Showing 111001 words to 114000 words out of 322641 words

Chapter 38 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6192

gari naita yawo aciki_

_na dinga lura da al'adun ciki_

_nakoyi yaren dasuke aciki_

_nai jama'a da mutanen dake ciki_"

"akwai wani abu da ake kira kafiya a waqa, shine ya kasance duk baitin waqarka ya dira lafiya lau, so samu ma ace duki kalmar qarshe tazo daya na wadannan baitikan misali a wadancan baitikan dana kawo kaga duk (ciki) shine kalmar qarshe, yana iya zama (ki) din qarshe ma duk ana iya yin Hakan saboda waqar tatafi a tsari takuma bada taste"

(duk inda nayi kuskure a wajen bayanin waqa acan sama๐Ÿ‘†๐Ÿป ayimin afuwa.
Qarfin hali ne kawai na marubuci, babu abinda nasani a waqa โ˜น๏ธ kawai dai hasashe na ne kuma saboda labarin ya ta'alaqa dashi shiyasa na sakoshi ciki, so mawaqa Ayi hqr ๐Ÿ‘ na shiga gonar da batawa ba๐Ÿ˜ waqar ma Dakyar nake hadata ๐Ÿ˜† donma a rubuce na, da na saurarone da babu kanta๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ?)


Deen da tunda tafara bayanin ya juyo yana sauraronta harta kai aya ya Kada kai yace
"ok, bari nasake gwadawa"

"ok gwada" inji zee dake readyn cin Dariya

Qara gyaran murya yayi yace

_saina siyawa kaka tsaraba dayaWA_

_ciki harda ku6eWA_

_harda alaWA_

_sai na hau abin haWA_

_nadawo gida ina.._

Shiru yayi ganin baitin bazai qare da WA ba

Saiya sake cewa

_nadawo gida ina riqeda ledar ku6eWAR_


Atare suka shiga yin Dariyar wannan karon don shi kanshi yasan he sounds so funny


Suna cikin haka wayar zee tayi ringing


Zaro wayar tayi ta duba mai kiran taga Aunty Feenah ce

Dan wara idanu tayi don ita shaf tama manta yadda sukayi daita

Daga wayar tayi ta kara a kunne tayi sallama cikin muryar da Dariya bata gama saki ba

"gamunan waje karki 6atamin lokaci" taji Feenah tace daga dayan 6angaren

"to Aunty, gamunan zuwa"

Kittt suka katse wayar Atare

Kallon Deen dake kallonta shima tayi

"kaga na manta ko?"

"menene?"

"Wata Aunty ta ta Ruma tazo tun ranar friday, to a schedule dinta gobe zata koma amma saboda wani abu daya taso cikin gaggawa shine tafiyar tadawo yau, ni kaina ban sani ba don Saida nazo school sannan ta kirani ta gayamin shine nace bazata tafiba sai tazo munyi bankwana, kaga har tazo ma"

"ayyah" yafada a gajarce yana murmushi

"muje muyi mata bankwanan"

Dan wara idanu yayi yace
"ni kuma? No kije zan jiraki"

6ata fuska tayi
"why? Yanzu fa zamu dawo"

"but.."

"shikenan kawai" tafada tana tashi alamun ranta ya 6aci ta dauki jakkarta ta rataya

Ganin Hakan yasashi tashi shima don kwata2 beson 6acin ranta, ko yaya yanayin fuskarta ya chanza sai yashiga damuwa


Dama tasan idan yaga tayi fushi zai taso Hakan yasa ta danyi murmushi a cikin zuciyarta

"ok mutafi a gaisuwa ce ko?"

Kada kai kawai tayi


"ok muje" yafada shima yana rungume littatafanshi a qirji



Tare suka jera suna tafe suna fira gwanin sha'awa kowanne da murmushi a fuskarshi


Saida suka fita wajen gate don motar na waje

Motar suka hanga daga gefen titi na dama, dukda zee tayi mammakin ganin ba tasu bace haka suka nufeta don ganin ko sune.

Tun kafin su qaraso murfin bangaren driver ya bude wani kyakyawan Saurayi yafito daga ciki

Dan wara idanu tayi
"Yaya Auwal?"

Murmushi saurayin yayi yace
"na'am diyarmu?"

Daidai nan itama Feenah ta Fito daga bangaren mai zaman banza

"Ina wuni yaya Auwal"

"lfy qalau lumi yar daughter mu, kin ganni kamar daga sama ko?"

Kada kai tayi tana murmushi


"zuwa mukayi daukar gimbiyar, mun samu Dakyar an sahale mana muzo" inji saurayin wanda ga dukkan alamu yanada faran2 sosai

Dan hararar shi Feenah tayi tana dan 6ata fuska cikin salo

Murmushi zee tayi tace
"aikau dai yaya, kuma dama kun rabu da shigowa k.t kunga har zuminci sai ayi"

"ashe kin gane, yar daughter mu" injishi yana Dariya

"ya karatu?"

"alhamdullilah yaya, ya aiki"

"gashinan munata fama wlh, wannan abokin nawa fa?" yafada yana kallon Deen dake baya yana sauraronsu

Sai a lokacin Deen ya dago fuskarta dauke da murmushi yayi musu sallama

Atare suka amsa suna maida mashi martanin murmushin

"Yaya Auwal, Aunty Feenah meet my course mate Deen, Deen wannan itace Aunty ta sai yayana"

Fuska dauke da murmushi ya gaidasu calmly sukuma suka amsa suma murmushi a fuskarsu sai kallonshi suke

"ya karatu, fatan za'a qara tighting belt"

"insha allah brother" inji Deen

"to allah ya taimaka, daughter mu zamu wuce" inji Auwal yana dan sunkuyawa ya ciro ledar dayayi mata siyayya ya miqo mata

"gashi Ayi manage"

"kai yaya, harda hidima? Thanks so much" inji zee tana amsa

"Don't mention" yafada yana komawa cikin motar

"to sai munyi waya ko?" inji Feenah tana dan kashe mata ido alamun akwai labari

"to Aunty a gaida kowa da kowa, ace nayi missing dinsu"

"eh, tunda ni yar aikenki ce ba?" tafada itama tana shigewa ta zauna

"pleeease" tafada cikin marairaicewa

"ok amma ba don halinki ba" tafada tana harararta

"eh babu komai" inji zee tana maida mata kofar ta rufe

Tada motar Auwal yayi nan suka shiga daga ma juna hannu harda Deen, Auwal yaja motar suka tafi

Ajiyar zuciya zee ta sauke sannan tajuyo ta kalli Deen

"how was that?"

"nice, they're so nice"

Murmushi kawai tayi suka juya suka koma ciki

Sallah duk suka wuce suka farayi sannan dik suka shiga class kasancewar suna da lecture a lokacin

Saida suka fito sannan suka zauna suka ci kayan da Auwal ya ba zee dukda Deen be wani ci sosai ba

Suna haka akazo daukar zee sukayi sallama ta tafi sannan shima ya fito ya samu abin hawa shima ya tafi


***


*10:15pm*


Kwance zee take kan gado wayarta a hannunta tana danne danne sai murmushi take akai akai da alamun abinda takeyi da ita na bata sugar

"hmm Aunty Feenah, wannan rudewa haka?" ta tura

Can sai message yashigo kamar haka

"wlh zee gayen yayi ๐Ÿ‘Œ๐Ÿป wai kinga sadda kuka jero? Yadda kikasan romeo and his juliet๐Ÿ˜"


"๐Ÿ˜†๐Ÿ˜† dama kin sansu a kammani ashe?"

"baki da labari ashe ๐Ÿคจ"

"banida โ˜น๏ธ"

"to saiki sani tun yau ๐Ÿ˜ ashe dai dama da walakin goro a miya ๐Ÿค” haba dole ai ki rude ki gigice, taga dan fari kyakyawa ๐Ÿ˜’"

"kai Aunty, duk kyawunshi ya kaini๐Ÿ˜Ÿ"

"๐Ÿ˜ณwa? Ke? ๐Ÿคฎ๐Ÿคฎ๐Ÿคฎ"

"๐Ÿ˜ฉ๐Ÿ˜ฉ๐Ÿ˜ฉ"

"kyaji dashi ๐Ÿ˜’, Gaskiya maganar Gaskiya kun dace, ya kamata kuyi ku daidaita junanku hakanan, Ca6 you'll make a perfect match, na so naga 'ya'yanku๐Ÿฅฐ"

"kai Aunty ๐Ÿ™ˆ๐Ÿ™ˆ๐Ÿ™ˆ"


"munafuka, anaso ana kaiwa market ๐Ÿ™„"

"kai Aunty ๐Ÿ˜ซ"

"yanzu dai kuyi ku daidaita junanku musha biki๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ"

"kai Aunty ๐Ÿ˜Ÿ nifa yarinya ce haryanzu ๐Ÿ˜”"

"sannu jaririya ๐Ÿ˜• ai naga ko yayeki ba'ayi ba"

"๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜"


"yar rainin sense kawai, ki gaida yaya da daddy, ni zan sauka, barci ๐Ÿฅฑ"


"tun yanzu ๐Ÿ˜ณ yau babu wayar ๐Ÿ‘‰๐Ÿปโค๏ธ ne?"

"ungo nan ๐Ÿ–๐Ÿป๐Ÿ˜ก"


Dariya zee tayi a zahiri ta turamata

"๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€"


Sannan ta rufe datarta ta koma ta kwanta rigingine ta jawo pillow ta rungume

Tunawa tayi da dramarsu ta dazu na koyan waqa

Murmushi mai sauti tayi ta murgina tsakiyar gadon ta rungume pillon gamm a jikinta



_*DEEN*_ tafada cikin shauqi da begen mammalakin sunan... โœ๏ธ



Ummin fasihu ๐Ÿงš๐Ÿปโ€โ™€๏ธ?
8/2/21, 9:36 PM - Buhainat๐Ÿ˜: *๐Ÿ™๐Ÿปโ€โ™‚๏ธDEEN ๐Ÿ™๐Ÿปโ€โ™‚๏ธ?*









*039*






*SIRRIN ZUCIYA โค๏ธ*






Akwana a tashi gashi har su zee sun qulla wata kusan biyu da resuming school


Komai yana tafiya masu daidai kuma sosai suka maida hankalinsu akan karatunsu musanmman ma Deen dake final year

Yana da burika dayawa dayake son cikawa a duniya ciki harda inganta rayuwarsu shi da kaka, most especially ma kaka saboda ita ta tsaya mashi kai da fata wajen karatunshi don kusan dik abinda tasamu nan suke tafiya saboda ta yarda karatu shine gatan mutum kuma ko ba dade ko ba jima zasuci gajiyar shi shiyasa bata wasa da abinda ya shafi karatunshi komai tana iya badawa muddin akan karatunshi ne

Shiyasa shima a nashi bangaren be sanyo wasa ko shiririta a bangaren karatunshi

Yanada burin zama wani abu a duniya ta dalilinshi yadda zai tallafi rayuwar kaka kamar yadda ta tallafi nashi


A 6angaren zee kuwa jiya-i-yau.

Haryanzu tana nan tana dakon soyayyar shi a zuciyarta

Kullum sonshi qara hauhawa yakeyi a zuciyarta kamar yadda kullum shaquwarsu ke qara qarfi


Sosai take azabtuwa da soyayyar shi datayi mata bake bake a zuciya Saidai haryanzu shiru a ta bangaren Deen Saidai akwai signs da symptoms na soyayyarta dayake nunawa amma that wasn't enough, so take ya furta mata, abinda taga bashi da niyyar yi kwata2.


A bangaren Feenah kau biki sai qara gabatowa yake don yanzu bekai wata daya ba, ata kowanne bangare shirye shiryen bikin akeyi musanmman ma bangaren Amaryar kasancewar itace auta shiyasa ata koina ake nuna mata gata.



***


Yau asabar, babu school don haka yini tayi a gida tana hutu

Fitowa tayi daga dakinta dauke da wani dan bowl din tangaran wanda tagama shan fruit salad cikinshi ta fara tako stairs don sauka qasa ta maida


Muryar mummy da daddy taji suna magana da alamu fira sukeyi

Murmushi tayi ta cigaba da saukowa Saidai maganar dataji mummy tayi yasa tafara slowing tafiyarta

"Gaskiya ne, nima dama nayi wannan tunanin, kaga Feenah tun tana makaranta ta tsaida miji, gab da zata gama kuma akasaka rana kaga yanzu duka watanta biyu da gamawa nan da yan satittika asha biki, me yafi wannan? Wlh zaman ba yi bane gwara da angama Ayi auren don shine mutuncin ko wacce 'ya mace dama namiji ma

Kuma idan akace sai an gama karatun sannan za'a samu mijin yaushe za'ayi kenan? Gwara tun yanzu asa sanwar abin bare kai dama ita kenan daya, kowa ya dauko idanu ya zuba maka yaga yadda zakayi

Ni sai inga Hakan shi yafi kawai"

Tsayawa zee tayi takasa qarasowa tana jujjuya maganar mummy cikin son gane inda ta dosa


Daddy taji yana cewa
"nima haka nagani wlh Maimuna, gwara afara tun yanzu. Gashi yaron yanada tarbiyya don nasanshi sosai, muna Yawan hadewa idan naje gidansu ko kuma wasu lokutan idan sunzo tare da baban.

Kuma bayan wannan kinga zumunci zai qara qulluwa, amintarmu da babanshi zai qara qarfi kuma bazanyi fargabar wani abu yasamu diyata ba don ko babu ni a duniya nasan Alhaji Abubakar mai iya riqe amanar iyalaina ne"


Kan zee yaqara kullewa

Tabbas tasan Alhaji Abubakar, babban aminin daddy ne kuma abokin kasuwancinshi.

Sau dayawa shida iyalanshi suna zuwa nan ziyara suma suna zuwa gidanshi Saidai zee bata cika son zuwa ba don yaran gidan mugun yan zafin kai ne, girman kansu yayi over shiyasa basa shiri don kamar yadda suke jinsu su wasu ne haka itama ke jin kanta shiyasa basa shiri sam

"wlh kam, to yanzu yakusan dawowa ne?" inji mummy

"eh, ga yadda muka tattauna dashi Alhaji Abubakar din cewa yayi yagama komai kawai sai yan ide ide, nan da wata daya nasan yadawo, to kinga me ake jira? Aiki dama akwai shi available shi dama yake jira, kinga a lokacin saisu fahimci juna da tashiga level 400 din sai asaka rana tana gamawa sai asha biki, ko yaya kika gani?"

"Gaskiya Hakan yayi Alhaji, kaga zamu sauke dukkan nauyinta akanmu, ga ilimi mun bata kuma mun aurar daita a lokacin daya dace, dama ni na matsu naga anyi Hakan saboda ita 'ya mace ce kuma duk inda hankalin iyayen 'ya mace yake to bazai ta6a kwantawa ba sai sunga sun rabu daita lafiya ta hanyar aurar daita. Allah yasa Hakan shi yafi alhairi kuma allah ya daidaita su kasan diyar taga yar tutsu ce wani sa'in"

Dariya daddy yayi
"ai karki damu, insha allah zaiyi mata 100%, nifa nasan taste din diyata, nasan abinda zataso da abinda bazata so ba kuma am betting you, zaki gani. Da hannu bibbiyu zata amshi tayin bari dai lokacin yayi"

"to allah yasa, ka dai san ba'a shaidar 'ya'yan yanzu, bare wannan diyar taka mai shegen ruwan ido, kana ganin yadda masu neman ta ke zuwa take musu wulaqanci, duk wanda yazo saita nemi makusanshi ta kushe, nayi fadan nayi nasihar a banza"

Dariya daddy yasake yi
"ai jewel din kenan, ita allura ce cikin ruwa, mai rabo ka dauka kuma *Asad* shine mai rabon don dama don shi taqi sauraron kowa, nasan diyata kuma nasan abinda takeso don hakama yasa nasan da Asad zasu dace, kuma zaki gani"

"to allah ya tabbatar da alhairi ai haka akeso" inji mummy cikin farinciki

"hmm kaji su Hajiya Maimuna an kusa zama in-law" inji Alhaji cikin tsokana

Dariya tayi tana juya idanu wanda a wurinta zee ta gado nata

"Ato, kana black stomach ne?"

"A'a, namafi kowa white stomach" yafada shima yana kwaikwayon juya idanun datayi

Dariya duk sukayi mummy na cewa
"to allah dai ya tabbatar mana da alhairi"

"Amin summa amin" inji daddy



Ahankali zee ta juya tafara taka stairs din don komawa batareda tayi motsin dazasu lura daita ba

Bude kofar ta tayi ta shiga sannan ta rufo ta taho ahankali kamar marar lakka ta ajiye bowl din hannunta saman bedside locker ta zauna ahankali gefen gadonta


Shiru tayi tana kallon Kaffafuwanta dake bisa dan carpet din dake gaban gadon kamar anan zataga amsoshin tambayoyin dake tsere a kwalwarta


*kinga a lokacin saisu fahimci juna, da tashiga level 400 sai asaka rana tana gamawa asha biki*
Maganar daddy ce tadawo mata a qwanya


*nasan abinda takeso don hakama yasa nasan da Asad zasu dace*

Wai wa yake magana akai? Waye kuma Asad? Wacece zasu dace dashi?

Hadiye wasu yawu dasuka taru a maqoshinta tayi


Me suke nufi? Tadai san basuda wata 'ya bayan ita kuma taji suna maganar sauke nauyi ta hanyar aurar da 'yar su

_Ni kenan?_


Sai kuma ta girgiza kai

_no this is impossible!_

_it can't be_

Waye wani Asad kuma? Suna ko gishiri babu.

Ca6 dasake wlh, yanzu yanzu ba sai anjima ba zataje tagayawa daddy don karma ya wahalar da d'an mutane wajen zuwa don Hakan bazai ta6a yiwuwa ba don tanada wanda takeso


Zumbur tayi tasake tashi ta nufi kofa

Harta dora hannu akan handle saita kuma dakata

Idan taje me zatace mashi?

"daddy Gaskiya ni banason wannan Asad din, inada wanda nakeso"

Sai yace
"waye?"

Me zatace?

Deen? Deen zata ambata?


Mutumin da har yanzu batasan matsayinta ba a gareshi?

Idan tace Deen din ne yakuma nemi ya ganshi me zatace?

Cewa zatayi ita ke sonshi? Ko cewa zatayi jiranshi take taji matsayinta a wajenshi?


Ahankali ta saki handle din

Tabbas tasan daddy, takuma san idan yayi farinciki to yaga tayi ne

Idan tace mashi bata sonshi bazai gardama mata ba don tasan bazai ta6a yimata dole ba

Amma shi wanda zatayi Hakan akanshi tanada tabbaci akanshi?

Tanada tabbacin yana sonta?


Ahankali takoma da baya2 ta lulubi stool din dressing mirror dinta ta zauna akai


Tasan idan tace bata son wanda suke magana akai zasu nemi sanin wa takeso, idan tace babu bazasu yarda ba musanmman mummy da dama burinta taga tayi aure kuma ga yadda taga ta nuna amincewarta sosai akan wannan maganar da wuya ta barta ta tafi a iska

Idan kuma tace tana da wanda takeso zasu so sanin ko waye, idan ta ambaci Deen zasu so jin ta bakinshi, idan kuma sukaji cewa bema san da maganar ba me kenan?


Hannuwa takai bisa kanta ta cusa yatsunta cikin lallausan gashinta tana maidasu baya sannan tayi interlocking din yatsunta bisa wuya


Anzo wajen!

Anzo ga6ar da take gudu


Lumshe idanuwanta tayi ahankali tana jin baqinciki na mammaye zuciyarta


Har zuwa yaushe? Har zuwa yaushe zata cigaba da jiran shi? Har zuwa yaushe zata cigaba da dakon soyayyarshi? Har zuwa yaushe zata cigaba da wahala


Ranta taji ya 6aci, zuciyarta ta dagule, jitayi kamar taita ihu don takaici.

Dama tasani, wannan slowness din nashi wahala zai bata, dama tasan saita fara zaucewa sannan zai bayyana mata sirrin zuciyarshi.



Haka ta qarashe Wunin ranar rai a matuqar dagule

Baqinciki, 6acin rai, takaici duk sun taru sun tokaremata qirji wanda Hakan yasa taji babu abinda keyimata dadi a duniyar nan




Haka ta qarashe weekend din wannan satin cikin cinkushewar zuciya, sosai takejin haushin Deen har cikin zuciya, jitake kamar ta sameshi taita duka ko zata huce shiyasa Koda yakirata da marece ranar lahadi kamar yadda yasaba sai bata daga ba sai tasa number shi yadda idan ya bugo zaiga line busy


Da daddare ma ta dade batayi barci ba kamar yadda yake a al'adarta indai akwai abu a ranta yakan hanata barcin kirki

Haka taita juyi kafin tasamu dakyar wani barci marar dadi ya dauketa




*WASHEGARI*





Zaune take a library wani qaton textbook a gabanta tana budewa ahankali page by page

A zahiri sai kayi tunanin wani abin kirki takeyi amma maganar Gaskiya ita kanta batasan me take dubawa ba, hankalinta da tunaninta yayi wani wuri daban



Deen ne yashigo library din, waige waige yadan farayi na ganin inda zai ganta sai ya hango ta can qarshen dakin

Murmushi yayi sannan ya nufo inda take cikin tafiyarshi ta nutsuwa

Tunda yashigo ta ganshi amma tayi kamar bata ganshi ba, haushin shi takeji kamar me? Jitake kamar ta tashi taita zazzagamashi abinda ke cin ranta

Tanajin Qarasowarshi amma bata dago ba harya ja kujerar dake facing dinta ya zauna


Sa hannu yayi ya rufe littafin data kafama idanu kamar mai karatun gaske, yana cewa
"hey... Book worm"


Sai a lokacin ta dago ta kalleshi da alamun bazata a fuskarta

"oh! You scared me"


Yar Dariya yayi yace
"ai kece hankalinki na kan Littafi baki jin ko motsin mutane, meye kike karantawa?" yafada yana juyo da littafin gaban shi yadda zai gani

Dan daga kafadu zee tayi tace
"just going through topic da mukayi jiya"

Kada kai yayi yana maida mata littafin shima ya doro nashi littatafan a sama

"good, how's your weekend?"

"Alhamdullilah" ta amsa a gajarce tana sake jawo littafin daya maido mata gabanta tana cigaba da dubawa


"meya samu phone dinki jiya?" yafada shima yana zaro wani littafi a tsakiyar littatafanshi


Zee da maganar nan ma datake yi duk dauriyace don ita tasan me takeji a zuciyarta ta dago ta kalleshi sannan ta daga kafadu
"babu"

"but nayita kira bata Shigowa saima line busy dayaita nunawa"

Qara daga kafadu tayi batareda ta dagoba tace
"qila lokacin waya nake"


"amma fa na dade ina kira tana rubuta Hakan har da daddare ma"

Qara daga kafadu tayi in an I don't care manner tace
"yeah, ina waya ne"

"wow! Da wa? Irin wannan dadewa haka?"

Dagowa tayi tadan yimashi murmushi
"kayi mammaki ne?"

"sosai ma"

Murmushi taqara yimashi tace
"to ka daina"

Shiru yadanyi yana kallonta

"and who is that if I may ask" yafada yana dan bubbude littafin daya ciro


*"my man"*


Cak ya tsaya da bubbude pages din dayake kamar


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login