Showing 309001 words to 312000 words out of 322641 words
Chapter 104 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
yasa suke badamu aikatau don susamu sauqin yawanmu ne don bawani iya riqemu sukeyi ba
nima dai naji dadin daukata da akayi agidan don nima nagaji da zaman gidan
ahaka aka tafi damu inda aka rarrabamu wa masu kudi inda ni dawasu guda biyar ne za'a tura saudiya aikatau don matar har qasashe take tutturawa mutane yan aiki
sosai naji dadi jin zanbar qasar gabadaya naje qasar da kullum nake burin ganinta koda a mafarki ne hakan yasa naita doqin tafiyar don har hangoni nakeyi acan ina shiga da fita da cud'anya cikin larabawa
cikin qanqanin lokaci akayimana shirye shiryen tafiyar inda mukabi jirgin ruwa (6arauniyar hanya) har muka samu muka shiga qasar
tunda nake ban ta6a ganin haddaden waje mai kyawun gaske irin na qasar. haka aka tafi damu munata zuba qauyanci har muka isa masaukinmu
anan muka kwana Washegari kuma aka rarrabamu a gidajen dazamuyi aiki
ni gidan wani attajiri aka kaini don kai koda ganin gidan kasan gidan masu dashi ne saboda haduwa, anan aka hadamu nida wadansu da suma aka kawo aikatau da matar gidan mai tsananin wulaqanci
kwata2 mutan gidan basa qaunar baqar fata don afili suke nuna qyamarmu ahaka aka rarrabawa kowa aikinshi dakuma fadamana kudin albashinmu
rayuwa agidan amatsayin yar aiki rayuwace ta wahala da qasqanci don kwata2 basa qaunarmu kamar ma ba kallon mutane suke mana ba don kuskure kadan idan kayi saika yabawa aya zaqinta
ahaka muke wannan qasqanttaciyar rayuwar wanda saida na gwammaci zamana a qasarmu akanta don abin nasu ba iya kyama da hantara ya tsaya ba, abin haryakai harda cin mutuncinmu na 'ya mace inda mazajensu keyimana kallon dabbobin dazasu iya zuwa sujuye qazanttaciyar buqatarsu akai suyi tafiyarsu
hakan dana gani yasa hankalina tashi ainun don abin abin tashin hankaline inda nan take nafara danasanin zuwana qasar
haka naita lalla6awa kullum cikin roqon allah ya kareni daga sharrin mutanen don naga yadda sukeyima kingin yan uwana masu aiki inda suke maidasu kamar karuwansu idan kuma baki yarda ba a laqamaki wani sharrin da za'ayi miki hukuncin dazakiji inama tunfarko kin yarda da buqatunsu (hakan nafaruwa a real wlh, mutane yan Africa masu zuwa wasu qasashen don aikatau dadai sauransu ba qaramin tashin hankali suke fuskanta ba acan saboda tsananin qabilanci da ake nunawa acan inda yawanci ake maidasu sex machine don yawanci sunfison Africans don acewarsu sunfi satisfying dinsu, allah ya kyauta)
ahaka nayi wata uku agidan ina kaff kaff dakaina ina addu'ar allah ya ku6utar dani saidai ba'a dauki lokaci ba wani d'an gidan yafara kawomun hari
sosai hankalina yatashi da ganin hakan, hakan yasa naita kakaucemashi ina addu'ar allah ya ku6utar dani daga sharrinshi
alokacin sosai zaman qasar ya gundureni don da nasan yadda za'ayi nagudu danayi gashi wacce takawomu tun ranar data kawomu bansake sata a idoba
ahaka har watarana saurayin yaso raping dina
lokacin babu kowa gidan don saida yayi yan dabarunshi na yadda zaisameni yaci karenshi babu babbaka
ranar naga tashin hankali don da tsiya yaso afkamin saidai allah yabani ikon makeshi da vase din tangarau mai nauyi akai inda nan take ya silale yasume jini nabin kanshi
ganin hakan yasa na rude don nasan shikenan tawa,ta qare don muddin akadawo aka taddamu haka shikenan nagama shaqar numfashi
hakan yasani fitowa agigice don ni duk tunanina mutuwa yayi, cikin sa'a kau ban tadda mai gadi a gate ba hakan yasa na afka waje nafara gudu irin gudun fanfalaki burina Kawai intsira da rayuwata
haka naita gudu shiga nan fita can batareda nasan inda na nufaba, kuka kau tun inayi harna kasa saboda muryata databar fita ahaka dare yayimin nasamu qarqashin wata gada na ra6a saboda yan kame dake kame da daddare na raku6e ina kyarmar sanyi ina addu'ar allah ya kawomin dauki
ahaka har dare yayi sosai koina yadauki shiru, motoci nawucewa jefi jefi asaman gadar dana 6uya
ahaka tun ban iya barci saboda sanyi da cizon sauro har wani barci marar dadi ya figeni
can cikin barci naji motsi sama2
abinka da dama atsorace nake sainayi firgigit na tashi ina zare idanu
ganin yadda hasken fitilu keta walainiya awajen yasani qara la6ewa ajikin bangon gadar ina toshe bakina don duk tunanina mutanen gidan danake aiki suka biyoni suna nemana kokuma yan kame
daga saman gadar suke haskowa da fitilarsu mai mugun haske kamar masu neman wani abu
nidai qamewa nayi wuri guda inata hawaye ina kyarma
bayan kusan minti daya da haske hasken naji qarar abu tsindum sunjefo cikin ruwan gadar dake gudana yana tafiya
atsorace nasake maqalewa ajikin bangon gadar ina qara toshe baki don atunanina su suka duro ciki
can sainaga nabar ganin hasken can kuma naji tashin mota tasaman gadar aka tafi
dukda antafi hakan besa na iya komawa barcin ba haka naita zaxzare ido cikin duhu ina kyarma saboda sanyin da akeyi gashi ina qarqashin gada
ahaka har haske hasken alfijir yafara ketowa inda anan na yanke shawarar barin wajen don nagaji da cizon da,sauro keyimin hakan yasa na lalla6a ina qoqarin fita daga gadar
kamar ance in kalli gabana saina hangi wani box mai dan girma daga nesa da inda nake
kasancewar akwai tazara,da inda nake yasa nakasa hango ko menene sosai
harzan wuce saina tuna da mutanen dasuka zo jiya suka jefo abu acikin gadar hakan yasa naji inason ganin koma menene
ahankali nake bin gefe gefen gadar ina tattaka dutsinan ciki gudun karna afka cikin ruwan
ahaka harna iso wurin kwalin daya jiqe jagab shima don dutsi ya tokareshi ne da,tuni yabi ruwa
tsayawa nayi ina kallon kwalin cikin dan hasken safiya daya farayi ina saqe saqe
zuciyata nabani qila sharace aciki suka jefar saidai kuma dukda hakan sainaji inason budewa inga me keciki
ahankali nasa hannuna dake kyarma kyarmar sanyin danake ji nabude kwalin inda ganin abinda yake ciki yasa numfashina daukewa cakk na wucin gadi
wani farin yaro nagani aciki hannayenshi da qafaffunshi a quqqule da igiyoyi bakinshi toshe da tsumma an daureshi tamau idanunshi alumshe babu alamun numfashi ko kadan attatare dashi....✍?
*manage banida charge, qila gobe inyi*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/11/21, 2:03 AM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*cigaban 097*
ja baya nayi amugun tsorace don ban ta6a tsanmmanin abinda zan gani kenan
nan take jikina yahau rawa nafara yin baya baya hannu toshe da baki
atsorace najuya nabar wajen dagudu ina bi ta duwatsun cikin ruwan harna samu na koma hanyar danabi nashigo qarqashin gadar nasamu nafita
daga saman gadar na tsaya ina kallon kwalin danake hange daga nesa har lokacin zuciyata banda bugawa babu abinda takeyi
sonike intafi amma kuma nakasa sai kallon kwalin nake batareda na iya motsawa daga inda nakeba
kamar wanda aka jawo saina tsinci kaina da komawa cikin gadar kuma ina tafiya ahankali nasake nufar kwalin
jiki na rawa nasake leqawa naga abinda nagani daxu
yaro ne da bazai wuce shekaru uku ba, farine dukda ba irin tass dinnan ba na larabawa don nashi irin farin nanne mai jajaja, gashin kanshi ajiqe kamar yadda sauran jikinshi yake ya kwanto yarufe rabin fuskarshi
nafi minti biyu atsaye ina kallonshi zuciyata na bugawa kafin cikin qarfin hali dasa hannu nadan ta6ashi
ko motsawa beyiba hakan yasa naqara ta6ashi duk atsorace
ganin be motsa ba yasa cikin qarfin halin na hau kekketa kwalin har ya ida fitowa fili sannan najuyoshi nasa hannu ina qunce mugun daurin da akayima bakinshi
saida nasha wahala sannan na kwance na zazzaro tsummunan da aka cuccusamashi cikin baki ina kuka sosai don an daure mashi bakinne cikeda mugunta ga bakin da kumatunshi sunyi jajur alamun kwanciyar jini
bayan nagama kunce bakin nakoma kan hannayenshi da qafaffunshi dake daddaure nahau quncewa, suma saida nashi wahala sosai kafin na samu kuncewa
saikuma narasa abinda zanyi mashi daganan gashi gari yawaye don haske yayi sosai
ganin hakan yasa nafara qoqarin daukarshi saidai yayimin nauyi sosai hakan yasa nadan kwantar dashi kan dutsin wajen nahau daddana mashi cikinshi daya dan yo sama
akau saigashi ruwa sunshiga fitowa ta hanci ta baki, haka naita dannawa har suka daina fitowa saidai har lokacin ko motsawa beyiba hakan yasa na cije na cicci6eshi dukda lokacin yadan rage nauyi nasamu dakyar nadorashi abaya na don har inayi ina faduwa sannan nashiga takowa ahankali don barin cikin gadar dashi
koda nafito rasa inda nanufa nayi gashi har lokacin ina tsoron kar ace yan gidan danake aiki nacan na nemana gashi nasan shima wannan yaron wadanda suka jefashi a gada sunyi hakan ne don son ganin bayanshi hakan na nufin daga ni har shi muna cikin hadari
hakan yasa maimakon nayi titi nashiga cikin mutane saina yanki daji kawai batareda nasan inda muka nufaba burina Kawai na tseratar da rayuwarmu dukda har lokacin banida tabbacin ba gawace goye abaya na ba
ahaka harna samu nayi nisa sosai harsaida naji ban iya tafiya sannan na haqura muka zube awajen ina sauke numfarfashi
dagowa nayi ina kallon yaron wanda farat daya yashiga zuciyata ina jinshi fiyeda nakejin d'ana dana haifa yakoma
bansan ko yana rayeba ko ya mutu don kwata2 baya motsi kuma natara yatsuna a hancinshi nidai banji yana numfashi ba
kunnena nasa a saitin zuciyarshi ina sauraro ko zanji bugun zuciyarshi saidai shima shiru saida na dade ina sauraro sannan naji bugun zuciyar can qasa qasa
sosai nayi murnar hakan don dafarko harna fara sadaqarwa dacewar yamutu
tashi nayi ina kallonshi batareda nasan wani taimakon dazanyi mashi ba, nasan asibiti yakamata na nema na kaishi amma zuciyata taqi bani hadin kai don gani nake kaishi asibitin daidai yake da jefashi cikin hadarin daya fito don qilan hakan yazamo silar dazaisa mutanen dasuka so ganin bayanshi dafarko susake dawowa
haka mukaita zama awurin cikin rashin sanin abinyi ga yunwa ga sanyi don daga ni har shi kayanmu ajiqe suke
haka mukaita zama har rana tafara fitowa inda anan nasamu nacire mashi jiqaqiyar rigarshi ko yadanji sauqin sanyin
haka natusashi gaba nabuga uban tagumi ina kallonshi batareda nasan abinda zanyi ba ahaka har rana ta take sosai
ganin hakan yasa nasake miqewa na daukeshi nasake goyashi nacigaba da tafiya acikin dajin
ranar naci baqar wahala don haka nawuni ina tafiya babu ci gwara gwara ruwa idan nahadu da matattarar ruwa ina dan kwalfa in jiqa maqoshina ahaka harna qarasa wani qauye qauye
anan qarfina yaqare bansan ya akayi ba kawai sainaji lumm idanuna na rufewa dakansu kaina na juyamin nazube awajen dani da d'an dake bayana
bansan iya adadin lokacin dana dauka ba asume saidai Kawai nafarka naganni cikin wani daki mai dan duhu duhu
firgigit nayi na miqe zaune ina waige waige anan nagane kamar ma cikin bukka nike
agarin waige waigena na hangi wannan yaron shima kwance daga dayan gefen dakin
bansan sadda naqarasa wurin ba da rarrafe nayi saurin tattaroshi ajikina na rungume
ga mammaki na sainaji yayi motsi yana yatsuna fuska saboda motsashi danayi saikuma yafara tari ahankali cikin wata iriyar dakussashiyar murya dabata fita sosai
farinciki ne ya lullu6eni ganin ya motsa hakan yasani sake rungumeshi ina jin wani irin sonshi har qasan zuciyata sai kallon kyakyawar fuskarshi nakeyi babu ko kyaftawa kamar nasamu madubi
ahaka wasu mutane suka shigo bukkar
jin motsinsu yasani dawowa daga duniyar kallon yaron naja dabaya atsorace ina binsu da kallo kamar yadda suma sukemin
suma larabawa ne saidai dagani yan qauye ne duba da yanayinsu
mace ce da namiji duk sun manyanta sun tsaya daga bakin kofa sun zubamana idanu
nima dai kallonsu nake amma atsorace sai qara rungume yaron jikina nakeyi qamm a qirjina yadda kasan za'a kwaceminshi
kallon juna naga sunyi sunyi murmushi sannan suka qaraso ciki suna kallon yadda nake qara jabaya ina mannewa da jikin bukkar
ganin yadda na tsorata yasa suka bar nufomu inda anan matar cikin murmushi don kwantar min da hankali tafara cemin na kwantar da hankalina babu abinda zasuyimin cikin larabci
dukda banajin larabcin sosai amma nagane abinda take nufi saboda gwadawar datakeyi da hannu hakan yasa hankalina dan kwantawa
miqomin hannu tayi akan nabata d'an nikuma saina qara matseshi jikina ina jada baya alamun ban badawa, murmushi sukayi sai mutumin cikin harshen larabci yake tambayata d'ana ne?
dan zaman danayi agidan danake aiki yasani dan sanin wasu guntayen larabci hakan yasa nagane abinda yace min hakan yasa na kada kaina cikin sauri
murmushi suka sakeyi nan suka hau nunamin baxasu cutar damuba taimaka mana zasuyi
dakyar dai suka samu suka lalla6ani na yarda dasu nabasu shi suka mayar dashi shinfidarshi suka kwantar dashi inda anan naga sun cigaba dayimashi wani hayaqi wanda yaita sashi tari da shaqaqiyar muryarshi
nidai ina gefe ina kallonsu harsuka gama yimashi duk maganin dasuke mashi suka kyaleshi yanata barcinshi
abinci suka bani wanda kamar jira nake na amsa hannu narawa nashiga ci saboda tsananin yunwar da dama nakeji
saida naci na qoshi sannan nadawo nutsuwata inda anan sukaso sanin wacece ni mekuma yakawomu qauyensu
dayake duk bajin yaren juna muke ba yasa maganar kurame (demonstration) duk tafi yawa a maganarmu inda anan nake kwantantamasu cewa gudowa mukayi za'a kamamu mu ba yan qasar bane nakuma nuna masu sonike mubar qasar
shiru sukayi suna kallona hakan yasa gabana cigaba da faduwa don duk a tunanina sungano yaron ba nawa bane don shi farine nikuma gaskiya baqa ce dukda ba irin qirin dinnan ba amma dai kwata2 bamuyi kama da yaron ba kuma gashi shi sak balarabe dukda jikinshi ba irin farinnan tass ba yake kamar na jikin kajin turawa amma farine irin mai jajaja wanda anasamun daidaikun masu irin fatar a Africa
tambayata sukayi wacce qasa nake nace Ghana a Africa
sai suka sake tambayata ina uban yaron
cikin qwarin gwiwa nabasu amsar yamutu nima nan aikatau yakawoni saboda tsananin rayuwa saina tsinci kaina da gayamasu duk abinda yafaru a tsohon gidan danake aiki da silar gudowata, abu daya ne ban gayamasu ba shine yaron tsintarshi nayi
sundade suna jujjuya maganata kamar dai basu yarda dani ba don saidai su kalli yaron su kalleni
can sukace karna damu zasu taimaka min nakoma qasarmu can Africa amma sai yaron ya farfado tukunna yasamu lafiya
ba haka nasoba amma babu yadda na iya haka na haqura ina addu'ar allah yarufamin asiri mubar qasar lafiya
saida muka kwana uku agidan kafin yaron ya farka
kuma abin mammaki yana farkawa yafara waige waige yana kiran ummie cikin muryar dabata fita munayin ido hudu dashi ya rarrafo wajena dasauri ya maqalqaleni
sosai na sauke ajiyar zuciya ganin yadda yaron yayi don da yaqi yarda dani da qila mutanen sun zargeni
duk yadda mutanen sukaso ta6ashi qiyawa yayi ya lafe ajikina yayi lamo kamar dagaske ni mamarshi ce
ahaka muka qara kwanaki biyu inda na matsa ni sonike nakoma qasarmu don har lokacin hankalina be kwanta da zamanmu qasar ba
izuwa lokacin sungama gamsuwa cewa d'ana ne saboda yadda yake liqemin kodayaushe yana maqale dani
duk yadda sukaso muqara zama ko don jikinshi dabe ida warwarewa ba qiyawa nayi nace idan naje can zankaishi ayimashi magani
ahaka suka haqura ranarda muka cika sati daya awurinsu namijin ya rakamu mukayi tafiya sosai bisa raqumma har mukazo wani qauye shima
anan ya hadamu dawani wanda aikinsu fitarda mutanen qasar ta 6arauniyar hanya
anan yabarmu bayan yadan bamu dan guzurin tafiya nikau naita godiya kamar zan ari baki
anan aka hadamu da wasu mutanen dasuma qasar za'a fita dasu rabi da kwatansu duk yan Africa ne inda aka lodamu awani qaton jirgin ruwa cikin dare muka daga
daren ranar ko rintsawa banyiba ina qanqame da KAMALDEEN kamar yadda nasamashi suna
hankalina be kwanta ba saida naga mun qetare iyakar saudiya sai lokacin naji sanyi sanyi araina
alokacin nakuma lura duk yawanci mutanen cikin jirgin yan Nigeria ne sannaniyar qasarnan datayi suna duk fadin Africa dama duniya bakidaya hakan yasa nima jin hankalina karkata acan
ataqaice dai saida mukayi kwana uku muna tafiya sannan muka iso Nigeria aka jibgemu garin lagos
lokacin jikin Kamal yaqara rikicewa saboda yanayin tafiyar tamu ga sanyin daya bibbigemu hakan yasa muna sauka na dangana da asibiti wanda dakyar dagano ta hanyar kwatance
ganin mawuyacin halin dayake ciki yasa aka kar6eshi cikin gaggawa inda anan likitoci suka shiga bashi taimakon nikau nakasa zaune nakasa tsaye saboda yadda jinina ke kan akaifa jinake kamar zan rasashi
ahaka likitocin suka fito daya daga ciki yanemi tattaunawa dani inda anan yake sanar dani yaron yakamu ne da ciwon nimonia (Pneumonia) saboda sanyin dayayi mashi mugun kamu (wannan ne Asalin ciwon Deen)
sannan ya rubuta min abbubuwan dasuke buqata tareda magungunna
koda naje wurin sayen sai akayi min lissafin kudadde masu yawa dukda ga lokacin bansan sunada yawaba don bansan kan kudin Nigeria ba sosai
tambaya nayi inda xa'a chanzamin yan kudaddena dana taho dasu daga Nigeria aka nunamin naje na chanzo inda anan na fahimci ko rabin kudin maganin banidasu
komawa nayi asibitin wurin likitan nayimashi bayani akan cewa kudaddena kenan ya taimaka ya dubamin shi banida komai bayansu
cewa yayi babu abinda zai iya yimin indai ina buqatar lafiyar yarona inje inkawo abubbuwan dasuka buqata
haka nasake fita hankalina amatuqar tashe gashi bansan kowaba bare na nufeshi ya taimakamin
haka naita yawo inda daga qarshe nayi abinda banta6ayiba wato bara
haka naita tare duk wanda nagamu dashi akan ya taimaka min inda qalilan ke saurarona har sudan bani wani abu wasu kau ko kallo ban ishesu ba
ahaka nasamu nadan tattara yan kudadden nakoma wajen likitan nazube mashi su da wanda nasamo da wanda dama nake dasu nace yaduba yaga ko sun kai
gani nayi yabi kudadden da kallo wanda hakan ya sanyaya jikina saikuma ya sa hannu yafara tattarasu ya hadesu ya kirga
yana gama kirgawa yadanyi murmushi yana girgiza kai wanda hakan yaqara sanyaya min gwiwa don da alamu dai basu kai ba
nurse yakira yabata wasu kudin banda nawa da takardar maganin yace taje tasiyo sannan yaturomin kudaddena yace na ajiye Kawai
godiya naita yimashi harda kukana don da be taimaka min ba bansan inda zankuma je insamu taimako ba
ahaka nurse din tadawo da abubbuwan daya aiketa saye nan da nan yatashi yafita yakoma inda aka kwantar da kyakyawana.."
dan shiru tayi ta dago tana kallon mutanen dakin daduk suka maidata t.v, daidaiku ne babu hawaye a idanunsu kowa idanunshi yayi jajir jikinsu duk yayi sanyi kamar wadanda akayima shegen duka
kallon Deen tayi da fuskarshi tayi jajir idanunshi sunyi jajir sungaji da zubda hawaye sai kallon kaka yake kamar yau yafara ganinta
ahankali takamo hannunshi tariqe tareda matsewa anata tana dan murmushi sannan tacigaba dacewa
"ataqaice dai saida muka kusan sati asibitin inda likitan duk ya daukemana komai nakula da lafiyar shi sai abinci Kawai nake siye da yan kudadden hannuna
acikin wannan yan kwanakin Kamal yasamu sauki sosai ya warware inda wata shaquwa tashiga tsakaninmu, yadda yake liqemin sai kayi tunanin dama can yasanni ko mun hada wani abu dashi kuma ba haka yakema kowaba don nalura yanada qiwuya don ko likitan baya yarda dashi amma ni yadda kasan uwarshi.
ahaka har aka bamu sallama inda likitan yaita gayamin abubbuwan daxan kiyaye saboda gudun tashin ciwonshi sannan