Showing 135001 words to 138000 words out of 322641 words

Chapter 46 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4311

ba, what matters most is Good heart"


Shiru daddy yayi kawai yana kallonta, this is the least he has expected


Ajiyar zuciya daddy ya sauke sannan yace
"kije ki sake tunani Daughter, amma wannan ba za6i bane"

Yana kaiwa nan ya miqe ya shige quryarshi


Binshi da kallo both zee da mummy da Tundazu takasa magana sukayi harya shige ya rufo kofar


Mummy ce ta maido dubanta kan zee Hakan yasata sunkuyar dakai tanajin wasu hawaye na taruwa a idanunta


Mummy batace komai ba itama ta tashi tabi bayan daddy suka barta zaune nan ita kadai



Bin mummyn tayi da kallo itama harta shige

Kafe kofar dasuka rufo tayi da idanu zuciyarta na lugude

Koda wasa bata ta6a kawoma ranta soyayyarsu zata samu matsala ta wannan sigar ba

She thought ko mahaukaci takawoma daddy a matsayin wanda takeso zai auramata shi don farincikinta, bata ta6a tsanmmanin wannan reaction dinba daga gareshi


Ahankali ta miqe itama tajuya ta nufi kofar fita daga falon tana share fuskarta da bayan hannu.




***


"nifa sai inga wannan abin duk bekai na tashin hankali har haka ba" inji mummy tana kallon daddy dake zaune Tundazu rai a jagule


Dagowa yayi ya kalleta
"bekai na tashin hankaliba kikace? Kinsan meke shirin faruwa kuwa? My only daughter in love with a mere street guy? Kema kinsan Hakan ba mai yiwuwa bane"


"Alhaji please calm down, wannan abin ahankali yakamata abishi bada zafi zafi ba, kamata yayi a zauna ayi tattaunawa ta fahimta akanshi"

Wani kallo yayima mummy
"wane tattaunawa? Kema kinsan ko me za'ayi diyata bazata auri irin wannan mutumin ba.

The whole diyar Dan Faranshi? Diyarshi tallin qwall? Ina?"


Shiru mummy tayi takasa cewa komai, she's confused also, itama burinta Zainab ta auri wani ko dan wani wanda Hakan daidai yake da qarin qima da mutuncinsu na masu arziqi amma ambatar suna Deen da zee tayi yasa zuciyarta tafara rawa akan wannan ra'ayin nata, Hakan yasa yanzu ita kanta batasan wanda take goyon baya ba, Zainab ko Daddy.

"ni ina nan ina jiran takawo za6inta, I thought it will be the best, ashe am mistaken? A tunanina duk wandanda ta kora mafiyinsu zata kawo ashe ba Haka bane? Taje can an huremata kunne, am very sure wannan ba ra'ayin ta bane wlh, wannan harda zuga da hurin kunne, ai nasan diyata ciki da bai. Babu yadda za'ayi ace wannan shine za6inta, babu.

Wannan kawai hurin kunnene irin na maza and I will never tolerate it, zan koyama mutum hankali ne koma wanene, babu ruwana" yafada cikin tsananin 6acin rai


Ajiyar zuciya mummy datayi zugum Tundazu tayi tace
"to allah ya kyauta"


Beko kalleta ba ya tashi ya nufi toilet din dakin.










Cikin sanyin jiki tafito daga part din daddy takoma part dinsu

Ahankali tashiga hawan matattakalan benen harta qarasa sama

Dakinta ta nufa Direct ta bude tashige ciki ta maido ta rufe sannan ta nufi gadonta ta zauna a gefenshi


Shiru tayi ta qurawa waje guda idanu, zuciyarta keson kawomata wani tunani amma taqi bata damar Hakan, taqi yarda taba kowanne irin tunani damar yin tasiri a ranta

Abu daya kawai ke qarfafa mata gwiwa

Shine Farincikinta shine na daddy itakuma batada wani farinciki daya wuce Deen Hakan na nufin dole daddy yayi accepting din Deen idan har yanason dorewar farincikinta kuma a wannan ga6ar ne batada tantama akai, daddy na iya sadaukar da komai akan farincikinta ciki harda farincikinshi, Hakan ne yaqara qarfafa mata gwiwa akan Deen Amma kuma ta rasa dalilin dayasa kuma zuciyarta ke rawa akan haka, tarasa dalilin dayasa take fargaba dukda tabbacin datake dashi, ta rasa meyasa takeji ajikinta wani abu marar dadi zai faru daita, dasu, ita da Deen.


Ringing din wayarta yasata sauke wata Ajiyar zuciya tana lumshe idanu tareda budewa

Shine, ko bata duba ba tasan shine.

A halin yanzu babu muryar wanda take buqatar ji kamar tashi haka zalika kuma babu wanda bata fatan yaji muryarta ahalin yanzu kamar shi

Jin Muryarshi zai kawo sauqi wa zuciyarta shikuma jin muryarta zai jawo fargaba da rashin kwanciyar hankali gareshi


Kiran farko ne ya katse, ba'a jima ba wani yasake Shigowa

Cigaba da kallon wayar take tana bin sunanshi dake motsi a screen din da kallo batareda ta Ko motsaba har itama ta katse

Daukar wayar tayi dafarko kamar ta kashe sai kuma ta chanza shawara ta sata a silent ta ajiyeta kan bedside locker itakuma ta zame ta jingina da frame din gadon

Idan akwai abinda bataso to tashin hankalin Deen ne don haka dole ta hadiye kwadayin jin muryar tashi ta zauna da nata damuwar ita kadai don tasan dayaji muryarta zaisan babu lafiya kuma zaiso tilasta mata ta fadamashi abinda ke faruwa wanda ita a ganin ta bashi da amfani don abune da bazaiyi wuyar warwarewa ba, tasan daddynta so batada case.
This is just a minor challenge.




*08:35pm*




Kwance take kan gadonta tana danne dannen wayarta tana iyakar qoqarinta na ganin ta kauda duk wani damuwa dake son yin tasiri a zuciyarta Saidai dannar wayar kawai take amma ita kanta bata gane me takeyi da wayar ba


Knocking din kofarta taji anyi

Dago kai tayi ta kalli kofar batareda tace komai ba

Gani tayi an murda handle din anshigo dakin

Mummy ce


Sauke kai tayi cikin zuciyarta tana cewa itafa bata jin yinwa ko an tilastata bawani abin kirki zataci ba

"dress into something decent ki sauko kinyi baqo" inji mummy babu alamun wasa


Saurin dagowa tayi ta kalli mummy
"baqo kuma mummy?"

"eh baqo kuma"

"but I thought..."

"look karki 6atawa mutane lokaci, Kiyi abinda nace yanzu!"


Saurin sauko da kaffafunta tayi daga kan gadon don tasan halin mummy idan ranta ya 6ace

"nabaki 5 mins Kiyi ki fito tun kafin ranki ya 6aci" inji mummy sannan tajuya ta fita

Binta da kallo zee tayi harta fita ganin Hakan yasa tafara dirje dirjen kaffafu aqasa tana kukan ta6ara


"ni ya kukeson nayi ne nace banasonshi banasonshi inada wanda nakeso, haan!" tafada tana hucin kukan datakeyi


Sai kuma ta tashi a fusace tanufi wardrobe ta budeshi da qarfi taciro wata baqar gown ta dorama nightie din jikinta ta yafa gyale tadan fesa turare sannan ta fita looking so angry.



A falon ta tarda mummy ba ita kadai ba harda daddy zaune bisa kujerar dake facing stairs


Bata kalli ko daya daga cikinsu ba tawuce centre table din dake akwai tray mai dauke da kayan motsa baki sama ta dauka ta fice batareda ta yarda ta kalli gefensu ba.


Binta da kallo duk sukayi sannan suka sauke Ajiyar zuciya

"Alhaji baka ganin kamar dolen dakace baxaka yimata ba shi kake niyyar yimata?" inji mummy


Shiru daddy da ranshi ke duk a jagule yayi can sai yace
"haryanzu ba dolen zanyi mata ba, idan basu daidaita ba still zan bata damar samo wani amma ba wannan yaron ba ko makamancinshi, ta nemo miji gidan manya gidan mutunci ba inda zan kaita ba inkasa cin abinci ba saboda tunanin ko ita tasamu abin sakawa aciki"


Ajiyar zuciya mummy ta sauke not knowing what to say don haryanzu batada ra'ayi acikin wadannan ra'ayoyin biyu wato na daddy da na Zainab, Itadai fatanta dai allah ya tabbatar da wanda yafi alhairi



***



Da sallama tashiga guest room din ma wannan karon


The same voice daya amsa sallamarta ta jiya ta amsa yau ma


Bata yarda ta kallo gefen dayake ba ta nufi centre table din Wurin ta ajiye tray din datake jin kamar ta sakeshi Tundazu

Kujerar da ta zauna akai jiya tasake akai yau tayi crossing kaffafunta tafara dannar wayarta


Tunda tashigo yake Binta da kallon qasan ido ganin yau batada niyyar tankamashi yasashi cewa

"sannu" kamar mai ciwon baki


Ahankali ta dago ta kalleshi saikuma ta maida kallonta akan wayarta
"yauwa" tafada itama kamar wanda aka tilasta


Shiru yaqara biyo bayan haka. Ita hankalinta na kan waya shikuma hankalinshi na kanta yana studying dinta


Sun kusa minti 15 ahakan sannan Asaad ya gyara zamanshi a kujerar dayake akai

"Am Asaad Abubakar Dikko by name, ni d'a ne ga Alhaji Abubakar Dikko, a graduate with masters certificate a fannin business, and you?" yafada yana tsareta da madaidaitan idanunshi

Sai a lokacin tasake Dagowa ta kalleshi sama sama tasake Janye idanunta

"Am Zainab.. Zainab Dan faranshi" tafada a taqaice


Kada kai yayi

"Good, hope kinsan dalilin zuwa na nan?"

"zan sanine bayan ka sanar dani"

Dan murmushi yayi na gefen baki sannan ya kada kai yana dan mere baki

"well, ni nasani kuma zan sanar dake dukda nasan kema kin sani"

Dan daga kafadu cikin qara ta6e baki yace
"I was sent here by my Dad, akwai abinda suke son qullawa tsakanina dake for their benefits don Hakan zai qara zumuncinsu da amincinsu kamar yadda sukace, shiyasa aka turoni don wai mu fahimci juna which I think bazai yiwuba don ni atsarina mata Africans basuyimin ba kwata2, primary dina kawai nayi a Africa, secondary dina nayishi ne a france, nayi first degree dina a uk and yanzu na qarqare masters a India

A duk cikin qasashennan babu baqaqen fata duk jajjayene wataqila shiyasa kwata2 bana ra'ayinsu, babban burina shine auren one of those jajjayen ba baqaqen Africans ba dukda ke naga you're not that black" ya qarashe yana dan ta6e baki

Zee tunda yafara ta maida hankalinta kanshi tana kallonshi dumpfounded

"so nazo nan ne ba don mu fuskanci a sigar da tsoffafinmu keso ba sai don mu fuskanci juna na ainahi wato sanin ra'ayin juna akanmu, ni kinji ra'ayi na, so samu kiyi co-operating mu samawa kanmu mafita"


Wani murmushi ya su6ucema zee tadan kauda kai tanayi

Bece komai ba sai cigaba da kallonta dayake yana jiran jin me zatace

Dagowa tayi taqara kallonshi sannan ahankali tafara magana
"A ganina a smart guy with sharp brain tun zuwanshi na farko a wajen budurwa zai gane yasamu kar6uwa ko be samuba.

Me haja shike buqatar talla.

Gaskiya ra'ayinmu yazo daya don nima ban cika ganin mutuncin desperate African a qasashen masu jajjayen fata ba. Wadanda basa kishin kansu bare akai ga kare martabar asalinsu, bana masu kallon mutane at all saboda a qasarsu sunfita sahun mutane saboda basa kishinta a can inda suke marari kuma ba'ayimusu kallon mutane.


Nayi primary school dina a Nigeria, Secondary school ma haka, and now nakusan graduating still a beloved qasata Nigeria and after that ko zanyi aiki I'll proudly reject kowanne offer na kowane qasashe musanmman na jajjayen and proudly stick to my beloved country Nigeria kuma ko zan fita din it will be within Africa din not outside.

So inajin there's no need of worrying tunda ra'ayi yazo daya and am glad it does don ni dama ba kowanne namiji nake ma kallon namiji ba" tafada itama tana dage kafadu kamar yadda yayi dazu.


Tsit dakin yayi

Kallonta yake babu kyaftawa, yama rasa mai zaice ko zaiyi.


Ganin shirun yayi yawa kuma baida niyyar cewa komai ko motsawa yasata sake dagowa ta kalleshi

"mr.... Yama sunan?

Well, whatever. I think tunda mungama fuskantar juna yakamata musan inda dare yaimana ko? As you can see am sleepy already, ko da wata maganar ne?"

Cije lower lip dinshi kawai yayi ya Janye idanunshi akanta

"No, I don’t think so" yafada saikuma yatashi tsaye yana pocketing hannayenshi
"Good night"

"yeah, mu kwana lfy" tafada itama batareda ta kalleshi ba


Zuwa yayi ya wuce ya bude kofa ya fita ya maidota da qarfi har Saida zee tadan dode Kunnuwanta

"stupid fool!" tafada tana bin kofar da harara tareda jan dogon tsaki

Sai kuma tahau Dariya, wai jajjaye yakeso gashi shi kamar gawayi, saikuma ta cigaba da Dariya tana tunanin yan wahala fa yawa garesu a duniya, ita ko dauramata shi akayi a qafa saita kwanceshi ta yar don babu abinda zatayi dashi

Tsaki tasake ja sannan ta miqe tafito itama daga dakin ta nufi cikin gida


Luckily babu kowa falon Hakan yasata hayewarta sama ta maido dakinta ta rufe ta cire gown din saman nightie dinta ta qure a.c ta baje tana fesar da iska daga bakinta.

Bata dadeba ahakan barci yayi gaba daita saboda dadin iskar dake shigarta










*WASHEGARI*



Zaune take tana waya da Deen daketa yimata mita wai jiya yaita kiranta bata dagawa har hakan yaja yakasa samun isashen barci itakuma tana yimashi Dariya

Jitayi anyi knocking din kofarta aka bude aka shigo

Ganin daddy ne yasata saurin katse wayar batareda ta shirya ba ganin yanayin daddyn

"Daddy?"

"Why? Meyasa zaki yimashi haka? Yes nasan bakya sonshi amma abin har yakai kicimashi mutunci? Beci yaci arziqin mahaifinshi ba Zainab?"

Gaban zee ne yafadi Hakan yasa ta saukar da kaffafunta qasa ta miqe tsaye

"Dad meke faruwa ne?"

"look, karma ki fara, nasan ki nasan halinki, tsaf zaki iya finma abinda yace"

"daddy ni me nace? Shi be fadamaku abinda yace ba? Wai he hate Africans wai bayason baqar mace?

"koma me yace be kamata ki kirashi da dabba ba ko don albarkacin amincin dake tsakaninmu da mahaifinshi"

"dabba? Ni yaushe na kirashi dabba daddy?"

"kin fini sani tunda ke kika fada don nasani tsaf zaki fadi fin haka amma ko babu komai ya kamata ko beci darajar mahaifinsa ba ni yaci daraja ta tunda ni na gayyatoshi"

"daddy.." tafada cikin rawar murya idanunta na kawo kwalla

"ba komai ai, laifinane, kinriga kince bakya sonshi nikuma na saki kije wajenshi dukda Hakan, babu komai, tunda baki sonshi fine, bazan tilasta miki shi ba, kije ki samo wani na aura miki amma banda wannan yaron, kin dai jini ko? Banda wannan yaron ko wani talaka irin shi don bazai ta6a yiwuwa ba, so ko shi ke zugaki that won't change anything bazan ta6a hada zuri'a da tallaka ba wlh, tsakanina dasu sai kyautatawa da taimako idan naga dama amma bana alaqa ta surukantaka, never!"
Yana kaiwa nan yajuya yabar dakin a fusace


Binshi da kallo zee tayi harya fice ya maido mata kofarta


Ahankali tayi baya baya ta zauna jagwab kan gadonta tana sauke numfashi ahankali

_meke shirin faruwa daita ne?_

_meyasa wannan case din data raina keson girmama?_

_what went wrong?_


Hannu tasa ta shafo kanta zuwa baya cikin tsananin damuwa

Tanaji tana ganin wayarta nata ringing da tone din Deen Amma takasa dagawa... ✍️






Ummin fasihu 🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:38 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?*



Hhh yau ga post din dare, Gaskiya yau typing ya wahalar dani 🥺




*046*





*THE CHALLENGE 2*







Wunin ranar haka ta qarasheshi rai a jagule, kwata2 tarasa abinda ke mata dadi.


Sosai fushin daddy da alwashinshi ya tsoratar da ita abinka da bata saba ganin haka ba


Da mummy ce tazo tayi mata wannan hargagin bazaiyi tasiri a ranta ba kamar yadda na daddy keyimata yanzu don ita mummy dama ta saba da ganin Hakan agareta amma daddy zata iya cewa tunda tayi wayau bazata iya tuna ranar da ya ta6a yimata fada ba shiyasa yanzu abin ya dameta fiyeda zatonta


Yinin ranar haka tayishi a dakinta ko abinci akazo akayi mata Maganarshi Saidai tace a hauro mata dashi sama kuma cikin sa'a mummy bata tankamata ba akan hakan, qila itama fushin takeyi




Wayarta kau kasheta tayi don tasan Deen bazai barta ta numfasa ba da kiraye kirayenshi gashi ita bata cikin mood din Waya dashi kwata2 don batama son ya fuskanci wani abu gameda abinda ke faruwa





Da daddare bayan wajajen 9:14pm tafito daga dakinta, tasan yanzu daddy na can yana kallon news while mummy na dakinta tana shiri

Dama wannan lokacin ta ware don tasamu daddy suyi magana takuma bashi hqr akan abinda yafaru.



Saukowa qasa tayi ta fita daga part din gabadaya ta nufi part dinshi tana saqa da warwara akan abubbuwan data shirya zata cemashi.


Doorbell ta latsa sau biyu a na ukun ne taji muryar daddy ta cikin dakin yana bada izinin Shigowa


Saida taja numfashi ta fesar sannan ta murda handle din ta tura kofar ta shiga da sallama.


Dagowa daddy yayi daga kallon labarai da yake a t.v yana amsa sallamarta


Ahankali ta qaraso cikin dakin cikin sanyin jiki tana jin hawaye na kawomata

Daddy kau kafeta da idanu yayi harta qaraso tsakiyar dakin Hakan yasa ya miqamata hannu alamun tazo ganin Hakan yasata da saurin qarasawa ta riqe hannunshi ya zaunar daita gefenshi


Dora kanta tayi a kafadarshi tafara sheshekar kuka ahankali Hakan yasashi dan rungumota a jikinshi yana rarrashinta ahankali


Saida ta dan tsagaita kukan nata sannan daddy yace
"am sorry shaleleta, nine ko?"


Ahankali ta girgiza kai
"nice daddy"


"bake bace, nine. I shouldn't have yell at you" yafada yana shafa kanta ahankali cikin sigar rarrashi


"A'a daddy, duk ni naja ai, da ban biyemashi ba Amma naji haushi ne dayace wai beson Africans bayan shima African din ne
Shiyasa nikuma nace mashi bana son wanda baya kishin kansa bare asalinsa don ni bana masu kallon mutane, shikenan fa abinda nace" tafada cikin muryar kuka


Murmushi daddy yayi ya sake rungumota a jikinshi
"na yarda dake daughter don baki yimin qarya, I know you amma kuma shima ai ba qarya yayi ba, baki fito fili kika kirashi da dabban ba amma shi ya gane abinda kike nufi tunda ba qaramin yaro bane, idan bakayima mutum kallon mutum ba To kallon dabba zakayi mashi cikin dayan biyu amma babu komai, karki damu nima dazu don raina ya 6aci ne shiyasa kikaga nayi reacting haka amma kar Hakan ya dameki, komai ya wuce, shima Alhaji Abubakar din be dauki abin da zafi ba tunda ko dazu muna tare dashi, so no need to worry"


Dagowa tayi ta kalleshi da watery eyes dinta fuska a marairaice tace
"daddy ka yafe min?"


Dariya daddy yayi
"ni dama ai bakiyimin komai ba, kima bar damun kanki kinji, pretend nothing happened"


Murmushi tayi cikin jindadi taqara kwantar da kanta akan kafadarshi tana lumshe idanu shikuma yayi mata kiss a tsakiyar kai sannan ya maida hankalinshi ga kallon dayakeyi


Shiru dakin ya dauka na wani lokaci babu abinda ke tashi dakin sai muryar yar jaridar dake karanto labaran duniya cikin t.v din.


Daddy hankalinshi kacokam yana kan news din itakuma zee saqa da warwara take akan yadda zata tado maganar Deen Amma takasa sanin ta ina zata fara


Haka sukaita zama har Saida aka gama news din

Ganin dai wannan shine daidai lokacin daya kamata ta tado maganar don mummy na iya Shigowa a kowanne lokaci yasata dan muskutawa ta daga kanta daga kafadarshi

"yadai? Barci ko?" inji daddy cikin kulawa

Murmushi kawai tayi sannan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login