Showing 309001 words to 312000 words out of 322641 words

Chapter 104 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6216

yasa suke badamu aikatau don susamu sauqin yawanmu ne don bawani iya riqemu sukeyi ba

nima dai naji dadin daukata da akayi agidan don nima nagaji da zaman gidan

ahaka aka tafi damu inda aka rarrabamu wa masu kudi inda ni dawasu guda biyar ne za'a tura saudiya aikatau don matar har qasashe take tutturawa mutane yan aiki


sosai naji dadi jin zanbar qasar gabadaya naje qasar da kullum nake burin ganinta koda a mafarki ne hakan yasa naita doqin tafiyar don har hangoni nakeyi acan ina shiga da fita da cud'anya cikin larabawa



cikin qanqanin lokaci akayimana shirye shiryen tafiyar inda mukabi jirgin ruwa (6arauniyar hanya) har muka samu muka shiga qasar


tunda nake ban ta6a ganin haddaden waje mai kyawun gaske irin na qasar. haka aka tafi damu munata zuba qauyanci har muka isa masaukinmu

anan muka kwana Washegari kuma aka rarrabamu a gidajen dazamuyi aiki

ni gidan wani attajiri aka kaini don kai koda ganin gidan kasan gidan masu dashi ne saboda haduwa, anan aka hadamu nida wadansu da suma aka kawo aikatau da matar gidan mai tsananin wulaqanci

kwata2 mutan gidan basa qaunar baqar fata don afili suke nuna qyamarmu ahaka aka rarrabawa kowa aikinshi dakuma fadamana kudin albashinmu

rayuwa agidan amatsayin yar aiki rayuwace ta wahala da qasqanci don kwata2 basa qaunarmu kamar ma ba kallon mutane suke mana ba don kuskure kadan idan kayi saika yabawa aya zaqinta

ahaka muke wannan qasqanttaciyar rayuwar wanda saida na gwammaci zamana a qasarmu akanta don abin nasu ba iya kyama da hantara ya tsaya ba, abin haryakai harda cin mutuncinmu na 'ya mace inda mazajensu keyimana kallon dabbobin dazasu iya zuwa sujuye qazanttaciyar buqatarsu akai suyi tafiyarsu


hakan dana gani yasa hankalina tashi ainun don abin abin tashin hankaline inda nan take nafara danasanin zuwana qasar


haka naita lalla6awa kullum cikin roqon allah ya kareni daga sharrin mutanen don naga yadda sukeyima kingin yan uwana masu aiki inda suke maidasu kamar karuwansu idan kuma baki yarda ba a laqamaki wani sharrin da za'ayi miki hukuncin dazakiji inama tunfarko kin yarda da buqatunsu (hakan nafaruwa a real wlh, mutane yan Africa masu zuwa wasu qasashen don aikatau dadai sauransu ba qaramin tashin hankali suke fuskanta ba acan saboda tsananin qabilanci da ake nunawa acan inda yawanci ake maidasu sex machine don yawanci sunfison Africans don acewarsu sunfi satisfying dinsu, allah ya kyauta)

ahaka nayi wata uku agidan ina kaff kaff dakaina ina addu'ar allah ya ku6utar dani saidai ba'a dauki lokaci ba wani d'an gidan yafara kawomun hari

sosai hankalina yatashi da ganin hakan, hakan yasa naita kakaucemashi ina addu'ar allah ya ku6utar dani daga sharrinshi

alokacin sosai zaman qasar ya gundureni don da nasan yadda za'ayi nagudu danayi gashi wacce takawomu tun ranar data kawomu bansake sata a idoba

ahaka har watarana saurayin yaso raping dina

lokacin babu kowa gidan don saida yayi yan dabarunshi na yadda zaisameni yaci karenshi babu babbaka


ranar naga tashin hankali don da tsiya yaso afkamin saidai allah yabani ikon makeshi da vase din tangarau mai nauyi akai inda nan take ya silale yasume jini nabin kanshi

ganin hakan yasa na rude don nasan shikenan tawa,ta qare don muddin akadawo aka taddamu haka shikenan nagama shaqar numfashi

hakan yasani fitowa agigice don ni duk tunanina mutuwa yayi, cikin sa'a kau ban tadda mai gadi a gate ba hakan yasa na afka waje nafara gudu irin gudun fanfalaki burina Kawai intsira da rayuwata


haka naita gudu shiga nan fita can batareda nasan inda na nufaba, kuka kau tun inayi harna kasa saboda muryata databar fita ahaka dare yayimin nasamu qarqashin wata gada na ra6a saboda yan kame dake kame da daddare na raku6e ina kyarmar sanyi ina addu'ar allah ya kawomin dauki



ahaka har dare yayi sosai koina yadauki shiru, motoci nawucewa jefi jefi asaman gadar dana 6uya

ahaka tun ban iya barci saboda sanyi da cizon sauro har wani barci marar dadi ya figeni

can cikin barci naji motsi sama2

abinka da dama atsorace nake sainayi firgigit na tashi ina zare idanu

ganin yadda hasken fitilu keta walainiya awajen yasani qara la6ewa ajikin bangon gadar ina toshe bakina don duk tunanina mutanen gidan danake aiki suka biyoni suna nemana kokuma yan kame

daga saman gadar suke haskowa da fitilarsu mai mugun haske kamar masu neman wani abu

nidai qamewa nayi wuri guda inata hawaye ina kyarma

bayan kusan minti daya da haske hasken naji qarar abu tsindum sunjefo cikin ruwan gadar dake gudana yana tafiya

atsorace nasake maqalewa ajikin bangon gadar ina qara toshe baki don atunanina su suka duro ciki

can sainaga nabar ganin hasken can kuma naji tashin mota tasaman gadar aka tafi

dukda antafi hakan besa na iya komawa barcin ba haka naita zaxzare ido cikin duhu ina kyarma saboda sanyin da akeyi gashi ina qarqashin gada

ahaka har haske hasken alfijir yafara ketowa inda anan na yanke shawarar barin wajen don nagaji da cizon da,sauro keyimin hakan yasa na lalla6a ina qoqarin fita daga gadar

kamar ance in kalli gabana saina hangi wani box mai dan girma daga nesa da inda nake

kasancewar akwai tazara,da inda nake yasa nakasa hango ko menene sosai

harzan wuce saina tuna da mutanen dasuka zo jiya suka jefo abu acikin gadar hakan yasa naji inason ganin koma menene


ahankali nake bin gefe gefen gadar ina tattaka dutsinan ciki gudun karna afka cikin ruwan

ahaka harna iso wurin kwalin daya jiqe jagab shima don dutsi ya tokareshi ne da,tuni yabi ruwa

tsayawa nayi ina kallon kwalin cikin dan hasken safiya daya farayi ina saqe saqe

zuciyata nabani qila sharace aciki suka jefar saidai kuma dukda hakan sainaji inason budewa inga me keciki



ahankali nasa hannuna dake kyarma kyarmar sanyin danake ji nabude kwalin inda ganin abinda yake ciki yasa numfashina daukewa cakk na wucin gadi


wani farin yaro nagani aciki hannayenshi da qafaffunshi a quqqule da igiyoyi bakinshi toshe da tsumma an daureshi tamau idanunshi alumshe babu alamun numfashi ko kadan attatare dashi....✍?




*manage banida charge, qila gobe inyi*






Ummin fasihu🧚🏻‍♀?
8/11/21, 2:03 AM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*








*cigaban 097*









ja baya nayi amugun tsorace don ban ta6a tsanmmanin abinda zan gani kenan

nan take jikina yahau rawa nafara yin baya baya hannu toshe da baki

atsorace najuya nabar wajen dagudu ina bi ta duwatsun cikin ruwan harna samu na koma hanyar danabi nashigo qarqashin gadar nasamu nafita

daga saman gadar na tsaya ina kallon kwalin danake hange daga nesa har lokacin zuciyata banda bugawa babu abinda takeyi


sonike intafi amma kuma nakasa sai kallon kwalin nake batareda na iya motsawa daga inda nakeba

kamar wanda aka jawo saina tsinci kaina da komawa cikin gadar kuma ina tafiya ahankali nasake nufar kwalin


jiki na rawa nasake leqawa naga abinda nagani daxu

yaro ne da bazai wuce shekaru uku ba, farine dukda ba irin tass dinnan ba na larabawa don nashi irin farin nanne mai jajaja, gashin kanshi ajiqe kamar yadda sauran jikinshi yake ya kwanto yarufe rabin fuskarshi

nafi minti biyu atsaye ina kallonshi zuciyata na bugawa kafin cikin qarfin hali dasa hannu nadan ta6ashi

ko motsawa beyiba hakan yasa naqara ta6ashi duk atsorace

ganin be motsa ba yasa cikin qarfin halin na hau kekketa kwalin har ya ida fitowa fili sannan najuyoshi nasa hannu ina qunce mugun daurin da akayima bakinshi

saida nasha wahala sannan na kwance na zazzaro tsummunan da aka cuccusamashi cikin baki ina kuka sosai don an daure mashi bakinne cikeda mugunta ga bakin da kumatunshi sunyi jajur alamun kwanciyar jini

bayan nagama kunce bakin nakoma kan hannayenshi da qafaffunshi dake daddaure nahau quncewa, suma saida nashi wahala sosai kafin na samu kuncewa

saikuma narasa abinda zanyi mashi daganan gashi gari yawaye don haske yayi sosai

ganin hakan yasa nafara qoqarin daukarshi saidai yayimin nauyi sosai hakan yasa nadan kwantar dashi kan dutsin wajen nahau daddana mashi cikinshi daya dan yo sama

akau saigashi ruwa sunshiga fitowa ta hanci ta baki, haka naita dannawa har suka daina fitowa saidai har lokacin ko motsawa beyiba hakan yasa na cije na cicci6eshi dukda lokacin yadan rage nauyi nasamu dakyar nadorashi abaya na don har inayi ina faduwa sannan nashiga takowa ahankali don barin cikin gadar dashi

koda nafito rasa inda nanufa nayi gashi har lokacin ina tsoron kar ace yan gidan danake aiki nacan na nemana gashi nasan shima wannan yaron wadanda suka jefashi a gada sunyi hakan ne don son ganin bayanshi hakan na nufin daga ni har shi muna cikin hadari

hakan yasa maimakon nayi titi nashiga cikin mutane saina yanki daji kawai batareda nasan inda muka nufaba burina Kawai na tseratar da rayuwarmu dukda har lokacin banida tabbacin ba gawace goye abaya na ba


ahaka harna samu nayi nisa sosai harsaida naji ban iya tafiya sannan na haqura muka zube awajen ina sauke numfarfashi

dagowa nayi ina kallon yaron wanda farat daya yashiga zuciyata ina jinshi fiyeda nakejin d'ana dana haifa yakoma

bansan ko yana rayeba ko ya mutu don kwata2 baya motsi kuma natara yatsuna a hancinshi nidai banji yana numfashi ba

kunnena nasa a saitin zuciyarshi ina sauraro ko zanji bugun zuciyarshi saidai shima shiru saida na dade ina sauraro sannan naji bugun zuciyar can qasa qasa


sosai nayi murnar hakan don dafarko harna fara sadaqarwa dacewar yamutu

tashi nayi ina kallonshi batareda nasan wani taimakon dazanyi mashi ba, nasan asibiti yakamata na nema na kaishi amma zuciyata taqi bani hadin kai don gani nake kaishi asibitin daidai yake da jefashi cikin hadarin daya fito don qilan hakan yazamo silar dazaisa mutanen dasuka so ganin bayanshi dafarko susake dawowa


haka mukaita zama awurin cikin rashin sanin abinyi ga yunwa ga sanyi don daga ni har shi kayanmu ajiqe suke


haka mukaita zama har rana tafara fitowa inda anan nasamu nacire mashi jiqaqiyar rigarshi ko yadanji sauqin sanyin


haka natusashi gaba nabuga uban tagumi ina kallonshi batareda nasan abinda zanyi ba ahaka har rana ta take sosai


ganin hakan yasa nasake miqewa na daukeshi nasake goyashi nacigaba da tafiya acikin dajin


ranar naci baqar wahala don haka nawuni ina tafiya babu ci gwara gwara ruwa idan nahadu da matattarar ruwa ina dan kwalfa in jiqa maqoshina ahaka harna qarasa wani qauye qauye

anan qarfina yaqare bansan ya akayi ba kawai sainaji lumm idanuna na rufewa dakansu kaina na juyamin nazube awajen dani da d'an dake bayana




bansan iya adadin lokacin dana dauka ba asume saidai Kawai nafarka naganni cikin wani daki mai dan duhu duhu

firgigit nayi na miqe zaune ina waige waige anan nagane kamar ma cikin bukka nike

agarin waige waigena na hangi wannan yaron shima kwance daga dayan gefen dakin

bansan sadda naqarasa wurin ba da rarrafe nayi saurin tattaroshi ajikina na rungume

ga mammaki na sainaji yayi motsi yana yatsuna fuska saboda motsashi danayi saikuma yafara tari ahankali cikin wata iriyar dakussashiyar murya dabata fita sosai

farinciki ne ya lullu6eni ganin ya motsa hakan yasani sake rungumeshi ina jin wani irin sonshi har qasan zuciyata sai kallon kyakyawar fuskarshi nakeyi babu ko kyaftawa kamar nasamu madubi

ahaka wasu mutane suka shigo bukkar

jin motsinsu yasani dawowa daga duniyar kallon yaron naja dabaya atsorace ina binsu da kallo kamar yadda suma sukemin

suma larabawa ne saidai dagani yan qauye ne duba da yanayinsu

mace ce da namiji duk sun manyanta sun tsaya daga bakin kofa sun zubamana idanu


nima dai kallonsu nake amma atsorace sai qara rungume yaron jikina nakeyi qamm a qirjina yadda kasan za'a kwaceminshi

kallon juna naga sunyi sunyi murmushi sannan suka qaraso ciki suna kallon yadda nake qara jabaya ina mannewa da jikin bukkar

ganin yadda na tsorata yasa suka bar nufomu inda anan matar cikin murmushi don kwantar min da hankali tafara cemin na kwantar da hankalina babu abinda zasuyimin cikin larabci

dukda banajin larabcin sosai amma nagane abinda take nufi saboda gwadawar datakeyi da hannu hakan yasa hankalina dan kwantawa

miqomin hannu tayi akan nabata d'an nikuma saina qara matseshi jikina ina jada baya alamun ban badawa, murmushi sukayi sai mutumin cikin harshen larabci yake tambayata d'ana ne?

dan zaman danayi agidan danake aiki yasani dan sanin wasu guntayen larabci hakan yasa nagane abinda yace min hakan yasa na kada kaina cikin sauri

murmushi suka sakeyi nan suka hau nunamin baxasu cutar damuba taimaka mana zasuyi

dakyar dai suka samu suka lalla6ani na yarda dasu nabasu shi suka mayar dashi shinfidarshi suka kwantar dashi inda anan naga sun cigaba dayimashi wani hayaqi wanda yaita sashi tari da shaqaqiyar muryarshi

nidai ina gefe ina kallonsu harsuka gama yimashi duk maganin dasuke mashi suka kyaleshi yanata barcinshi

abinci suka bani wanda kamar jira nake na amsa hannu narawa nashiga ci saboda tsananin yunwar da dama nakeji

saida naci na qoshi sannan nadawo nutsuwata inda anan sukaso sanin wacece ni mekuma yakawomu qauyensu

dayake duk bajin yaren juna muke ba yasa maganar kurame (demonstration) duk tafi yawa a maganarmu inda anan nake kwantantamasu cewa gudowa mukayi za'a kamamu mu ba yan qasar bane nakuma nuna masu sonike mubar qasar

shiru sukayi suna kallona hakan yasa gabana cigaba da faduwa don duk a tunanina sungano yaron ba nawa bane don shi farine nikuma gaskiya baqa ce dukda ba irin qirin dinnan ba amma dai kwata2 bamuyi kama da yaron ba kuma gashi shi sak balarabe dukda jikinshi ba irin farinnan tass ba yake kamar na jikin kajin turawa amma farine irin mai jajaja wanda anasamun daidaikun masu irin fatar a Africa

tambayata sukayi wacce qasa nake nace Ghana a Africa

sai suka sake tambayata ina uban yaron

cikin qwarin gwiwa nabasu amsar yamutu nima nan aikatau yakawoni saboda tsananin rayuwa saina tsinci kaina da gayamasu duk abinda yafaru a tsohon gidan danake aiki da silar gudowata, abu daya ne ban gayamasu ba shine yaron tsintarshi nayi

sundade suna jujjuya maganata kamar dai basu yarda dani ba don saidai su kalli yaron su kalleni

can sukace karna damu zasu taimaka min nakoma qasarmu can Africa amma sai yaron ya farfado tukunna yasamu lafiya


ba haka nasoba amma babu yadda na iya haka na haqura ina addu'ar allah yarufamin asiri mubar qasar lafiya



saida muka kwana uku agidan kafin yaron ya farka

kuma abin mammaki yana farkawa yafara waige waige yana kiran ummie cikin muryar dabata fita munayin ido hudu dashi ya rarrafo wajena dasauri ya maqalqaleni

sosai na sauke ajiyar zuciya ganin yadda yaron yayi don da yaqi yarda dani da qila mutanen sun zargeni

duk yadda mutanen sukaso ta6ashi qiyawa yayi ya lafe ajikina yayi lamo kamar dagaske ni mamarshi ce

ahaka muka qara kwanaki biyu inda na matsa ni sonike nakoma qasarmu don har lokacin hankalina be kwanta da zamanmu qasar ba

izuwa lokacin sungama gamsuwa cewa d'ana ne saboda yadda yake liqemin kodayaushe yana maqale dani

duk yadda sukaso muqara zama ko don jikinshi dabe ida warwarewa ba qiyawa nayi nace idan naje can zankaishi ayimashi magani


ahaka suka haqura ranarda muka cika sati daya awurinsu namijin ya rakamu mukayi tafiya sosai bisa raqumma har mukazo wani qauye shima

anan ya hadamu dawani wanda aikinsu fitarda mutanen qasar ta 6arauniyar hanya

anan yabarmu bayan yadan bamu dan guzurin tafiya nikau naita godiya kamar zan ari baki

anan aka hadamu da wasu mutanen dasuma qasar za'a fita dasu rabi da kwatansu duk yan Africa ne inda aka lodamu awani qaton jirgin ruwa cikin dare muka daga


daren ranar ko rintsawa banyiba ina qanqame da KAMALDEEN kamar yadda nasamashi suna

hankalina be kwanta ba saida naga mun qetare iyakar saudiya sai lokacin naji sanyi sanyi araina

alokacin nakuma lura duk yawanci mutanen cikin jirgin yan Nigeria ne sannaniyar qasarnan datayi suna duk fadin Africa dama duniya bakidaya hakan yasa nima jin hankalina karkata acan

ataqaice dai saida mukayi kwana uku muna tafiya sannan muka iso Nigeria aka jibgemu garin lagos


lokacin jikin Kamal yaqara rikicewa saboda yanayin tafiyar tamu ga sanyin daya bibbigemu hakan yasa muna sauka na dangana da asibiti wanda dakyar dagano ta hanyar kwatance

ganin mawuyacin halin dayake ciki yasa aka kar6eshi cikin gaggawa inda anan likitoci suka shiga bashi taimakon nikau nakasa zaune nakasa tsaye saboda yadda jinina ke kan akaifa jinake kamar zan rasashi

ahaka likitocin suka fito daya daga ciki yanemi tattaunawa dani inda anan yake sanar dani yaron yakamu ne da ciwon nimonia (Pneumonia) saboda sanyin dayayi mashi mugun kamu (wannan ne Asalin ciwon Deen)

sannan ya rubuta min abbubuwan dasuke buqata tareda magungunna

koda naje wurin sayen sai akayi min lissafin kudadde masu yawa dukda ga lokacin bansan sunada yawaba don bansan kan kudin Nigeria ba sosai

tambaya nayi inda xa'a chanzamin yan kudaddena dana taho dasu daga Nigeria aka nunamin naje na chanzo inda anan na fahimci ko rabin kudin maganin banidasu

komawa nayi asibitin wurin likitan nayimashi bayani akan cewa kudaddena kenan ya taimaka ya dubamin shi banida komai bayansu

cewa yayi babu abinda zai iya yimin indai ina buqatar lafiyar yarona inje inkawo abubbuwan dasuka buqata

haka nasake fita hankalina amatuqar tashe gashi bansan kowaba bare na nufeshi ya taimakamin

haka naita yawo inda daga qarshe nayi abinda banta6ayiba wato bara

haka naita tare duk wanda nagamu dashi akan ya taimaka min inda qalilan ke saurarona har sudan bani wani abu wasu kau ko kallo ban ishesu ba

ahaka nasamu nadan tattara yan kudadden nakoma wajen likitan nazube mashi su da wanda nasamo da wanda dama nake dasu nace yaduba yaga ko sun kai

gani nayi yabi kudadden da kallo wanda hakan ya sanyaya jikina saikuma ya sa hannu yafara tattarasu ya hadesu ya kirga

yana gama kirgawa yadanyi murmushi yana girgiza kai wanda hakan yaqara sanyaya min gwiwa don da alamu dai basu kai ba

nurse yakira yabata wasu kudin banda nawa da takardar maganin yace taje tasiyo sannan yaturomin kudaddena yace na ajiye Kawai

godiya naita yimashi harda kukana don da be taimaka min ba bansan inda zankuma je insamu taimako ba

ahaka nurse din tadawo da abubbuwan daya aiketa saye nan da nan yatashi yafita yakoma inda aka kwantar da kyakyawana.."

dan shiru tayi ta dago tana kallon mutanen dakin daduk suka maidata t.v, daidaiku ne babu hawaye a idanunsu kowa idanunshi yayi jajir jikinsu duk yayi sanyi kamar wadanda akayima shegen duka

kallon Deen tayi da fuskarshi tayi jajir idanunshi sunyi jajir sungaji da zubda hawaye sai kallon kaka yake kamar yau yafara ganinta

ahankali takamo hannunshi tariqe tareda matsewa anata tana dan murmushi sannan tacigaba dacewa


"ataqaice dai saida muka kusan sati asibitin inda likitan duk ya daukemana komai nakula da lafiyar shi sai abinci Kawai nake siye da yan kudadden hannuna


acikin wannan yan kwanakin Kamal yasamu sauki sosai ya warware inda wata shaquwa tashiga tsakaninmu, yadda yake liqemin sai kayi tunanin dama can yasanni ko mun hada wani abu dashi kuma ba haka yakema kowaba don nalura yanada qiwuya don ko likitan baya yarda dashi amma ni yadda kasan uwarshi.


ahaka har aka bamu sallama inda likitan yaita gayamin abubbuwan daxan kiyaye saboda gudun tashin ciwonshi sannan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login