashi

amsa yayi yana godiya sannan yafara sha

yasha sosai sannan ya ajiye, nan ya buqaci yin sallah

habeeb ya rakashi bakin toilet yayi alwala yafito sannan yahau sallayar da har an shimfidamashi ya rama sallar asuba don lokacin har gari yawaye don takwas ma tawuce


duk fita sukayi lokacin dazaiyi sallar yarage saura habeeb Kawai da Ahmad

yana nan zaune ya idar da sallar aka bude kofar

atare duk suka dago suka kalli kofar don ganin mai shigowa

Aysha ce tsaye abakin kofar batool abayanta

hada idanu sukayi da Deen dake kan sallaya har lokacin

kafe juna sukayi da idanu yayinda bugun zuciyoyinsu ya tsananta

ahankali hawaye suka taru a kumburrarun idanun Aysha tana kallon yayan nata dasu

shima dai Deen kallonta Kawai yakeyi yana Jin wani feeling na alaqa mai qarfi gameda ita a zuciya da gangan jikinshi


"come in Aysha, come in and say hi to your brother" inji Ahmad dake kallonsu

dagowa tayi ta kalli Ahmad saikuma tasake kallon Deen dashima ita yake kallo har lokacin

dafa mata kafada batool tayi cikin qarfafa gwiwa hakan yasa Aysha fara takawa kamar wadda kwai ya fashemawa aciki ta nufi Inda Deen yake tana kallonshi

saida ta qaraso gabanshi ta tsaya suna kallon juna saikuma tayi qasa ta durqusa cikin daidaita tsayinsu tana kallonshi still

sake kafe juna da idanu sukayi na wani lokaci

ahankali Deen yasakarmata guntun murmushi

bin dimple din tsakiyar gemunshi Aysha tayi da kallo babu kyaftawa

"what's your name?" yafada ahankali

dagowa tayi tana kallon eyeball dinshi

"A..Aysha" tafada cikin rawar murya hawayen idanunta na gangarowa

"meyasa kike kuka?" ya tambayeta da harshen turanci

saurin goge hawayen tayi tana girgiza kai
"n..na daina" tafada cikin muryarta dake a disashe

murmushi yayi shima idanunshi na chanza launi

miqomata hannu yayi

kallon hannun tayi saikuma ta dago hannunta ahankali tasaka acikin nashi ya riqe gamm wani feeling na jini na yawo ajikinsu

"dagaske ke qanwata ce?" ya tambaya ahankali yana kallonta

wasu hawayen suka gangaromata tana kadamashi kai dasauri

"dagaske ni twin ne kuma... kuma inada Mama?"

fadawa jikinshi tayi cikin kasa jurewa tafashe da kuka mai ta6a zuciya

"eh yaya.. kanada Mama..mai sonka, tana sonka sosai yaya..muma muna sonka yaya.. bamu ta6a mantaka ba daidai da second daya ba tun tafiyarka, meyasa katafi kabarmu?.. meyasa kabarmu da kewarka yaya? karka qara tafiya yaya.. karka qara barinmu.. muna sonka yaya"

kuka take sosai koina na ilahirin jikinta banda rawa babu Abinda takeyi, ta qanqameshi sai sheshekar kuka takeyi

ahankali Deen yasa hannu ya zagayo bayanta ya rungumeta shima batareda ya iya cewa komai ba sai sauraron bugun zuciyoyinsu

abin haryanzu bebar yimashi kama da mafarki ba, wai shikeda family, shikeda qanwa, shikeda mahaifiya

lumshe idanu yayi yana sauraron sautin kukan Aysha yana Jin yadda kukan ke ta6amashi zuciya

ahankali yaqara bude baki yace
"stop crying.. please"

kamar cewa yayi taqara saita qara rushewa da kuka tana qara cusa fuskarta a qirjinshi

Ajiyar zuciya ya sauke sannan yabude jajjayen idanunshi ahankali

"am here now, I promise bazan sake tafiya ba" ya tsinci kanshi da fadin haka

qara fashewa da kuka Aysha tayi tana qara qanqameshi kamar zata shige jikinshi

shima qara rungumeta yayi zuciyarshi na melting

babu wanda zuciyarshi bata motsa ba don masu saurin kuka irinsu batool harsun bude shafi

kamar ance yadago sai suka hada idanu da Mussadiq dake tsaye bakin kofa yana kallonsu

kafe juna da kallo sukayi kamar sunsamu t.v

shima Mussadiq idanunshi sunyi jajur sun dan kumbura harda lips dinshi

yanzu babu coat ajikinshi sai t-shirt din ciki kamar dai Deen

ahankali Deen yadaga Aysha daga jikinshi idanunshi still akan Mussadiq

komawa gefe Aysha tayi tana kallon yayyen nata biyu tana hawaye

cigaba da kallon juna sukeyi babu mai ko kyaftawa

ahankali Deen ya dago hannunshi ya miqoma Mussadiq

binshi da kallo Mussadiq ya cigaba dayi batareda ya motsa ba

kowa na dakin shi yake kallo yaga me zaiyi

Deen be sauke hannunshi ba kuma be janye idanunshi daga kanshi ba

ahankali Mussadiq yashiga takowa yana tunkaro Deen harya qaraso gabanshi

kallon hannun da Deen ke miqomashi yayi yana tuna kalamansu daddy

*Mujaheed be mutu ba, yana raye kuma yadawo gareku*


maida kallonshi yayi akan fuskar Deen yana kallo sannan ahankali kamar wanda ake controlling da remote yadago hannunshi ya dora akan na Deen

wani irin electric feeling ya tsirgamasu gabadaya ilahirin jikinsu

zubewa Mussadiq yayi on his knees the next minute sai gani mutanen dakin sukayi sun qanqame juna cikin wata iriyar wawiyar runguma


"Mujaheed.." Mussadiq yafada cikin wata iriyar murya kamar ba tashi ba


"Mussadiq.." inji Deen shima cikin rawar murya

wasu hawaye masu zafin gaske suka gangaromasu alokaci daya suna qara qanqame juna


"Mujaheed..😭"



"Mussadiq😭"...✍�




Ummin FasihuπŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEENπŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*












*085*







*THE REUNION*





sun jima ahakan rungume dajuna kamar zasu shige jikin juna, feeling dasukeji yana tasomasu daga zuciya zuwa ilahirin jikinsu is unexplainable


ahankali suka raba jikinsu dana juna suka hade goshinsu waje guda kowanne na mayar da numfashi

dago wet eyes dinsu sukayi atare suna kallon juna batareda sun iya cewa komai ba

"I thought you're gone..forever" inji Mussadiq cikin muryar rad'a daidai wasu hawayen naqara gangarowa daga idanunshi

kasa cewa komai Deen yayi sai hannu daya daga yayi cupping fuskarshi

"the memory is still fresh Mujaheed.. nakasa mantawa..lokacin..,lokacin dasuka sakaka amota suka tafi, nan kadai nake iya riqewa.. nasan ya isa na manta saboda dadewa da shudewar shekaru.. amma nakasa.. nakasa
kullum sai wannan scene din yazomin a mafarki.. kullum sainayi mafarkinka da yadda aka rabamu..." in between kuka Mussadiq ke wannan maganar

"ashe zaka dawo? ashe zanqara ganinka?.. kasan yadda rabuwarmu tayi affecting dina? kasan yadda rayuwata ta chanza bayan tafiyarka?"

shidai Deen kallon yadda yake kuka sosai yake shima hawayenshi naqin tsayawa, besan meyake magana akai ba don shi betuna komai ba amma kalamanshi ba qaramin ta6amashi zuciya suke ba bare yadda yaga yana kuka sosai kukan da kallo daya zakayimashi kasan daga qasan zuciya yake tahowa

shima Mussadiq grabbing fuskar Deen yayi

"ina kashiga all these years? meyasa katafi kabarmu? karka qara wannan gangancin kaji? if you do I'll kill you" yafada yana riqe fuskar Deen sosai

murmushi suka saki atare suka sake rungume juna

"I won't, I promise" inji Deen yana qara rungume Mussadiq

Aysha dake gefe itama ta rarrafo wajensu ta rungumo bayansu

atare suka dago suka kalleta da wet eyes dinsu sai suka sakarmata murmushi suka sake rungume juna su ukun suka hade kansu waje guda


kowa na dakin share hawayen farinciki yake kowa murmushi a fuskarshi mai nuna farinciki dasuke ta
ya wadannan bayin allahn


sun dade ahakan sannan suka saki juna kowanne murmushi afuskarshi

sai a lokacin suka lurada yadda mutanen dakin suka qara yawa don harda su mummy adakin

da kallo duk suka bisu suna kallon yadda suke masu murmushi kowanne farincikinshi yakasa 6oyuwa

suma murmushin suka maida masu atare fuskarsu na nuna how grateful they are

kafin wani yayi magana acikinsu wani Dr yashigo dakin riqeda waya

sallama yayi sannan yace
"wannan wayar tunjiya ake kiranta, a dayan dakin muka tsinceta"

duk kallon wayar sukayi

"akhie, your phone" inji Aysha

Jin hakan yasa Mussadiq miqa hannunshi Dr din yabashi, saida yayimashi alamun thank you da ido sannan ya maida hankalinshi akan wayar, lokacin harta tsinke

wani murmushi yayi sannan yadago yakalli Deen dake kallonshi

"it's ummie" yafada yana nunamashi screen din wayar

gaban Deen yafadi saidai bece komai ba sai cigaba da binshi da kallo dayayi ganin yana re-dialing number

handsfree yasa shiyasa kowa na dakin kejin sautin ringing din alamun tashiga

bugu uku tayi aka daga

cikin wata kamillaliyar murya mai sirki da yanayin damuwa akayi sallama ta dayan bangaren

gaban Deen yasake yankewa lokacin da muryar tadaki kunnenshi sai kallon wayar yakeyi kamar yana hango mai maganar ta cikinta

amsa sallamar Mussadiq yayi cikin wata murya mai cikeda annushuwa yana gaidata da harshen larabci

bema ida gaisuwarba ta katseshi itama cikin harshen larabci da
"Mussadiq ina kake? dama kabaro Australia? nayita kiran numberka tacan bana samu, yaushe kadawo? kuma kasan jiya Aysha bata dawo ba? gidan wannan qawar tata taje birthday dinta tun yamma amma haryanzu bata dawoba gashi wayarta bata shiga, ina cikin damuwa sosai Mussadiq gashi kaima naita kiranka baka dagawa"

tun sadda tafara magana Mussadiq keta murmushi yana kallon yanayin fuskar Deen dayayi kasaqe yana sauraron yaren da ummie keyi, yasan larabci ne amma besan metake cewa ba don bayaji kwata2 sai dan wanda ba'a rasaba wanda suke dan tsinta a islamiyya

kallon wayar Kawai yakeyi yabata dukkan hankalinshi yana sauraron muryar da akecewa ta uwarshi ce

dafa kafadarshi Mussadiq yayi still yana murmushi sannan ya amsa ma ummie

"ummie muna tare daita" yafada yana kallon Aysha dake sauraronsu itama

"kuna tare? yaushe kadawo harkuka hade?" inji ummie adayan 6angaren a mammakince

"jiya.. karki damu gamunan zamu taho yanzu and guess what" yafada yana kallon Deen

"what" inji ummie

"zamu tahomaki da wani Abinda bazaki ta6a mantawa ba" yafada yana kallon Deen yana murmushi

"menene abin?" inji ummie

"sai munzo Kawai, gamunan"
daga haka saiya katse kiran

dagowa yayi ya kalli Deen daya maidashi t.v tundazu

murmushi yayi mashi
"are you ready to see your ummie?" yafada yana mashi murmushi

gaban Deen ne yaqara faduwa

"I..don't know" yafada ahankali

murmushi duka yan dakin sukayi

"c'mon akhie, just calm down, we'll be there for you and you'll like her I assure you" inji Aysha

kada kai Kawai Deen yayi saidai he's very nervous

zaije ganin wata kuma wai mahaifiyarshi, shida ya girma da tunanin baida mahaifa amma yanzu wai mahaifiyarshi zaije gani, wannan tunanin nasashi Jin wani iri.


tashi Mussadiq yayi yaqarasa gabansu Abbu yana murmushin da ke nuna tsantsar godiya da hallarcin dasukayi masu

cikin turanci yafara magana
"bansan ta ina xanfara ba amma inaso kusani ko za'a tara dukkan kalaman duniyar nan babu wadda zatayi daidai da bayyana maku irin godiyar damuke muku, allah kadai zai iya sakamaku Abinda kukayi mana"

duk murmushi sukayi abbu yace
"mu godewa allah son, allah shine yanufi hakan zai faru, allah shine abin godiya"

dik kada kai kingin sukayi

atare kuma suka furta alhamdulillah cikin tsantsar nuna godiyarsu ga allah subhanahu wata'ala


"zamuje gida, inaso kubiyomu don allah" inji Mussadiq din

yadda yazage yana magana cikin Kasa dakai da fara'a zai baka mammaki kamar ba wannan proud Mussadiq dinba mai ego


"eh to, bazamu ce A'a ba saidai ba dukkanmu zamuje ba, as you can see anan ma bamuda yawa don su daddy sun koma gida dazu saboda wata yar matsalar data taso, so muma munason zuwa can ne amma aymaan da Ahmad suna iya binku, muma lalurace zata hana hakan" inji Abbu

basuji dadin hakan ba amma basuce komai ba

"Ahmad ina aymaan?"

"yana office I guess" inji Ahmad

"to kayimashi magana kace yabiku injini"

"to shikenan Abbu"

"abbu don allah batool tabimu? pleeease?" inji Aysha cikin marairaicewa

kallonta Abbu yayi saikuma ya kalli batool itama ta shagwa6e fuska

"alright then" inji Abbu

dadi sukaji wanda hakan.ya bayyana a fuskarsu

"yanzu bari mu mutafi"

da addu'ar tsari suka bisu suka fice suka bar daga Deen sai Mussadiq, Aysha, batool, Ahmad da habeeb

anan Ahmad yafita don nemo aymaan shikuma Mussadiq yafiddo wayarshi yayi kira

a office dinshi yasameshi tareda Abbu

yanayin dayaga fuskar aymaan yasa yasan maganar me Abbu kemashi

"kajini ko?"

"to Abbu" inji aymaan fuskarshi na bayyana rashin jindadin shi

"to saikun dawo mu muntafi" inji Abbu yana yin hanyar fita

da addu'ar tsari suka bishi harya fita sannan Ahmad yajuyo kan aymaan da ranshi ke a6ace

"meye fa'idar binsu din?" inji aymaan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login