Showing 255001 words to 258000 words out of 322641 words

Chapter 86 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4319

zee tayimata tana gwalemata idanu sannan tayi hanyar sama tana dariya


tana jinta tafashe da kukan shagwa6a tayi wucewarta tana murmushi


kaya tafara ragewa tashige toilet ta watsa saboda zafin da akeyi sannan tafito

tunanin dawowarsu Aymaan kawai takeyi, tunda suka tafi sau daya sukayi waya lokacin data kirashi tayimashi ya hanya a washegarin tafiyarsu daga ranar basu qara waya ba sai taji kamar bata kyautaba takamata taqara kiranshi ko sau daya ne

daga kafadu kawai tayi don aikin gama ya gama tunda harsun taho ma

kaya ta chanza tana tunanin wane tsaraba yayi mata, yace zaimata tsarabar dabazata manta ba, to meye shi? nan ma daga kafadu tayi koma menene ai zata.gani Idan sun iso.


saida tagama shiryawar sannan tafito daga dakin tayi joining ummy a kitchen

itama tayi mammakin ganin girke girken data tadda tanayi, lallai ummy naji da Aymaan, wadannan duk na tarbonshi ne?

saida tafara zuba abincin ranarta taja kujera agefe ta zauna tana ci tana taya ummy da fira, saida tagama sannan itama tazo tayi joining Ummin suka cigaba da shirya girkin tana cewa dole batool tayi kishi wannan irin gara da ake shiryawa Aymaan?

murmushi kawai ummy tayi batace komai ba don batason zee tasan da zuwansu Daddy tafison abin yazomata as surprise.



Sai wajajen magrib suka gama dukkan shirye shiryen nasu suka gyagyara koina gida yaqara extra kyalli, harda batool aka kama wajen aikin bayan tagama kumbure kumburenta saidai every now and then saitayi complaining akan irin uban shirin da akeyi na tarbon Aymaan din.


saida suka gama komai sannan suka haura sama don lokacin har anfara kiraye kirayen sallah


sai wajajen 8 Abbu yafita da mota don zuwa taryarsu a airport, tun a lokacin batool tafara kokwanto anya Aymaan dinne kadai don bataga dalilin dazaisa Abbu yaje tarbonshi ba a airport kamar wani baqo, shiru tayi kawai ta cigaba da zuba ido tana jiran dawowarsu.


suna falo suna kallo suna fira motar Abbu tadawo, ummy ce farkon miqewa kamar wadda aka tsikara tayi waje tana lale lale marhabin


nan take suma su zee suka tashi suka takemata baya don ganin kwam


lokacin dasuka fito har motar tayi parking mutanen ciki sunfara fitowa

kamar a mafarki zee ta hango Mummy tafito daga motar

wara manyan idanunta tayi cikin tsananin mammaki tana bude baki lokacin dataga shima Daddy ya zagayo daga dayan 6aren motar

wani irin ihu tasaki sannan taruga dagudu saitinsu

direct Daddy tanufa tana zuwa ta qaleshi ta maqalqaleshi tana cigaba da ihun murnarta.


dariya sosai kowa nawajen keyi ganin yadda take ihu tana tsalle tsalle kamar yar yarinya


raba jikinsu tayi taqara kallon Daddy kamar mai son tantance eh shi dinne saikuma taqara rungumeshi tana cigaba da ihun murna tana kiran sunanshi

sosai farinciki ya mamaye zuciyar Daddy da bakinshi yaqi rufuwa, ganin diyar tashi yake kamar ba ita ba taqara mashi girma kodon sun jima basu hadu bane?

hango Mummy datayi tareda ummy yasata sakin Daddy taruga wajenta itama ta rungumeta tana kiran sunanta cikin tsananin murna


murmushi kawai Mummy tayi tana Dan shafa bayanta don ba qarya itama tayi missing dinta sosai

suna ahaka batool tazo ta ture zee daga jikin Mummy tana cewa
"dalla ya isa hakanan, kinwani bi kin maqalqaleta saikace mummyn takice ke kadai" tafada itama tana rungume mummyn


harararta zee tayi takoma wajen Daddy

"Daddy shine baka gayamin zakuzo ba?"

murmushi Daddy yayi
"ai gashi yanzu kinganmu daga sama ko?"

"i miss you soo much Daddy!"


"miss you more shalele"


"to ya isa hakanan, mushiga ciki, sun kwaso gajiya zaku qaramasu wata gajiyar" inji ummy

gabadaya suka dunguma suka nufi ciki Zainab still a maqale jikin Daddy

binsu da kallo Aymaan da babu wanda yayi ta tashi yayi saiya girgiza kai yanufi booth yafara sauko kayan ciki

muryar batool ce ta katseshi daga abinda yakeyi

"oyoyo Akhie! ashe harda kai aka dawo? wlh nama manta dakai akayi tafiyar sai yanzu dana hangoka"


wata lafiyayyar harara ya makamata ya cigaba da fiddo kayan

"da fatan dai kayomin tsarabobi na don ina ganinka naji babu Abinda nake kwadayi kamar goruba"

daukar jakka daya yayi ya rataya yajawo dayan trolley din yanufota

juyawa tayi saurin yi tanufi cikin gidan dagudu don tasan Idan ya kamata saita gane kurenta

a tsaitsaye a falo batool ta taddasu hakan yasa ta qaraso da sauri jim kadan saiga Aymaan shima yashigo

bude baki ummy tayi sannan tace
"Allah sarki, wlh na manta dakai"

6ata fuska Aymaan yayi yaqaraso dakin yana cewa
"ai dama nasan ba'aji dani"

dariya duk sukayi daidai lokacin zee ta dago suka hada ido da Aymaan

wani kyakyawan murmushi tasakar mashi wanda yakusan melting zuciyarshi, hakanan tayi hasashen qila wannan shine tsarabar dayace zaiyi mata wato ya kawomata su Daddy

shima mayarmata martanin murmushinta yayi yana jin wani sanyin farinciki na ratsa zuciyarshi sannan yayi hanyar sama yana cewa
"to nidai na haye kafin gajiya ta kadani"


Jin hakan yasa Abbu cewa suma su Mummy arakasu masaukinsu su Dan huta kafin sufito cin abinci

su zee suka rakasu har masaukin nasu dayasha gyara sai qamshi yake

badon zee tasoba suka juyo suka barsu don sudanyi freshning up



basu dade ba suka sake dawowa main falo din inda suka dunguma gabadaya sukayi dining inda aka baje kolin girke girken da akayimusu kowa yashiga kwasa

fira ce sosai ta 6arke a tsakanin wadannan families din biyu, hira suke cikin raha da barkwanci, zee haryanzu tana maqale kusada daddynta murmushi yaqi barin fuskarta shima aymaan sosai ake firar dashi don nan take fara'arshi da surutunshi yadawo kamar bashine yakoma wani dunkum ba a Nigeria

sun raba dare sosai atare suna maida yadda akayi saida sukaga barci yafara cin qarfinsu sannan suka haqura kowa yaje ya kwanta.




*WASHEGARI*




Ranar fashin school sukayi sukaqi zuwa sai sukayi qaryar basuda lecture ranar

Haka sukayi zamansu suna aikin bude tsarabobin dasu Mummy sukayi musu suna hira cikin nishadi

Mummy kau dik inda zee ta gifta saita bita da kallocikin sha'awa don taga zee taqara hankali sosai kamar ba itaba ga kuma tausayinta datakeji a qasan zuciyarta don sosai taji dadin yadda ta taimakama Deen batareda tayi la'akari da Abinda yayi mata ba, that's shows tanada good heart.


sai bayan asr Ahmad shima yaduro gidan.

dama jiya tun a airport suka rabu shi yawuce gida kasancewar dare yayi lokacin kuma dama yayimusu alqawarin zai dawo yau don akwai zaman da Daddy keso suyi ayau din.


bayan sun gama gaigaisawa cikin mutunci shima ya zauna aka dasa firar daga inda ta tsaya.


can Daddy yayi gyaran murya wanda ya tattaro hankalin kowa zuwa wajenshi suka zubamashi ido cikin son jin mai zaice

"to Alhamdullilah, muna godewa Allah daya hadamu cikin aminci da qoshin lfy muna kuma roqonshi ya cigaba da wanzarda farinciki da hadin kai atsakaninmu"

"wannan zaman namu yanada.dalili koko ince zuwanmu qasarnan ma gabadaya, wasu acikinku sunsan dalilin wasu kuma basu saniba ammazasu sani very soon inshaAllah.

amma dafarko zanfara nuna jinjina da yabawa ga jajircewar wadannan samarin biyu wajen qoqarinsu na aikin qwarai dasuka sanyo gaba, haqiqa kun cancanci yabo akan jarumta da nargartattun halaye naku kuma muna fatan Allah yabiyaku yasaka maku da alhairinsa"

duk da Amin aka ansa wasu kuma kamar irinsu zee da batool basusan inda zancen yadosa ba haryanzu

"Aymaan da Ahmad sunje Nigeria akan wani aiki, aikin da babu mai iya biyansu sai Allah, kuma muna fatan Allah yabamu nasara yakawo mamu warwarewar wannan al'amari.

sunyi mana bayani, bayanin da nasan kowa anan yasanshi kuma mun gamsu hakan yasama muma muka shirya mukazo nan don ida warware matsalar dukda badamu aka faraba"

zee dai kallon Daddy take very confused don haryanzu takasa gane inda ya dosa

kamar ance ta dago kai sai sukayi ido hudu da Aymaan dake kallonta tundazu

wani guntun murmushi yaimata kawai ya dauke kai

"ga wadanda suka sani dakuma wadanda basu saniba ina farincikin sanardaku bayyanar KAMALDEEN MUHAMMAD wato DEEN"


wani irin bugawa zuciyar zee tayi har saida ta dafe saitin zuciyar tana miqewa tsaye batareda tasaniba

gasping batool tayi tana wara idanu kamar zasu fado cikin tsananin shock


murmushi Daddy yayi yana kallon zee dake tsaye haryanzu hannunta a saitin zuciyarta idanunta a ware tana kallonshi

"yes daughter, Deen is back. Deen yadawo, yana Nigeria. can su Aymaan sukaje kuma sun ganshi sunyi magana dashi"

girgiza kai zee take unbelievabling tanajin komai a mafarki tanason yin magana amma takasa

"eh Zainab, Deen ya bayyana, munsan inda yake. yana Abuja yazama mawaqi, munso mugayamaki tunda wuri amma muka yanke shawarar fara confirming.komai sannan, Deen ya bayyana, na ganshi Aymaan ma ya ganshi, munyi magana dashi"

cigaba da girgiza kai zee tayi don sam zee bata yarda ba, dole wani suka gani, wani mai kamadashi kokuma Mussadiq, yes qila Mussadiq suka gani sukayi tunanin Deen ne

"m..mussadiq ne" tafada cikin wata murya mai rawa sosai

"A'a Zainab, ba Mussadiq bane, Deen ne. look.. duba dakanki kigani" yafada yana fiddo wata laptop yabude

duk zubamashi idanu sukayi in curiosity harya gama yan danne dannenshi ya juyomasu ya ajiye akan stool din kusadashi yayinda image din laptop din yafito tarr kowa na falon nagani


waqa ce ta video


da sajenshi tafara tozali kasancewar gefen fuskarshi akafara haskowa


bugun zuciyarta ne ya ninku lokacin da aka hasko pink lips dinshi wadanda bazata ta6a qin ganesu ba daidai lokacin lips din suka fara motsawa cikin salon waqa



_karki barni.. sahibata_


_karki qini... ki fahimta_


_sai dakee... zani huta_


_zuciyata ga kece ta lalla6o_


_ta amince ki maidata yar dako_


_kinga qaunarki taimun riqon la6o_


_wani reshe ya kama ya jijjigo_


zee batasan sadda takoma kan kujerar data tashi ba jagwab lokacin datayi tozali da full face din Deen din.


_kingani ban iyawa da So haka_


_magani zaki ban don na waraka_


_kinga ya maidani wani sa d'aka_


_yafi qarfina sai yaita ha66aka_



_tunda nabaki raina da zuciyaa!_


_me kikeso nayimiki zan iyaa!_


_yau dake gobe na shaida tunjiyaa_


_kinga nazam kamar marar lafiyaa_


_zuciyata ❤️ tanaimun bugun tara💗_


_gashi nikuma naqi na haqura_

_dukda nasha wuya bani daddara_

_kai bala'i na So🤍 nada takura😭_


_wai ina kika jene masoyiyaa!_


_nayi nemanki naqara tambaya!!_


_har wadansu sunaimini dariya😔_


_ni bazan daina sonki ba kinjiya_

_dukda yasani ban jiyo Dan kira_


_tallafa min kissamini lafiya🙏🏻😭_
(sai dake ? hamisu breaker)



Ummin fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*








*079*







*wannan page din nakine takwara, nagode da ziyarar jiya fatan kun koma gida lafiya🥰*









Rufe baki batool tayi da hannunta dake dan 6ari idanunta cikeda kwalla, she's shocked Idan akwai kalmar datafi shock ma tayishi.

she can't believe Deen ne wannan, she can't believe Deen is back!

dauke idanunta tayi daga screen din laptop din takalli saitin zee

haryanzu zaune take inda take motionless, idanunta dasuka sauya launi kafe a screen din babu ko kyaftawa

haka suka cigaba da kallo har waqar taqare

kowa Juyowa yayi yana kallon zee don ganin reaction dinta amma haryanzu tana a yadda take yadda kasan statue

"munfara ganinshi ne ta media, mawaqine sosai wanda ke zamani. yana xaune a Abuja kuma acan yake gudanar da rayuwarshi, wannan tafiyar ma damukayi duk don muganshi ne kuma muga inda yake yadda komai zaizo mana da sauqi" inji Ahmad yana kallon zee

Aymaan kau hannunshi ne rungume a qirji ya sadda kai qasa bakama ganin fuskarshi bare kasan halin dayake ciki.

kuka ne ya kufcema batool tayi saurin rungume zee dake gefenta tanayi ahankali
"Zee Deen is back"tafada cikin rawar murya tana qara qanqame zee dahar yanzu batayi motsiba

ganin batace komai ba yasa batool dan sakinta ta dago ta kalleta ganin still idanunta na saitin laptop saita sa hannu tajuyo fuskar saitinta

"kinji zee, Deen is back, say something. abun farinciki ne right? abun farinciki ne" inji batool tana hawaye sosai

kallonta zee kawai keyi batace komai ba sai gangarowa da hawayen dake maqale a idanunta sukayi

ahankali tasa hannu ta janye hannayen batool daga riqon datayiwa fuskarta ta miqe ahankali

kowa dagowa yayi yana kallonta harda Aymaan da shima idanunshi sun chanza launi sosai


ahankali tafara takawa ta wuce ta nufi stairs

ahankali Aymaan daya lura da yanayin tafiyarta ya miqe idanunshi akanta

takai bakin stairs ta daga kafa kenan zata fara taka stairs din wani wawan jiri ya dibeta tayi baya baya

Aymaan da dama kamar yasan da hakan yayi wuff cikin zafin nama ya qarasa kafin takai qasa ya tarota tafado jikinshi har yana durqushewa akan gwiwa daya

farr farr idanunta keyi kamar mai qoqarin budesu yayinda sukuma suke rufewa

kafe fuskarta Aymaan yayi na kallo yana jin yadda jijjiyoyin kanshi ke tashi rudu rudu

"Zainab.." yafada ahankali kamar a rad'a

"Deen..." itama tafada ahankali daidai lokacin da idanunta suka ida rufewa ruff



tsayawa yayi yana kallon fuskarta kawai batareda ya iya ko motsawaba


kingin yan dakin ne suka qaraso wajen a gigice kowa na kiran sunanta.


dagudu batool tadawo hannunta riqeda bottle water ummy ta amsa aka bude murfin aka shashafamata ruwan a fuska amma shiru

qara yayyafamata sukayi nanma ko motsi batayi ba

ganin hakan yasa Aymaan dake jin kanshi kamar zai rabe gida biyu don sara yunqurawa ya tashi daita a hannunshi

hanyar fita falo yanufa hakan yasa Ahmad saurin ficewa yanufi parking space.


kafin Aymaan ya isa harya bude mashi back seat Aymaan ya sunkuya ya sakata ciki sannan ya nufi gaban motar yana barma su ummy kofar bayan bude don su shiga.


ummy da Mummy ne suka shiga bayan while Aymaan da Ahmad ke gaba sukuma Daddy suka hau dayar motar tareda batool daketa qoqarin dakatar da hawayenta

cikin qanqanin lokaci suka fice daga gidan suka nufi hospital din da Aymaan ke aiki.



babu 6ata lokaci aka kar6eta aka kuma shiga bata taimakon gaggawa

Aymaan baya cikin likitocin dake dubata don suna kaita dakin da aka kwantar daita yafice daga asibitin

su ummy sune suka zauna waje jugum kowa abin duniya ya dameshi

ba'a dade ba akafara kiraye kirayen sallar magrib hakan yasa duk mazan suka wuce massalaci suka bar matan anan.

dawowarsu daga massalacin yayi daidai da fitowar likitocin daga dakin da aka kwantar da zee


saurin qarasawa sukayi suna tambayar yadda ake ciki

ataqaice suka amsamasu yanzu komai yayi daidai amma zasuso ganin mahaifanta personally a office


Abbu da Daddy suka bisu suka wuce office din.


bayani marar dadi likitocin suka basu na hawan jinin zee daya qara tashi ya hau sosai

sunkuma sanar dasu damuwa tayimata yawa har abin na neman ta6amata zuciya

shawarwari suka basu na yadda yakamata su bar barinta tana shiga damuwa domin hakan ba qaramin illa bane agareta yanzu

sannan sukace zasu daurata akan magani wanda zai taimaka mata sosai akan halin datake ciki.


sosai jikinsu yayi sanyi sunajin badadi sosai

Abbu ne yayi qarfin halin tambayarsu halin datake ciki yanzu sukace yanzu sun shawo kan komai don yanzu haka barci take sanaddiyar allurai da akayimata.

sosai suka qara yimasu bayanai akan ciwon zee din da shawarwaru sannan suka shaidamusu mutum daya kawai za'abari yayi jinyarta kingin saidai sukoma gida.

Tare da likitocin suka sake fitowa daga office din suka nufa ward din da aka kwantar da zee din gabadaya

a kwance suka taddata tana sauke numfashin barci ahankali hannunta daure da drip

babu wanda be tausayamata ba a wannan halin don she looks so pale kamar wadda tayi wata tana jinya.

basu dade ba aciki suka fito waje inda anan suka hau shawarar wadda za'a bari wajenta tunda sunce mutum daya suke buqata.

daga qarshe dai ummy aka bari daita kingin duk suka fito zasu gida batool sai 6atarai take don ita da so samune ta zauna.


haka suka bar asibitin cikin nauyin zuciya da jimami kowanne tausayinta danqare a zuciyarshi.



koda suka isa gida kowa shigewa yayi part dinshi kasancewar dare yayi hakan yasa kowa shigewa sashenshi with heavy heart.


batool na zaune bisa sallaya bayan tagama sallolinta wayatafara Ringing

waigawa tayi taga wayar zee dake kan mirror ke Ringing din

tashi tayi ta dauka da niyyar kasheta amma ganin mai kiran yasata dakatawa

kallon wayar ta cigaba dayi tana shawarar ta daga ne koko

ganin zata tsinke yasata saurin dagawa ta kara a kunne

"Aslm Ummie na" inji Aysha daga dayan bangaren

"wslm Ayush" inji batool cikin son daidaita yanayinta

"laa sis batool, ya kike"

"lfy lau, ya kike yasu Ummie?"

"duk lfy, ina mutuniyar?"

Dan shiru batool tayi saikuma tace
"oh tayi barci"

"barci yanzu? this is just to 9"

"ai... qila agajiye takene shiyasa" tafada adan daburce don dama batool bata iya qarya ba


Dan shiru Aysha tayi can tace
"this is not true, gayamin meke faruwa? ina Ummie?"

"ai...ai gaskiya nake.."

"no sis batool kada muyi haka dake, kifadamin gaskiya please, tsakaninki da Allah ina Ummie?"

rolling idanu batool tayi, batajin tana iyayin qarya kuma bayan ta hadata da Allah

Ajiyar zuciya ta sauke
"tana hospital"

"what!!"

"erm... look da sauki sosai kawai dan zazza6ine bawani abu ba"

"innalillahi waina ilaihi rajiun, wane hospital? meya sameta?" tafada hankali tashe

"zazza6ine kawai kuma nace miki dasauqi"

"wane hospital take?"

"A-shifa'u hospital amma nama san gobe za'a sallame... hello? hello?"
ina har an katse kiran

sauke wayar tayi daga kunnenta tana sauke Ajiyar zuciya ahankali.



***


ahankali ya murda handle din kofar ya turo ahankali batareda tayi qara ba sannan yashigo shima

hango ummy yayi saman dayan gadon wanda dama na masu jinya ne tana barci

ida qarasowa yayi dakin idanunshi akanta har saida yazo gabb da gadonta

kafe fuskarta datayi fayau yayi da idanunshi dasukayi ciki ciki

ya dade sosai ahakan kafin ya motsa yabar wajen yanufi yar locker kusada gadonta ya dauki file din dake kai ya bude yashiga going through dinshi

saida yagama sannan ya maida ya ajiye ya gyaramata tafiyar ruwan drip din sannan yajuya yafice daga dakin as quietly as he entered






*WASHEGARI*





Da wuri mutanen gidansu batool suka bar gidan suka nufi hospital don dama jinsu suke kamar akan qaya, saida suka hadama yan asibitin breakfast sannan suka fito suka hade dasu Daddy suka kamo hanya.



lokacin dasuka isa har lokacin zee bata farka ba amma likitocin sun tabbatar musu komai is normal kawai alluran ne basu gama sakinta ba.


haka suka zauna don ana barin zama a ward din suna fira wanda duk ta Deen ce da zee.


suna ahakan har wajajen 11am lokacin harda su Daddy cikin ward din aka kwankwaso kofa

izinin shigowa sukabada don sunyi tunanin Ahmad ne ko Aymaan dukda Aymaan din be dade da fita ba

murda kofar akayi aka turo

Dan wara idanu batool tayi ganin mai shigowar

Aysha ce sanye cikin milk abaya tayi irin shigarsu ta larabawa saidai fuskarnan dauke take da alamar damuwa

mammaki ne yakama batool don ita tama manta dawata wayar dasukayi daita jiya

mammaki be ida kasheta ba saida Aysha tashigo na bayanta ya bayyana

sakin baki tayi cikin tsananin mammaki bama ita kadai ba harda dukkan mutanen dakin

zuciyar Daddy da Mummy sukayi wata iriyar faduwa lokacin da idanunsu sukayi tozali dashi


sanye yake cikin simple qanannun kaya sa6anin suit da aka saba ganinshi dasu saidai wannan baqin tabarau din nashi na gado nanan maqale da idanunshi


kowa na dakin idanunshi nakanshi yayinda shikuma idanunshi ke kanta ya kafeta dasu babu kyaftawa.

gaisuwar Aysha ta dawo dasu daga duniyar kallon Mussadiq duk suka maido hankalinsu kanta

yan dakin suka shiga amsa gaisuwar tata banda Mummy data kafe Aysha itama da kallo tana ganin wasu qanannun qanannun kammaninsu da Deen kama daga coolness din muryarta da dimple dinta na tsakiyar gemu mai lotsawa koda


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login