Showing 213001 words to 216000 words out of 322641 words

Chapter 72 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4299

wannan mace ce kuma tadan manyanta)

Qarasowa zee tayi ta fada jikin Ummie taqara Fashewa da wani sabon kukan

"subhanallilah! Ya bunatie, meya faru?" tafada a rude tana tashi daga kishingiden datake

Cigaba da kukanta Aysha tayi tana qara qanqame Ummin

A rude Ummie ta cigaba da Tambayar Aysha meya faru cikin harshen larabci hankalinta duk ya tashi, tuni maids din dakin suka shiga sulalewa daya bayan daya suna fita


Dakyar Aysha ta samu ta tsagaita kukanta, cikin larabci tashiga cewa
"Ummie, yaya ne"

"yaya? Meya faru dashi?" ta tambaya hankali tashe

Girgiza kai Aysha tayi tace
"kawai daga zuwa saiyasa aka kama bestie ta da ita da yayanta akaje aka kulle" tafada cikin kuka


"aka kulle? Bangane ba"


"Ummie, wannan qawar tawa danake baki labarinta? Itace yau yaya yazo school don ya ganta don kodayaushe cikin matsa mashi nakeyi yazo ya ganta shine yau yazo amma daga zuwa sai suka kama fada wai spy ce tana spying dinshi ne wai don ya ganta wasu wuraren kafin nan, shine ita tace ba spy bace shine yaji haushi zai mareta sai yayanta yazo From nowhere ya tare sai fadan yakoma kanshi sai yasa aka kamasu aka kulle"


Tunda tafara maganar ummie bata fahimci ko kalma daya nata ba din a dunqule take bata labarin Hakan yasata zama so confused

"look Aysha, ki nutsu. Ki fadamin komai cikin kwanciyar hankali yadda zan gane"

Kada kai Aysha tayi tana share hawayenta da bayan hannu

"to ina jinki yanzu, wace qawarki kike cewa?"

"wannan wanda nake baki ku gaisa?mai sunanki"

Kada kai ummie tayi cikin gamsuwa
"eh nagane, takwarata? To meya faru?"


Cikin nutsuwa Aysha tashiga bata labarin abinda yafaru From A-z


Ajiyar zuciya ummie ta sauke tana dan dafe kai

"ya sallam, yanzu shikenan duk wanda ya ra6eka yazama abokin gabanka? Wannan wane irin hali ne ga bunnaya?" tafada cikin rashin jin dadin abinda yafaru

Qara share hawayenta Aysha tayi tace
"ummie nayi qoqarin fahimtar dashi itama tayi qoqarin fahimtar dashi amma yaqi ya saurari ko daya daga cikinmu, ita batama san shine Mussadiq al-hassan ba, batasan status dinmu ba don ban ta6a gayamata ba kawai nadai bata labarin mu ne in a simple way bance nice qanwar mussadiq al-hassan mai companies din Nurul-haqq ba, tayaya to zatayi mashi leqen asiri mutumin da batama sani ba, ni babu abinda yafi dagamin hankali kamar idan na tuna yanzu haka suna can kulle" tafada cikin kuka


"kiramin shi a waya, wannan abin nashi yafara wuce gona da iri, shikenan kowa saiya dora mashi alamar zargi? Soyake ya hana kowa mu'amalla da kowa kamar yadda ya hana kanshi? Kiramin shi"


"ummie kinsan bazai daga ba, ki kirashi da wayarki zaifi saurin dagawa"

"miqo min ita gatacan bisa cushion, wai ina ma yake shi?"

Aysha data tashi da sauri zata dauko ta amsa da
"ya dai ajiye ni yatafi"

"badai gudu yake ba kamar yadda yasaba, ya tafi da driver?"

"bana tunanin Hakan, can dai shikadai yazo"


Amsar wayar ummie tayi daga hannunta tayi dialing din number ta kara a kunne


Ringing daya biyu aka daga

Daga can 6angaren sukaji muryar mussadiq yana cewa
"Aslm alaiki ya ummie"

Dan Hade fuska ummie tayi wanda yayi mugun yimata kyau kamar dai yadda Deen keyi
"wslm, ina kake?"

"ina wani aiki ne ummie"

"wane aiki? Aikin kama mutane da basuji ba basu gani ba?"

"Ummie waya..."

"kazo kasameni gida yanzu yanzunnan, fatan kajini" tafada in warning

Cikin amsar umarni yace
"to Ummie"

Katse kiran ummie tayi sannan ta cigaba da kwantar ma autar tata hankali akan ta kwantar da hankalinta komai zai warware




Sai gashi ko minti tallatin ba'ayi ba ya iso gidan

"bunnaya, me kake so kazama ne? Shikenan kowa ma abokin gabarka ne? Shikenan kowa ma bazai ra6eka ko ya ra6i wani naka ba? Wannan wane irin aqida ne?"


"ummie mutane ba abin yarda bane, maqiyi bazai fito da pasta manne da goshi na rubutun shi maqiyinka ne, kowa na iya zama maqiyinka"

"kai shikenan baka kyautatawa kanka zato? Kalleka.. Bakada aboki ko daya saboda rashin yarda, yan uwanka ma baka zuminci dasu yadda ya kamata, kowa.. Kana iya yiwa kowa kallon maqiyi.
A dalilin Hakan yasa baka bayyana kanka, anfi sanin sunanka fiyeda kai kanka, yan tsiraru kawai suka sanka, kana iya zuwa wuri kayi hidimarka kafita ba'asan dakai ba Amma dukda Hakan zargin kowa kake, anya wannan hanyar daka dauko mai 6ullewa ce?"

Shiru yayi

"Nan gaba waya sani qila har muma zargin mu zaka dinga yi, a dalilin wannan halin naka ko budurwa baka ta6a yi ba, ga yanmata nan masu sonka a cikin families dama abokan arziqi amma kai bama ta aure kake ba, mussadiq nima inason ganin jikana, inason ganin jininka dana Aysha kafin na mutu dukda ita mutuwa bata ga babba bata ga yaro saita dauki yaro tabar tsoho amma ai ko babu komai anfi sama babban ran fara tafiyar, mussadiq Koda banga 'ya'yanku ba zanso ganin auren ku"

Jikin mussadiq yayi sanyi, dama haka yake kuma ummie tasan lagonshi data ambaci mutuwa sai komai nashi ya sure, ya tsani ummie takira ma kanta mutuwa sai yaji kamar da gaske din tafiya zatayi ta barshi kamar yadda mahaifinsu da dan uwanshi sukayi

Dagowa yayi ya kalli ummie
"ummie kibar fadin haka don Allah"

"to ai Gaskiya ce bunnaya, kowanne mai rai saiya dandani mutuwa, kuma ita wannan yarinyar ni kaina na santa don muna Gaisawa da ita ta waya, da ba alhairi bace ba agareku da naji Hakan a jikina, tun magana ta daita ta farko ta kwanta mun, be kamata kome yazo kanka ka yanke hukunci dashi ba"

"ummie sau uku kenan nake haduwa daita..."
Nan ya fayyace musu yadda duk haduwarsu ta kasance

"bunnaya, akwai coincidence, bayan Hakan wata haduwar ta allah ce kuma alhairi ce, ta yiwu allah keta hadaku wataqila yanada wata manufa akanku amma kayi bincike, abinda ya kamata kayi kenan tun farko bawai kaita zargi ba"

"nafara, yanzu haka school din nakoma nasa an daukomin file dinta, muna tsaka da Hakan kuka kirani"

"yauwa, bincike ya kamata kayi saika kamata dumu2 da hujjoji sannan zaka yanke hukunci bawai ka yanke hukunci akan zargi ba
Yanzu kasa a sallamesu ka kuma basu haquri inyaso sai ka cigaba da binciken ka akansu

Insha allah babu wani mugu dazai ra6eku, kodayaushe kuna cikin addu'o'ina dare da rana, kuma zaku cigaba da kasancewa cikin addu'o'ina, insha allah babu mugun dazai ra6eku"


Kada kai mussadiq yayi cikin gamsuwa


Cigaba dayi musu nasiha tayi mai ratsa jiki kamar yadda tasaba yimasu sannan ta sallami mussadiq akan yaje yasa asake su.





***



A can gidansu Aymaan kau hankalinsu duk ba a kwance ba, driver yaje daukar zee Saidai batanan, duk inda ake saka ran ganinta a fadin makarantar ba'a ganta ba

Ga shima Aymaan wayarshi bata shiga kamar dai ta zee

Kuma sun kira Ahmad sun sanar dashi yaje asibitin ance shima ya dade da fita

Haka dai Ahmad yaita yawon nemansu musanmman ma zee da ba koina tasani ba a garin, ga numbobinsu basa shiga Hakan yaqara dagula masu lissafi.






*AYMAAN/ZEE*






Suna zaune Jigum Tundazu abin duniya ya ishesu musanmman zee take jinta a matuqar takure

She can't believe wai yau ita aka rufe a custody dukda ba irin wannan rufewar bace ta wulaqanci

Tunda nan Wajene mai tsafta ga fili ga fresh air don akwai fankoki masu bada iska sosai aciki ga abinci mai kyau da aka basu Tundazu wanda haryanzu babu wanda ya kalleshi gashi babu duka babu zagi don tunda mutanen nan suka fita banda wanda yakawo musu abinci babu wanda yaqara Shigowa

Saidai kullewa kullewa ce Koda a cikin gidan aljannar duniya aka kulleka, dole wannan right of movement din da aka tauyemaka ya dameka


A 6angaren Aymaan kau abin yafi 6ata mashi rai, shi ba kulleshi din ba yafi 6ata mashi rai wanda yasa aka kulleshi dinne

Gani yake bekai wannan matsayin ba, gani yake qasqanci ne Hakan mutum kamar mussadiq yasa a tsareshi dukda kau yasan ya isa yasa ayimashi fiyeda Hakan ma kuma ayi din babu yadda ya iya

Amma ya rasa meyasa tun haduwarsu ta farko yaji baya son gayen, yana jin haushinshi fiyeda tunani shiyasa yake ganin tsareshi da akayi ta dalilin shi ba qaramin qasqanci bane a gareshi



Suna ahaka sukaji ana bude kofa


Babu wanda ya dago acikinsu bare ya kalli mai shigowar


"kuna iya fitowa" inji wanda yashigo din

Dagowa sukayi atare suka kalli mutumin sai kuma suka kalli juna da alamun tambaya

"you're free, zaku iya fitowa"


Wata nannauyar Ajiyar zuciya zee ta sauke tana jin sanyi a zuciyarta shikuma Aymaan yadan ta6e baki alamun ko ajikinshi


Atare suka tashi suka fito

Ce masu yayi su biyo bayanshi sukayi yadda yace harya kaisu wani office daban

Ce masu yayi su shiga suka shiga shikuma yafito ya rufo kofar yayi tafiyarshi


A tsaye yake jikin window yana kallon waje ta window din hannayenshi zube a aljihunshi


Wani qululun baqinciki ya sake tokare Aymaan, da yasan shi zasu gani a office dinnan da babu abinda zai sashi Shigowa


Ahankali mussadiq ya juyo yana kallonsu still hannayenshi zube a aljihu


Shiru ya ratsa dakin na wasu daqiqu babu mai uhm bare uhm uhm


Can saiya tako ya dawo kusada wani table din office din yadan jingina dashi yana dora hannu daya akan desk din


"seems yau ma is a Lucky day for you guys, Saidai rana 99 na 6arawo rana daya kuma na meshi, ku tafi amma idan kere na yawo zabo na yawo zasu hadu Saidai ku kuji haduwarmu ta gama don it gonna be worst"


Atare suka ta6e baki kamar hadin baki

Aymaan na shirin magana zee ta rigashi

"a juri zuwa rafi dai, kuma am assuring you wannan tsaremu dakasa akayi na few hours saikayi regretting dinshi, saiyasa watarana ka kasa hada idanu damu

Mutum darajja gareshi kowanne mutum da baiwar da allah yabashi wanda sai an taqa zai gane Hakan

Kayi amfani da matsayinka ka tsaremu, to kajira ranar da kai kanka kunyar kanka zaisa ka kasa daga idanu ka kallemu straight in the eyes kamar yadda kayi yanzu

A lokacin zaka gane arziqi is nothing don arziqin besa kasamu abinda wadanda ka wulaqanta suka samo maka ba, a lokacin zaka gane kowama da ranarsa kuma gamewar bazata amfaneka da komai ba don it's like crying over a split milk"



Aymaan ne yadanyi murmushi
"haba lil sis, meyasa kike 6ata yawun bakinki har haka? Magana ta hankali mai hankali ake yimawa don shi zaifi ganewa, it's better Kiyi saving din yawunki mai daraja for something more valuable"


Takowa mussadiq yayi gabansu ya tsaya yace
"kamar yadda nafada dazu, you guys are very Lucky, shiyasa har kukeda damar maida yadda akayi yanzu, amma ku guji ranar da Luck din xaibar side dinku cos you'll regret it. Kuna iya tafiya tun kafin Luck din ya fece yabarku tun yanzu"


"kai kalmar Lucky ta cancanta don albarkacin wani kakeci da nasa akowanne daqiqa ka dinga tuna ni cikin qunar rai amma unfortunately bazan iya ba saboda darajar shi dama mai daraja akecin darajar shi" inji zee


"out.. Kun isheni da hayaniya and this is not market, so out!" Yafada yana nuna kofa

"ko baka fadaba, amma ka tuna zuru batacin zuru" inji Aymaan sai ya kama hannun zee suka juya suka fita daga office din suna maido mashi kofar da qarfi


Bïñ kofar yayi da kallo sannan ya sauke Ajiyar zuciya yakoma ya zauna bisa kujerar Wurin mai jujjuyawa yafara jujjuyawa


_the girl_


Meyasa presence din yarinyar kesashi jin wani iri, absence dinta ke dada jefashi wani hali

Meyasa yakasa mancewa da ita tun haduwarsu ta farko

Meyasa yakasa mance fuskarta tun a gani na farko?


Shi ba mutum bane mai yawan maida kai ga kammanin wani musanmman mace amma sai gashi ita tun a ganin farko kwalwarshi tayi capturing face dinta

A haduwa ta farko bayan ya warwatsa mata kudade ajiki yayi tafiyarshi yaji wani yanayi marar dadi kamar yasa ajuya ya koma wajenta


A haduwarsu na biyu ma bayan yatafi yabarsu da cashier gab da zasu sha kwana ya juyo yana kallonta Daga nesa suna barin wajen, nan ma Wannan feeling din yaji kamar ya tsaidata kamar yakoma wajenta


Yanzu ma basu ida fita ba yaji kamar ya dakatar da ita inda Koda dakatar da itan yayi besan me zaice mata ba


Menene Hakan to?

Meye ma'anar Hakan?... ✍️






Ummin fasihu 🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:41 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?*










*067*






*THE UNVEIL*









Fitowa sukayi harabar wajen suka nufi hanyar gate


Aymaan kanshi na kan wayarshi da aka maido masu abinsu dazasu fita yana kunnata

Babu dadewa ta kunnu yashiga contact ya lalubo number Ahmad yayi dialing


Ringing daya biyu aka daga

"ya sallam Aymaan ina ka shiga? Na nemeka kamar zan zauce.." abinda Ahmad yafara dashi kenan yama manta da sallamar


"hmm, ai gashi yanzu kajini ko? Kana ina?"


"ganinan nadawo gidanku daga yawon nemanku, kasan kau zee ta 6ata?"


Dan murmushi Aymaan yayi ya dan kalli zee dake kallonshi shima saita Janye nata idanun


"gamunan tare, kazo ka dauke mu"


Jin sallalamin su ummy da ihun murnar batool yasa yadan Janye wayar daga kunnenshi kadan


"dagaske? Amma kai dan air ne, ina kuka shiga munata neman ku harda hadawa da police station?"


"kazo c.i.d headquarter ka daukemu" be jira amsarshi ba ya katse kiran


Sake kallon zee yayi yaga bashi take kallo ba Amma ta kare goshinta da hannunta saboda hasken rana


Juyawa yayi yaga wasu kujeru qasan wani tent saiya kalli zee yace
"muje can mu zauna mu jirashi"


Kallonshi tayi kamar zatayi magana saikuma tafasa suka wuce inda yace din suka zauna


Shiru wajen ya dauka na wani lokaci

Can zee tadan muskuta wanda Hakan yasa Aymaan Dagowa yana kallonta

Batareda tabari sun hada idanu ba ta fara cewa
"Am sorry.."


Shiru yayi yana kallonta Hakan yasa ta dago idanunta itama ta kalleshi

"for what?" ya tambaya yana kallonta cikin ido


Sauke nata idanun tayi sannan ahankali tace
"I caused it all, duk ni naja komai"


Murmushi yayi mai kyau yace
"bake ya kamata kibada haquri ba.. Nine.

Am sorry nakasa hanaki zama a tsare for some hours"

Dagowa tayi tasake kallonshi cikin wani yanayi sai ta girgiza kai

"nice najamana, naja maka tsarewa na wani lokaci"

Murmushi yayi ya kalli gate daga inda yake zaune

"I can do more than that... For you." ya qarashe yana maido kallonshi akanta

"kawai baqincikina shine kasa kareki danayi daga zaman tsarewar, dani kadai ne ko shekara nawa zanyi bazan damu ba Amma the thought of ke a tsare shiyafi komai dagula min rai... Am sorry"


Sunkuyar dakai kawai tayi batace komai ba sai wasa data cigaba dayi da zoben hannunta


Shima be sake cewa komai ba sai maida hankali dayayi yana hango gate ta inda suke zaune


Babu dadewa motar Ahmad ta iso wajen

Ajiyar zuciya Aymaan ya sauke

"ya iso... Muje" yafada yana tashi tsaye

Itama Dagowa tayi ta hango motar sannan ta tashi tabi Aymaan daya fara tafiya

Har Ahmad ya fito saiya hangosu Hakan yasashi tsayawa


Kofar baya Aymaan ya budewa zee ta shiga ya rufo sannan ya bude ta kusada driver yashiga shima Ahmad ya shiga suka rurrufo kofar, tada motar Ahmad yayi yaja suka bar wajen.




Tafiya sukeyi ahankali cikin normal speed babu mai cewa komai


Can Ahmad ya juyo ya kalli Aymaan da idanunshi ke kan titi


"Aymaan, wai meya faru ne? Meya kawoku wancan Wurin?" yafada yana maida kallonshi a titin

"muje gida sannan" Aymaan ya amsa a taqaice

Ajiyar zuciya Ahmad yayi ya cigaba da tuqinshi


Zee na Jinsu amma batace komai ba sai kallon waje datake ta window din motar


Koda suka isa gida duk su dama ake jira, nan take akayi musu caa akan meya faru, ina sukaje


Saida suka zauna sannan Aymaan yafada masu komai daga inda yaje school din da niyyar daukota har hangosu dayayi a parking space din kamar suna hayaniya da mutumin har Qarasowarshi wajen da yadda fadan yakoma kanshi


Sai aka maida akalar Tambayar ga zee akan me ya hadasu

Nan zee ta gayamasu yadda komai yafaru takuma gayamasu haduwarsu da mussadiq din a supermarket lokacin da suka fita da batool siyo jakka Saidai ta 6oyemasu cewa la6el tayimashi ta dinga binshi abaya, kawai cewa tayi tayi 6atan hanya ne sai suka hade dashi shikuma sai yace shi take bibiya


Kowa mammaki ya cika shi da kuma jimami akan abinda yafaru, cikin masu mammakin harda Ahmad da abin yafi kowa kadashi, lallai ba qaramin tsallake rijiya da baya sukayi ba

Mussadiq? Mussadiq al-hassan yasa akamasu kuma ya sakesu da wuri haka?


Nan su Abbu suka yanke shawarar fidda zee daga makarantar saboda tsaro tunda zuwa makarantar na neman zama barazana agareta, kawai gwara a maida ta school dinsu batool tunda ba'ayi nisa a semester din ba qila a kar6eta


Sosai Batool taji dadin Hakan don Hakan na nufin tare zasu dinga zuwa school kenan kuma zasu dinga yini tare

Cikin wadanda sukaji dadin Hakan harda Aymaan don shima abinda ke ranshi kenan kawai sun rigashi furtawa ne kuma yaji dadin da bashi ya furta din ba


A 6angaren zee kau ba taji dadin haka ba sam, Saidai bata nuna ba, that means tabar makarantar annur kenan? Tabar Aysha?




***




Kwance take idanunta akan cieling din dakin tana kallon design dinshi wanda a zahiri bashi take kallo ba tayi nisa ne a tunaninta


"zee nasan bakiji dadin hukuncin dasu ummy suka yanke ba Amma that's the best solution, tunda mutumin nan ya dora ayar tambaya akanki bazai barki ba, zaita bibiyar ki ne har saikin fada tarkonshi so maganin kar ayi kar asoma gwara kibar musu school din"


Ajiyar zuciya zee ta sauke still idanunta akan ceiling din

"ni ba barin school dinne matsala ta ba, rushewar hanyar cikar mission dina yafi damuna, gashi na shaqu da Aysha, zanyi kewarta"

"hakane amma abinda zaki duba anan shine wannan hukuncin is for your own Good, Ahmad yana yawan bani labarin how dangerous that guy is, yana iya yin komai kuma yaci bulus don yanada both matsayi da kudi da connections, ja dashi ba qaramin kasada bane, batun mission dinki kuma allah zai kawo mana mafita ta hanyar da bama zato kawai mu cigaba da addu'a"


Qara sauke Ajiyar zuciya zee tayi tace
"to allah yasa Hakan shiyafi alhairi"


"Amin summa amin" batool ta amsa


Wayar zee ce tayi Ring


Tashi tayi ahankali zaune sannan ta jawo wayar dake kusada ita kan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login