Showing 258001 words to 261000 words out of 322641 words

Chapter 87 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4317

magana take.

kasa janye idanu Mummy tayi akanta tanajin zuciyarta na melting ahankali cikin shauqi, tabbas wadannan jinin Deen ne ko makaho tashafa saiya gane.

cikin damuwa Aysha tawuce gefen zee dake kwance takama hannunta ahankali tana tambayarsu yamai jiki asanyaye kamar mai shirin kuka

cikin sigar kwantar da hankali su ummy ke amsamata cewa da sauqi sosai yanzu ma barci take.

shiru Aysha tayi tana kallon fuskar zee kamar zatayi kuka don ganinta a wannan condition din ba qaramin ta6ata yayi ba.


ahankali shima Mussadiq dake bakin kofa har lokacin qarasowa dakin idanunshi dake lullu6e da tabarau akan sleeping zee

Daddy har wani dauke numfashi yayi saboda Juyowa dayayi ya kalleshi

cikin alamun girmamawa yadan russunar dakai yace
"good morning" ataqaice


dafarko kasa amsawa Daddy yayi saboda rikicewa saikuma yasamu ya fizgo muryarshi dakyar yace
"y..yes, g..good morning"

be qara bi takanshi ba yawuce wajenda su ummy ke zaune suma yashiga gaidasu cikin turancinshi mai slant din Arab

ganin hakan yasa Daddy saurin juyawa daga dakin ya bude kofa yafita duk arikice.


amsawa su ummy da Mummy data kasa janye idanu akanshi sukayi, gani take kamar batun wannan na gabansu ba Deen bane ba qaryane don itadai idanunta Deen yake gwadamata

tambayarsu yayi jikin mai jiki suka amsamashi cikin fara'a

daga nan yaja bakinshi yayi shiru.

batool ce ta dago tadan saci kallonshi sannan ta gaidashi

beko kalli gefenta ba ya amsa ahankali ya cigaba da tsayuwarshi yana kallon zee dake barcinta ahankali


"Aysha meet Mummy, maman zee" inji batool tana nuna Mummy

tare suka kalli Mummy da Aysha da Mussadiq

wara idanu Aysha tayi cikin mammaki
"really?"

kada mata kai batool tayi hakan yasa Aysha wucewa wajen Mummy dasauri tayimata side hug cikin jindadi tana dariya

wani farinciki ya kama Mummy itama tanata murmushi suka shiga sabuwar gaisawa Aysha na tambayarta ya Nigeria kuma yaushe sukaxo Mummy na amsa mata.

ummy ce tadago ta kalli Mussadiq dake tsaye daga nesa dasu kamar wani saqago cikin larabci tace mashi
"ko ka iya cire drip kunga yaqare gashi basu shigo ba"


kallonta yayi saikuma yakalli drip din sannan ahankali ya qarasa wajen batareda yace komai ba

duk binshi da kallo sukayi harya qaraso yafara cire drip din daga cannula din hannun zee

yana cikin hakan idanun zee suka fara motsi arufen dasuke

shidai Mussadiq belura ba don hankalinshi nakan Abinda yakeyi

ahankali tafara bude idanunta dake ganin biji biji harsuka ida budewa tangaram


again wannan fuskar ita taqara yin arba dashi


kafe gefen fuskar tashi tayi da ido babu ko kyaftawa harya gama yajuyo shima ya kalleta suka hada ido.


Shima kasa dauke idanunshi yayi akanta suka kafe juna da idanu na wani lokaci

tunawa dayayi akwai mutane a dakin yasashi saurin janye idanunshi daga kanta yajuya zai wuce

caraff yaji an cafko hannunshi wanda hakan yasashi tsaya cak daga tafiyarshi


Dan shiru yayi sai kuma yafara Juyowa ahankali harya ida Juyowa ya sauke idanunshi cikin nata dake qyallin hawaye

tsayawa yayi yana kallonta kawai batareda ya iya amsar hannunshi daga nata ba.

"Deen..." tafada in whisper...✍?



*kuyi hqr, haryanzu jikin sai a slow, acigaba dasani a du'a🙏🏻*




Ummin fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*













*080*









ahankali yasa hannu yaxare glasses din idanunshi yana kafeta da oily eyes


kamar wadda idanun suka tunama wani abu saitafara releasing hannun nashi ahankali still idanunsu acikin najuna


dukkan mutanen dakin idanunsu na kansu not moving

"waye shi?" yafada ahankali idanunshi anata


kowa wara idanu yayi yana kallonshi in outmost shock

"who is Deen?" yaqara tambaya yana kallon tsakiyar idanunta


bazai manta ba farkon haduwarshi daita Abinda takirashi kenan, wancan haduwar tasu a library ma ta kirashi da hakan and know? waye mai wannan sunan? meyasa Idan ta ambaci sunan saitayi hawaye?

su ummy ko kallonsu suke hankali a mugun tashe kowa yakasa motsi


"tell me, who the hell is he!" yafada da Dan qarfi idanunshi na dan sauya launi


"hey Mr, incase ka manta this is hospital ba filin kasuwanciba"

Juyowa duk sukayi suna kallon Aymaan dake tsaye bakin kofar ward din hannunshi zube a aljihu

wani qololon baqinciki ya tsayawa Mussadiq awuya daga ganinshi hakan yasashi jan guntun tsaki yajuya ya cigaba da kallon zee data maida idanunta ta lumshe

"Ummie..."

"muna buqatar kowa yafita don zamu dubata" yaqara jin muryar Aymaan na katseshi da hakan

su ummy dai kasa cewa komai sukayi sai binsu da kallo dasuke da daddaya

ignoring dinshi Mussadiq yayi ya cigaba da kallon zee
"are you ok?"

"wannan likitan ta zai iya gane hakan wanda hakan zai yiwuwu ne Idan kuka bashi wuri ya dubata, don't ask her if she's ok cos you can only get the answer from her doctor.. that is Me" inji Aymaan yana qarasowa gaban gadon shima


Juyowa Mussadiq yayi yana kallonshi in the eye sternfully shima Aymaan na maida martanin irin kallon yadda kasan zakaru biyu masu shirin afkawa juna


kingin mutanen dakin kallonsu kawai suke sunkasa cewa komai kowa da Abinda ke jeka kadawo a zuciyarshi

Mummy ce tayi qarfin halin tankawa ta hanyar cewa
"it ok, Bari mufita dama tunda ta tashi kamata yayi adubata, batool, daughter kutaso mukoma waje" tafada reffering to Aysha da batool

kamar jira sukayi duk sai suka tashi harda ummy sukayi waje

har lokacin da Aymaan da Mussadiq basu Bar jifan juna da mugun kallon dasukeyi ba can ahankali Mussadiq ya maida shade dinshi yana cije lower lip dinshi sannan shima yajuya yafice daga ward din kamar zai tashi sama



da kallo Aymaan da zee suka bishi harya fita.

Dan tsaki Aymaan yaja sannan yajuyo ya kalli zee, sauke idanunta zee tayi kawai batareda tace komai ba

qarasowa gefen gadon yayi yana kallonta

"ya jikin?" yafada yana zura hannu daya a aljihu idanunshi kanta

kadamashi kai kawai tayi batareda tace komai ba

shima batareda yasake cewa komai ba yashiga dubata

saida yagama sannan yadanja baya yana sauke abin kunnenshi qasa ya dauki file dinta ya ciro pen yafara rubutu

"I hope kinsan condition din heart dinki"

dagowa tayi takalleshi taga hankalinshi ma na kan rubutun dayake

"Idan ta cigaba da samun attack irin wannan am sorry to say komai na iya faruwa... ciki harda bugawarta"

sauke idanunta tayi batace komai ba

"the heart is the strongest organ of the body and at the same time the most fragile organ, ya danganta da yanayin datake ciki at the particular time, saidai akowanne yanayi take yakamata mai ita yasan cewa it's the most important organ that without it no other organcan perform it's function"

daidai nan yadago ya kalleta yaga itama shi take kallo

"without out heart there will be no life, tana bugawane tareda rayuwa, tana tsayawa rayuwa ma zata tsaya.. cak kamar tsayuwar agogo"

still idanunsu nacikin najuna

"mutuwa abuce data zama dole, mutuwa ta sanaddiyar bugawar zuciya is very normal don mutuwa daya ce amma silolinta nada yawa kuma bugawar zuciya na daya daga cikinsu Don haka don zuciyar mutum tabuga yamutu abune da bazai zama na alhini ba... saidai Idan zuciyar tabuga a dalilin Abinda be cancanci bugawar zuciyar ba ko akan wanda be cancanta ba.. za'a kira hakan ne bada tsautsayi ba saidai ganganci"

kallonshi take sosai lokaci guda kuma hawaye suka fara taruwa a large eyes dinta

"zaya mutu ne akan wanda be cancanci hakan ba yabar wadanda suka cancanci hakan, wadanda kullum burinsu farincikinshi, walwala da nishadi. wadanda suke iya sadaukar da komai akanshi tunkafin yazo duniya har yashigo duniyar har wannan lokacin dayake qoqarin wancakalar da rayuwarshi akan wani abin daban.. har abada"

"zaya tafi yabarsu suna baqinciki, baqincikin da wanda yatafi dominshi bazaiyi rabin rabinshi ba saboda shi bashida asara ko yanada ita yar kadan ce batakai ta wadannan mutanen ba... kuma ba kowa bane wadannan mutanen face IYAYE"

"Iyayenka ne zasu iya xama dakai akowane irin yanayi, suyi sharing kowane feeling dakai, farinciki? baqinciki? qunci? damuwa? komai.
kuma duk lalacewarka bazasu ta6a rabuwa dakaiba duk wahalar dakake basu bazasu ta6a yin watsi dakai ba.. duk runtsi"

"wadannan mutanen?.. su ya kamata mutum yafara sawa agabanshi, yafara duba wane hali zasu shiga Idan har ya aikata wani abin bawai mu rufe zuciyarmu ba mu makance qarshe muzo muyi Abinda zaiyi hurting our beloved ones na har abada"


Dan shiru yayi yana kallon yadda hawayenta yaqi tsayawa

Dan murmushi yayi yana sauke idanunshi kan file din dake kan locker haryanzu

"hawaye... wani lokacin rahamane domin yana gangarowane tareda kaso mafi yawa na damuwa amma Idan yayi yawa harya rikida yakoma jini yana zama babban illa.. ga zuciya da gangar jiki gabadaya"


sake dora pen yayi kan file din yasake yan rubuce rubuce sannan ya maida yarufe

dagowa yayi batareda yasake kallonta ba yace
"za'a doraki akan magani, please endeavor to take them at the right time ko don beloved ones dake damuwa da damuwarki"

yana kaiwa nan yajuya yanufi kofa.


binshi da kallo tayi da rinnanun idanunta harya fice

fashewa tayi da wani kuka mai tsuma zuciya tajawo pillon kusada ita ta cusa fuskarta aciki tana cigaba dayi.






***

A bangaren Mussadiq kuwa yana fitowa beko kalli kowa ba yanufi hanyar fita daga wajen.

sosai ranshi ke a 6ace don ba qaramin qonamashi rai Abinda Aymaan yayimashi yayi ba.

harshi zai mashi taqama da matsayinshi? harshi zai koro waje don kawai taqamarshi shi likita?


a stairs suka kusa cin karo da Daddy dake tareda Abbu suma sun karyo kwana

saurin sake dauke numfashi Daddy yayi ganin kamar ya kalloshi ya kauda kai har Mussadiq da 6acin rai bemasa yawani tantancesu ba yayi wucewarshi


sauke numfashi yayi nannauya yana bin bayanshi da kallo sannan yajuyo gun Abbu dake kallonshi

"lafiya daiko?" inji Abbu


"lfy... kawai Idan nadora idanuna akanshi.. sainaga kamar Deen ne" inji Daddy yana qara bin inda Mussadiq yabi da kallo


murmushi Abbu yayi yace
"ai ikon Allahn kenan, wani abin saisun hadu su biyun ankasa tantancesu, Allah dai ya nunamana ranar"

"Amin" inji Daddy sannan suka wuce saman



Direct parking space din asibitin Mussadiq yanufa ya nufi motarshi ya bude yashige ya maido ya rufe

yadda yake abubbuwa da qarfi zaisa kagane har lokacin afusace yake

saida yashiga motar sannan yatuna ashe tare suke da Aysha

dogon tsaki yaja sannan yazaro wayarshi ya lalubo numberta yayi dialing


Ringing biyu aka daga

cikin larabci yafara yimata bala'i kamar zai jawota ta wayar ya daka (nidai bansan meyake cewa ba🙁)

can ya katse kiran yana sake jan wani tsakin yakoma jikin kujerar motar ya rungume hannayenshi a qirji

Idan akwai wanda kebashi haushi duniya to saidai yabiyo bayan Aymaan, yarasa dalilin da tun a haduwarsu nafarko yaji bemashi ba, he just hate him for no reason.


*Deen?*


waye Deen? meyasa zee ke yawan ambatar wannan sunan? meyasa take kuka duk lokacin datake ambatar sunan?

dole yagano kowaye? dole yagano dalilin kukanta akodayaushe akanshi.

rungume hannayenshi yayi yana saqa da warwara shikadai.





sauke wayar tayi daga kunnenta jiki asanyaye sannan ta kalli su Mummy

"erm... I think I have to go" tafada asanyaye

"tun yanzu?" inji batool tana matsowa kusada ita

ahankali ta kada kai cikin damuwa

"Akhie ne... yace nafito.. qila akwai inda zashi" tafada asanyaye


murmushi Mummy tayimata tace
"ayyah, ai mungode qwarai ma. kiyi sauri to karku tsaidashi, batool ki rakata"

da to batool ta amsa tana gyara mayafinta


ajiye ledar hannunta Aysha tayi tace
"Allah ya sawwaqe, insha Allah zan dawo"

"to mungode qwarai ki gaida Ummie qwarai kinji?" inji ummy cikin kulawa

kada kai tayi tana murmushi sannan suka juya tareda batool suka wuce


Tafiya suke basu cewa komai saidai batool ta lura kamar Aysha tana cikin damuwa


"yadai?" inji batool tana kallonta

Dan murmushi kawai Aysha tayi batace komai ba

"karfa kidamu, insha Allah taji sauqi, trust her she's strong, danasan hakan zaki damu da ban gayamaki ba tunfarko"


murmushi Aysha tayi tace
"I want to see her before I leave, kinga fa tafarka yakamata naganta kafin natafi"

Dan shiru batool tayi kamar mai tunani sai can tace
"in that case muje mugani nasan yaya bazai hanaba iyaka yayimana warning yace karmuyi hayaniya"


cikin jindadi Aysha tace
"yes! let's go please"


ida qarasawa bakin ward din zee din sukayi, saboda zumudi Aysha ce agaba

murda handle din tayi tatura tasawo kai daidai lokacin da shima yasawo nashi sai jikake quuum! sun qume.


saurin jabaya tayi tana dafe goshi cikin jin zafi kamar yadda shima yayi

alokaci daya suka dago suka kalli juna

"ya sallam! sannu, bigewa kukayi?" inji batool data qaraso wajen

ahankali yanayin Aymaan ya chanza lokacin daya gane ko wacece Aysha saiya hade rai yana qarasa fitowa yajawo kofar


Aysha data lura da sudden chanjin fuskar saitayi tunanin ko laifinta ne dasuka qumen hakan yasata cewa
"sorry"


"same" ya amsa sama sama batareda yasake kallonta ba


ganin zai wuce yasa batool saurin cewa
"amm.. yaya wai da ganin zee zatayi kafin tatafi, tafiya zatayi"

Dan Juyowa yayi yadan kallesu sannan yace
"saidai wani lokacin amma yanzu ba'a yarda wani yashiga ba"

daga hakan yajuya yawuce suka bishi da kallo

cikin rashin jindadi batool takalli Aysha

"sorry"


Dan murmushi Aysha tayi tace
"babu komai ai zan dawo, muje Akhie najira"


Juyawa sukayi suka nufi hanyar ficewa daga asibitin


lokacin dasuka isa parking space Mussadiq yakusan bindiga, tun daga nesa yake jifansu dawani mugun kallo

ganin hakan yasa batool dakatawa tun kafin su qarasa sukayi bankwana

qarasawa Aysha tayi ta zagaya tashige motar yaja kamar dama shigowarta yake jira suka fice a tamanin

ta6e baki batool tayi tajuya itama tanufi cikin gida...✍?




*ya hqr dani🙁 adai cigaba da wanke hannu ana tayamu du'ai wlh aljannun typing dina sunfara kawo gardama😆 anemo masu ruqiya🤣🤣*





Ummin fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*












*081*








Inda su mummy suke aymaan yanufa ya taddasu zazzaune hardasu daddy dabasu dade da isa wajen ba

duk dagowa sukayi daga firar dasuke suna kallonshi shikuma yaqaraso yana murmushi

"likita bokan turai, fatan dai diyar tawa tana lfy" inji abbu

murmushi yasakeyi
"eh komai normal, yanzu abinda xataci za'a samarmata taci saitasha magani"

masha allah duk suka fada cikin jindadi daddy yadora da
"sannu da qoqari d'ana, allah yayi albarka wa rayuwa"

duk da amin suka amsa banda aymaan dayayi murmushi Kawai

"to yanzu muna iya shiga ko? dazu kawani koromu waje ko yar kararnan babu" inji ummy tana harararshi

dariya duk sukayi daddy yace
"ato ai gwara hakan idan kuna ciki ba lallai bane kubari yayi aikinshi yadda ya kamata ba"

shidai murmushi aymaan yayi bece komai ba

tashi duk sukayi zasu wuce ward din daidai nan batool data dawo daga rakiyar aysha tayi joining dinsu

"ina zaku mummy?"

"wajen zainab, we can see her now"

kallon aymaan tayi cikin mammaki, ba yanzu yace ba'a buqatar kowa cikiba?

mugun kallon daya watsamata yasata kauda kai tana dan turo baki sannan tajuya tabisu mummy da har sun wuce



Jin alamun za'a bude kofar yasa zee saurin share fuskarta ta maida idanunta ta rufe


Jin muryoyinsu mummy adakin yasata bude idanun dasukayi ja tana kallonsu harsuka qaraso wajenta

duk sannu suka shiga yimata kowa namata kallon tausayi kowanne damuwa qarara a fuskarshi

ahankali take kada masu kai tana dan murmushi

cikin dan qanqanin lokaci aka hadamata kakkauran shayi aka bata don tasha

babu musu ta amsa tana sha tana kallon yadda kowa ke qoqarin kyautata mata don sata farinciki


*sune zasu iya zama dakai akowane irin yanayi, suyi sharing kowane feeling dakai, farinciki? baqinciki? qunci? damuwa? komai.*
maganar aymaan tadazu tadawo mata a kwalwa


*wadannan mutanen?.. su ya kamata mutum yafara sawa agaba, yafara duba wane hali zasu shiga idan ya aikata wani abin bawai mu rufe zuciyarmu ba mu makance qarshe muzo muyi abinda zaiyi hurting our beloved ones na har abada*


Dan lumshe idanu tayi tasake budesu.

tabbas aymaan yayi gaskiya, meyasa kullum takeyin abinda daga qarshe beloved ones dinta ke finta shan wahala?
meyasa kodayaushe take saka beloved ones dinta cikin damuwa?

meyasa take sakasu a wahala bayan wanda takeyi donshi bemasan tanayi ba?

imagine? he's a musician, famous musician while ita tananan tanason kashe kanta awofi

tunawa tayi tun bayan barowarta Nigeria wanda yanzu almost 1year ne babu wani abin kirkin data ta6uka illa 6ata lokacinta, tunaninta da tsaddadun hawayenta ga wanda qila yanzu bayama iya recalling sunanta

ita tananan tana hauka akanshi tana 6ata lokacinta akanshi while shi yanacan yayi moving on harya zama wani abin acan

how foolish is she?


jitayi ma ta tsani komai ma, ta tsani asibitin ma, idan ta tuna saboda shi take kwance akan gadon datake akai saitaji wani baqinciki yaqara mamaye zuciyarta


maganinta akabata ta kar6a ta shanye sannan takoma jikin pillon da aka taramata abaya ta jingina

"are you ok now ko kina buqatar wani abin?" inji ummy cikin kulawa

kallon ummy zee tayi saita kada kai sannan ahankali tace
"inaso mukoma gida"


duk kallonta sukayi

"mukoma gida? why? keda bakida lfy?" inji abbu

Dan murmushi da iya fatar le6e ya tsaya tayi tace
"naji sauqi ai, Kuma banason scent din hospital dinne yana tadamin zuciya" taqarashe zancen tana yatsine fuska

"ikon allah, to ai sai abari likitocin suzo muji ta bakinsu tunda suke bada sallamar idan sunga lafiya lau ana iya sallamarki saisu bada, zaman asibiti dama sai don dole bayada wani dadi" inji ummy


daidai nan aka bubbugo kofar ward din

saida akabada izinin shigowa sannan aka murdo kofar saiga Ahmad yashigo tareda ummanshi da aymaan cikin yin sallama

cikin fara'a mutanen dakin suka amsa sallamar sunama umman Ahmad maraba

umman Ahmad mai yawan fara'a ta qarasa ciki suka shiga gaisawa cikin fara'a da girmama juna tana tambayar jikin mai jiki

batool tunda umma tashigo takasa sakewa Kuma

akunyace ta gaidata ta amsa warmly cikin kulawa daga haka ba'a qarajin bakinta ba

zee ma cikin girmamawa ta gaida umman wadda ta amsa cikin kulawa tana tambayarta ya jiki ta amsa da dasauqi itakuma umman tashiga kwararamata addu'o'in samun afuwa

gaisawa sukayi da Ahmad shima yana tambayarta yajiki shima ta amsa da da sauqi

fira ce ta kaure adakin atsakanin ahalin cikin fara'a da nishadi Inda manyan ke firarsu sukuma qananun na sauraronsu daga bayama Ahmad da aymaan suka fice daga ward din


sai wajajen 12 noon suka sake dawowa dakin Inda anan su ummy sukayima aymaan zancen sallamar da zee tace tanaso

qara dubata yayi sannan yace za'a sallameta bayan zuhr don taji sauqi sosai Kuma zata ida warwarewa muddin zata cigaba dashan maganinta on time


umman Ahmad na taredasu har lokacin sallamar aka sallamesu suka fito tare Inda Ahmad yawuce da ummanshi gida suma aymaan sukayo gida suma.



Acikin kwanakin dasuka biyo baya zee tayi iyakar bakin qoqarinta naganin taragewa kanta damuwa

kodayaushe cikin making kanta busy take don kar ma tabama tarin tunannikan dake qunshe aranta damar tasiri azuciyarta.

kodayaushe cikin walwala take Kuma cikin mutane don bata yarda ta kadaice ko yaya ne.

sosai take fighting da zuciyarta wajen ganin ta yakice tunaninshi kwata2 daga zuciyarta


A bangarensu ummy kau wannan sabon halin na zee sosai yabasu mammaki don zee ta tashi daga zee din dasuka sani tana neman komawa her real lively zee

Abinda yafi dauremusu kai shine watsi da maganar Deen datayi don tun ranarda aka gwadamata shi bata sake tada maganarshi ba Kuma dataji alamun za'a dauko topic dinshi zata tashi tsam tabar wajen.

abin nabasu mammaki sosai don ga yadda abaya tanuna son bayyanar deen basuyi tunanin xata shashantar da maganar ba dawuri haka.

ganin bata ko qaunar atada maganarshi don kosun tada barin wajen take yasa suka bar tadamata zancen nashi suka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login