Showing 216001 words to 219000 words out of 322641 words

Chapter 73 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6140

bedside locker


Dan Wara idanu tayi ganin sunan dake yawo a screen din

Ganin Hakan yasa batool cewa
"waye?"

"Aysha" zee ta amsa tana picking call din


"bestie" inji zee cikin fara'a


Wani irin wawan Ajiyar zuciya zee taji Aysha ta sauke sannan cikin murya Kamar zatayi kuka tace
"ummie na"

"na'am sahibatie"


"wayyo ummie na, nayi tunanin bazaki daga kirana ba Tundazu nake son kira amma fargaba ta hanani"

Murmushi zee tayi tace
"inqi dagawa kuma mezai hanani dagawa?"

"komai ma ummie, am sorry, am very very sorry for what happen dazu, da nasan abinda zai faru kenan da ban fara gayyatarshi ba"


Murmushi zee tasake yi
"Don't be, misunderstanding ne kawai"


"wlh bakiji yadda naji ba a lokacin, laifi na ma ne, nasan halin yaya sarai amma banyi tunanin abin zakai Hakan ba da ko sunanki bazan ta6a ambata mashi ba"

"kinga babu komai, kibar damun kanki, komai ya wuce insha allah" inji zee

"nagode qwarai ummie da fahimtarki, fatan dai komai lafiya, ba'ayi muku komai ba ko?"


"babu abinda akayimana, komai lfy lau"

"yayanki fa? Shima is ok ko?"

"kowa lfy lau, na gayamaki babu abinda sukayimana"


"masha allah, naji dadin jin Hakan... Ga ummie ku gaisa"


Wara idanu zee tayi saita kalli batool da itama ta Wara nata idanun don wayar a handsfree take duk tana sauraron su


"Assalamu alaiki habibty" muryar Ummie mai cike da kwarjini ta daki dodon kunnenta


Hadiye wasu yawu tayi sannan cikin nutsuwa itama ta amsa sallamar ta dora da gaisheta, duk maganar dasuke a harshen turanci suke yinta

"lfy lau habibty, ya gida ya mutanen gida"

"alhamdullilah, ummie" inji zee cikin nutsuwa

"masha allah, ina mai baku haquri akan abinda yafaru tsakanin ku da hussain, Gaskiya banji dadi ba kwata2, abin ya 6ata min rai sosai kuma zan dauki mataki akai kuyi hqr kinji"


"haba ummie komai ya wuce insha allah, dama rashin fahimta ce kawai"


"babu wata rashin fahimta, haka yake. Narasa inda yasamo wannan baqar aqidar, shikenan mutum beda yarda kona misqala zarratin? Ai dazu Saida nayi mashi fada sosai nakuma ya sakeku kuma saina dauki mataki akai"

Murmushi zee tayi cikin jin qaunar matar, da wata ce ko ajikinta bare har tayi tunanin kira ta bada haquri

"babu komai ummie, allah yaqara lafiya"


"Amin, ina Ummin naki?"


"tana dakinta"

"kai mata mu gaisa don Allah"

"to ummie, hold on" tafada tana tashi tsaye ta nufi kofa batool ma ta sauko daga gadon ta maramata baya


A daki suka iske Ummu batool tafito daga bayi da alamu ma wanka tayi


Kaimata wayar tayi

Daga gira Ummu batool tayi alamun waye, cikin rada zee tace mata umminsu Aysha ne

Kara wayar Ummu batool tayi a kunne tayi sallama ummie ta amsa ta dayan bangaren


Gaisawa suka farayi cikin mutunci sannan ummie tayi introducing kanta takuma shiga bata hqr akan abinda yafaru

Cikin fara'a Ummu batool ke nuna babu komai ai komai ya wuce insha allah

Sundan jima suna wayar sannan sukayi sallama ummie ta maido ma zee wayarta

Koda ta maida a kunne sai taji muryar Aysha

Nan take gayamata gobe insha allah zatazo

Da farko zee taso hanata zuwa amma saita nace akan saitazo Hakan sukayi sallama bayan tace zee ta turo mata address dinsu


Kallon Ummu batool zee tayi tana Tambayar ta tura mata din

Cewa tayi ta tura mata din tunda zuminci zatazo babu komai taga alamun suna da kirki sosai kuma kamar basuda matsala

Da Hakan ta turama Aysha address din suka koma dakinsu da ita da batool suna cigaba da firar kirkin ummie da Aysha





Sai gashi washegarin kamar yadda tace zatazo tazo din bayan sallar la'asar


Sosai zee tayi murnar ganinta kuma akayimata tarbar mutunci


Sosai suka gaisa da Ummu batool sannan suka wuce daita sama dakinsu zee

Batool tunda taga Aysha taji itama ta kwanta mata a rai lokaci guda don ko ba'afada ba kallo daya zakayi mata kasan tanada nutsuwa sosai

Anan zee tayi introducing din batool agareta suka kuma gaisa cikin mutuntawa sannan zee tafito ta sauko qasa don samarwa qawar tata abin ta6awa.


Lokacin da ta dawo saita tarar firarsu ma sukeyi abunsu saita ajiye masu abin data kawo tana musu bismillah


Tare duk suka sauko qasa kan dan carpet din data shinfida masu suka shiga cin abincin suna fira


"uhmm, abincin nan yayi dadi, daga ji nasan ummie na ta girka" inji Aysha tana lumshe idanunta alamun abincin na kaimata karo

"to ni na dafa, wannan dakike ganinta babu abinda ta iya sai a girka ta shaqe plate taci, duk abincin dazaki shigo gidan nan kici ko agaba ne ni na girka shi" inji batool


Dariya duk sukayi

"kai nidai ban yarda ba, ummie ta tafi kama da wanda ta girka abincin nan"

Dariya suka sakeyi batool tace
"wato har kammani ke akwai kenan na wanda ya girka abinci?"

"qwarai kuwa, da kin kalli abincin kika kalli wanda ya girka sai kiga sunyi matching"

Dariya suka sake sawa

Haka sukaita firarsu har suka gama cin abincin aka kauda abubbuwan dasuka 6ata suka koma kan gado aka shiga fira

"ummie, wlh jiya dake na kwana arai, tsabar yadda nasa abin a raina sai gashi harda su mafarki wai yaya yaqara sawa an kamaki"

Dariya sukayi

"kincika sa abu arai wlh" inji zee tana Dariya

Itama dariyar tayi tace
"wlh, ai haka nake. Gashi dama halin yayan nawa nasani, haka yake bayada yarda kona diss, haka yake tun yana qaramin shi.
Can you believe ko aboki qwara daya baya dashi?
Ummie tace yafara wannan halin ne tun bayan rasuwar dan uwanshi"

Dan Wara idanu zee da batool sukayi cikin hadin baki sukace
"tun rasuwar dan uwanshi?"


Murmushi Aysha tadanyi

"ummie, ban gayamaki mu asalin wayeba, na baki tarihina just briefly batareda na fadamaki wasu abubbuwa ba

Kinsan ko waye yaya na?

Kinsan companies din nurul haqq masu rassa daban daban?"

Batool tayi saurin amsawa
"waye besan nurul haqq ba? Saidai idan ba a dubai yake ba, itama kanta zee datazo jiya jiyan nan tasan wasu wuraren, sis wannan park din damukaje ranan? To shima na nurul haqq ne" tafada tana kallon zee

Zee data dauki hasken abinda batool ke nufi saita Kada kai cikin mammaki tace
"natuna, koba wannan mai girman ba? Mai Hade da zoo"


"shi... Na yayana ne" inji Aysha


Duk Wara idanu sukayi sosai cikin mammaki dukda sunsan komai pretending ne kawai


"yayana ne mammalakin duk wani company na nurul haqq, mussadiq al-hassan"


"ya sallam! Kina nufin ke qanwar mai wadannan wuraren ce?" inji batool cikin kaduwa, yadda take acting din yayi mugun hawa kamar dama yau tafara sani


Murmushi Aysha tayi tace
"eh, duk wadannan wuraren mallakin yaya mussadiq ne, Saidai baya bayyana identity dinshi kamar yadda muma yake hanamu bayyana namu duk don maqiya wai.

Yanada saurin zargi da rashin yarda shiyasa shi kanshi idan ba saninshi kayi ba baka gane babban dan kasuwa ne kuma shi keda wadannan wuraren.

Na ta6a baki labarin cewa twins ne ko?" tafada tana kallon zee dake kallonta Tundazu babu kyaftawa

Kada kai zee tayi saurin yi
"eh kika ce dayan ya rasu ko?"

Kada kai itama Aysha tayi
"eh haka nace amma a zahirin Gaskiya ba mutuwa yayi ba"

Ji zee tayi kamar an kwada mata guduma akai

"b..be mutu ba?" tafada cikin rawar murya itakau batool tama kasa cewa komai sai kallon Ayshar datakeyi

"to ya mutun za'ace amma ba mutuwar allah da annabi ba.. Ina nufin kasheshi akayi"

Wannan karon tashin hankalin zee qarara yafito a fuskarta

"kasheshi akai? Waya kasheshi?"

Da Aysha mai lura ce data lura da yadda zee ta tashi hankalinta fiyeda yadda ya kamata data dora ayar tambaya akan Hakan

"eh, saceshi akayi daga baya aka kasheshi"


"innallilahi waina ilaihi rajiun" zee da batool suka fada atare hankalinsu a tashe


"nima ummie ke bani labari don a lokacin ko haihuwata ba'ayi ba akwai dai qaramin cikina wanda ba'ama san dashi ba.


Mujaheed shine Hassan mussadiq kuma Hussaini, yan biyu ne masu tsananin kama da juna don ummie ma kanta takan kasa banbancesu wani lokacin

Saida suka dan fara girma aka fara samun signs da ake banbancesu dashi

Nafarko shine dimple dinsu.
Mujaheed nada dimple a tsakiyar gemu kamar dai nawa don ance shi na biyo while mussadiq nashi a kumatun haggu yake

Na biyu kuma yanayin qiriniyarsu.
Mussadiq yafi Mujaheed qiriniya nesa ba kusa ba don Saida mussadiq yariga mujaheed fara rarrafe harma tafiya ma

Kamar ummie ke cewa mujaheed yanada sanyi sosai sa6anin mussadiq dake da qiriniya don Mafi yawancin lokuta inda ta ajiye mujaheed nan zatazo ta dauke shi shikau mussadiq daka ajiye shi zai qara gaba yaje yaita 6ana

Haka ma yara basa qwarar mussadiq don shi ba'a sashi kuka Saidai yasa Yayinda shikuma mujaheed babu ruwanshi sai yara suyita bugunshi baya ramawa

Saidai kuma mujaheed yafi mussadiq juriya da haquri don da wuya yayi kuka don cewa tayi ko rashin lafiya yake baya irin rigimar da mussadiq keyi Idan shine bashi da lafiya, Saidai shirunshi da sanyinshi suqara yawa, ko cikin yara yashiga masu qiriniya suna qwararshi baya kuka duk abinda zasuyi mashi idan kaga yayi kuka to abin yakai qurewa

Shiyasa ko a soyayyar dasuke masu ta mujaheed tafi don shi bayan soyayya harda tausayi don yaro mai sanyi dama yafi soyuwa a zuqatan iyaye ko don tausayawa yanayinshi


Abin yafaru ne ranar washegarin wata babbar sallah, lokacin suna saudiya don dama can ne asalinmu daga baya muka dawo nan


Kamar yadda al'adar wannan ahalin take dik washegarin sallah walau babba ko qarama ana haduwa a babban family house dinmu inda anan kowa da kowa na dangi, qwansu da kwarkwatan su saisun hallarta harda wadanda ba garin suke ba

Ana haduwa agidan don taya murnar sallah da sada zuminci


To suma haka suka shirya ranar tunda safe Abbanmu yakai ummie da twins dinta

Lokacin Abbanmu dan kasuwa ne wanda yayi suna sosai a madina a harkar kasuwancinshi kuma a lokacin shima ana iya sashi a sahun masu kudin family dinmu


Kamar yadda ummie ta gayamin tace tunda sukaje gidan Hassan wato mujaheed ya liqemata duk inda yayi yana maqale gashi ranar sanyinshi yaqara yawa fiyeda yadda yake da

Sai tayi tunanin ko bayada lafiya ne dukda jikinshi babu zafi

Saita sa6eshi ta goyashi ta cigaba da aikinta dashi a baya

Haka taita yawo dashi abaya har bayan zuhr don Koda zatayi sallah ma Saidai ta ajiye shi kusada ita yana kallonta har tagama sannan ya rarrafo yadawo kusada ita ya sake lafewa ajikinta


Ganin wannan lauye lauyen nashi yafara yawa yasa tasa aka siyomashi maganin ciwon kai don aganinta qila bejin dadi ne

Tabashi yasha ta maida shi baya ta goya har yayi barci ma

Be farka ba sai wajajen la'asar, tabashi abinci yaci sannan cikin gwarancinshi ya nuna wa ummie zaije wajen mussadiq da tunda suka shigo gidan yake cikin yara suna wasa

Sawa tayi akaishi wajensu din dukda bata cika son yana shiga yaraba saboda qwararshi da akeyi saikuma tayi tunanin ai gwara ya saba qila da haka da haka shima zai iya ramawa idan akayi mashi

Nan ta cigaba da hidimarta cikin dangi anata kai kawo cikin annushuwa da nishadi

Can wajajen bayan la'asar kadan aka fara jin hayaniya a tsakar gidan

Tun suna ji sama sama har abin yafara yawa Hakan yasasu fitowa ciki harda ummie

Abinda ummie tagani yayi matuqar girgizata don Saida jiri yakusan kadata ba don anyi saurin tareta ba

Mussadiq tagani jina jina jikinshi duk ciwo ga kayanshi sunyi futu futu harda yagewa a wasu wuraren

Da gudu suka nufeshi cikin tashin hankali don anason riqeshi amma sai fizge fizge yakeyi

Da gudu ummie ta qarasa gabanshi ta jayoshi ajikinta tana kiran sunanshi cikin kuka

Jin muryar ummie yasa yabar fizge fizgen saiya dago ya kalleta saikuma luuu yafada ajikinta asume.


Kwatanta tashin hankalin da aka shiga a lokacin 6ata baki ne

Nan take aka shiga kiran iyayen maza dasuka fita ta waya cikin qanqanin lokaci saigasu sun duro gidan ciki harda Abbanmu


Lokacin gidan banda koke2 babu abinda akeyi

Cikin gaggawa aka wuce dashi asibiti cikin masu zuwa harda Umminmu


Nan take likitoci suka kar6eshi aka shiga bashi taimakon gaggawa


Saida aka kusan awa sannan akasamu aka shawo kan mussadiq numfashinshi yadawo normal yakuma samu barci sanadiyar allurar barci da akayi mashi

Sai a lokacin likitocin suka fito wajensu ummie da suka kasa tsaye suka kasa zaune nan suka kwantar masu da hankali akan komai ya daidaita yama samu barci

Nan kowanne ya sauke Ajiyar zuciya na jindadin Hakan Saidai ashe zaune bata qareba

Tafiyar su likitocin keda wuya sai ummie da sai a lokacin tasamu zama taqara zabura ta miqe tsaye kamar wanda aka tsikara

Duk sai aka kalleta ana Tambayar lafiya

'mujaheed... Ina mujaheed?'

Nan kowa ya tuna dashi don tashin hankali yasa anma manta dashi

Tofa nan aiki sabo yafara don duk inda aka duba inda akasan za'a ganshi dama inda bazai iya shiga ba Amma babu shi

Babu inda ba'a duba ba a fadin gidan lungu da saqo amma babu mujaheed babu alamunshi


Nanfa hankali ya tashi ba ko kadan ba, tsakanin ummie da Abba aka rasa wanda yafi wani rikicewa

Duk fadin unguwar dama wajenta babu inda ba'a duba ba Amma babu mujaheed

Ummie har qaramin hauka saida tayi suma kau tayishi babu iyaka


Wasa wasa har dare babu mujaheed

Izuwa lokacin an yada cigiya gidajen t.v da radio amma shiru

Daren ranar babu wanda ya runtsa a familynmu, ranar murna ta chanza lokaci guda zuwa ta baqinciki, abu goma da ashirin, ga mussadiq a asibiti ga mujaheed ya 6ata.



Washegari ma dasa neman da akeyi akayi inda aka baza jami'an tsaro sosai wajen nemanshi

Ummie a lokacin bata ganuwa don itama dole qarshe aka bata gado a lokacin ma aka san da cikina.


Wasa wasa kwana daya yakoma biyu yakoma uku amma still babu mujaheed, Izuwa lokacin ummie da Abba sunzama abin tausayi ba kamar ummie don ita abin yafi ta6ata, babu abinda take Tunawa sai maqale mata dayaitayi tun safe, datasanin barinshi fitar datayi yafi cikin kwando Saidai komai muqaddari ne Daga allah, dole allah ya rubuta Hakan zai faru"



Dakatawa tayi ta dago ta kalli su zee da izuwa lokacin fuskarsu sunyi sha6e2 da hawaye sai a lokacin itama taji dumi dumin nata a fuskarta Hakan yasa tasa bayan hannu ta sharesu dukda Hakan ba yana nufin wasu bazasu sake zubowa ba

"A kwana na hudu aka bugo ma Abba waya da number da akayi hiding dinta.

Yana ganinta jikinshi yabashi kiran yashafi mujaheed dinshi

Hannu na rawa ya daga yana jin zuciyarshi kamar zata faso qirji

Kamar yadda yayi tunani Hakan ne don wadanda suka sace mujaheed ne suka bugo suna buqatar kudin fansa inhar suna son a sakomasu dansu.

Da farko Abba qin yarda yayi yace dole saiya ji muryar danshi yakuma tabbatar shine sannan

Aikau sai suka bashi saiga muryar mujaheed radam yana kiran Abba da ummie cikin kuka

Sosai hankalin Abba yayi mugun tashi nan take shima hawaye suka kawo mashi a idanu

Nan take yashiga magiyar don Allah suyi hqr karsu cutar mashi da danshi zai basu duk abinda sukeso

Jin Hakan yasa suka ce zasu sake shi amma sai sun bada kudin fansa

Nan suka yankama Abba kudin dazai bayar na fitar hankali

Abba yaso neman ragi amma firr suka qiya sukace ya za6a ko kudi ko mujaheed
Nan kuma suka jamashi kunne akan karya saki yasako jami'an tsaro aciki don sakosu aciki daidai yake da mutuwar mujaheed, suka kuma ce zasu sake kira don gayamasu inda zasu kai kudin.


Sosai hankalin ahalinmu yasake tashi

Inda duk wanda yaji adadin kudin dasuka nema saiya girgiza

Saidai Abba a shirye yake ya bada dukkan abinda ya mallaka don dawowar danshi Mafi soyuwa a gareshi

A lokacin mussadiq ya dade da farfadowa Saidai wata irin rashin lafiya yake mai zafin gaske ga ciwukkanshi da basu ida warkewa ba kullum cikin kukan ina mujaheed yake abinci ma Dakyar yake ci.

Ummie kuwa tafi kowa zama abin tausayi kodayaushe ciki kuka take duk tabi takoma kamar ba ita ba ga tashin hankali ga ciki.


Wasu daga cikin family dinmu suka bada shawarar sanyo jami'an tsaro acikin case din amma firr Abba yaqi yarda don babu abinda zaisa yayi tempering da rayuwar danshi.

Haka ya hada kudin nan cass family dinsu suma duk sun kawo gudunmawa aka hada kudadden ana jiran suqara bugowa don dole saisun bugo tunda da hidden number suka bugo wancan karon

Sai bayan kwana biyu suka bugo suna Tambayar an hada kudin, baki na rawa Abba ya amsa da eh sai suka fadamashi inda xa'akai

Roqonsu yashigayi cikin magiya kan suqara bashi mujaheed yaji Muryarshi

Babu musu aka bashi

'Abba' mujaheed yafada cikin mugun sanyi

'Abba... Ummie'

Kasa controlling kanshi Abba yayi Saida yayi hawaye

'mujaheed bunnaya, kana lafiya?' yafada cikin rawar murya

'Abba?' mujaheed yasake fada

'kayi hqr zaka dawo kaji? Abba zaizo ya daukeka' inji Abba hawaye na gudu sosai a kumatunshi

'muccadik' mujaheed yaqara fada cikin sanyin murya


'mussadiq nanan lfy, shima zaizo kaji? Kaji dana'

Daga Hakan sai yaji muryar daya daga cikin 6arayin na cewa ya isa haka nan tunda sunyi maganar

Nan yasake gayamasu inda zasu kai kudin da lokacin dazasu kai dakuma qara yimasu gargadi akan karsu sake su sako jami'an tsaro aciki idan ba Haka ba a bakin ran dansu.

Nan aka shirya komai Abba da kanshi yaje bada kudin

Kuma ya ajiyesu inda suka ce sannan yatafi



Saidai shiru shiru basu bugo ba sukace ga inda zasuje su dauki yaron ba

Tun suna jira har hankalinsu yafara tashi da jin yadda shirun yayi yawa

Sai a kwana na biyu da bada kudin sannan aka bugamashi waya, a lokacin saura qiris ya zauce

Nan aka gayamashi inda zaije ya dauki mujaheed cikin wata ash din mota, zasu bar motar a bude dayaje kawai ya bude ya fiddashi ya tafi dashi

Cikin jindadi Abba yayi shirin tafiya, jikinshi har rawa yakeyi don har jiri jiri yakeji na neman dibanshi

Dashi da Hussaininshi suka tafi dauko shi inda akace din


Wuri ne da sai anfara fita daga gari ma, babu gidaje a wajen sai busassun ciyayi don lokacin rani ne

Tun daga nesa suka hango motar ash colour din da akace gefen titi.

Parking Abba yasa Hussaininshi yi tun kafin su qarasa suka fito da sauri suka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login