Showing 180001 words to 183000 words out of 322641 words
Chapter 61 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
"alhamdullilah"
Shiru yadan ratsa wajen, jin Hakan yasata dagowa sai taga shima ita yake kallo sai tayi saurin sauke idanunta qasa
"tell me, menene?" yafada tenderly
Sake dagowa tayi ta kalleshi sai kuma ta saukar da kanta qasa ahankali kamar mai ciwon baki tace
"park din da mukaje jiya"
Dan shiru Aymaan yayi saikuma yace
"yes? What about that?"
"sunanshi.. Nakeson ka gayamin" tafada still idanunta a qasa
Tsayawa yayi yana kallonta for some moments
Jin shiru yasa ta qara Dagowa ta kalleshi da shining eyes dinta dake glittering saboda dan ruwan daya taru aciki
"please" tafada ahankali tana kallonshi
"meyasa kike son sanin sunan?" inji Aymaan still yana kallonta kamar mai son karantar wani abu a fuskarta
"babu, just tell me"
"zan gayamiki amma saikin fadamin dalili" yafada still idanunshi akanta
"please.." tafada ahankali sai kuma ta sauke idanunta wanda yayi daidai da digar hawayenta qasa
Cigaba da kallonta yakeyi yana jin zuciyarshi kamar ana melting dinta
"ki fadamin me zakiyi da sunan and I'll tell you" yasake fada
"babu ruwanka, just tell me" tafada cikin cracking voice, a inda yake tsaye yana hango diddigar hawayenta
"da ruwana saboda ke sister ta ce, idan batool ce tazo ta tambayeni itama haka zan cemata, ke da batool daya ne a wajena"
Ba don bata iya zuciya ba da babu abinda zai qara tsaidata a gabanshi, Hakan yasata cewa
"inason.. Naje ne"
"Wani abu kikeso? Ki fadamin koma menene zanje nasiyo miki" inji Aymaan din
"babu abinda zan siyo, nidai ka fadamin.. Don Allah" Sai kuma ta rufe fuskarta da taffukan hannayenta ta shiga sobbing ahankali
Lumshe idanu Aymaan yayi cikin quncin zuciya sannan yasake budesu suna kadawa ya kalleta dasu
"Me zakiyi acan?" yasake tambaya Muryarshi na chanzawa
Cikin kuka zee tafara magana
"I know I may sound ridiculous ko ayimin kallon mahaukaciya, I don’t care.
Zuwa zanyi nemanshi, bazan iya jure abinda zuciyata keyimin ba, I can't
Zuciyata na gayamin yana can, yana nemana, Inason inqi zuwa amma bazan iya ba, bazan iya cigaba da jure azabar datake minba, nayi qoqarin jurewa daga jiya zuwa yau but not anymore.
Ka fadamin sunan wajen, ko cab ne sai yayi dropping dina
Idan kuma bazaka fadamin ba zan tafi, zan tafi naita nema harna gane"
Tunda tafara maganar Aymaan ke kallonta batareda yayi qoqarin katse mata hanzari ba har Saida takai aya.
Dan murmushi yayi wannan yafi kama da mai ciwo sannan yace
"to meye na kukan? Why the tears? Da Alamu dai beneath that eyes akwai qoramun ruwa shiyasa abu kadan sai sharr hawaye.
Meye aciki to? Ni bakiyi sounding ridiculous to me ba, thats what your heart wants and so be it.
Jeki shirya na kaiki"
Dagowa tayi ta kalleshi da wet eyes dinta
Kada mata kai yayi
"yes, ki shirya zan kaiki basai kin hau cab ba"
Girgiza kai tayi tace
"A'a nidai kawai ka fadamin sunan, thats all"
Shima girgiza kai yayi yace
"naqi din, go and dress up bari nima na shirya saimu tafi"
Be bata damar qara magana ba ya bude kofar dakin nashi ya shige ya rufo
Bïñ kofar tayi da kallo sai kuma ta share hawayenta ta juya ta koma daki tana jiran fitowarshi don ita dama a shirye take.
Kujerar dake facing din gadonshi ya samu ya zauna akai tareda dafe goshinshi
Shi kadai yasan abinda yakeji a zuciyarshi, musaltashi kuma 6ata lokaci ne don bazai misaltu ba
Ya kusan Mintuna goma ahakan sannan ya miqe ya zare jallabiyar jikinshi sannan ya nufi toilet.
Zaune take kan stool din gaban mirror tana daga kai tana kallon agogon dakin akai akai
Tunda tashigo ko gefen batool bata sake kallo ba don haryanzu haushinta takeji na qin gayamata sunan Wurin datayi wanda Hakan ma yasa taje tasamu Aymaan din
Itakau batool bata damu ba sai cigaba da harkan gabanta da itama tayi batareda ta kulata ba.
Suna Hakan zee tajiyo budewar kofar dakin Aymaan
Jitayi kamar ta miqe ta fita amma tasamu ta danyi controlling kanta kadan ta cigaba da jira
Kwankwasa kofa yayi Hakan yasa tayi zumbur ta miqe tsaye ta nufi kofar
Dakatar da abinda takeyi batool tayi tana kallon kofar don ganin wa ke bubbuga kofar
Bude kofar zee tayi sai sai idanunta sukaci karo da Aymaan da ya chanza shiga zuwa manyan kaya irin namu na hausawa farare sunyi bala'in amsarshi
Murmushi yayi mata
"sorry na tsaidaki ko?"
Batace komai ba sai sauke kai qasa datayi
"oya muje" yafada yana kaucemata a hanya
Dama abinda takeson ji kenan Hakan yasa ta ida fitowa tafara tafiya shikuma ya biyo bayanta
"Akhie!!" muryar batool ta tsaidasu dga tafiyar dasuka fara
Juyowa sukayi suna kallonta Yayinda itakuma ta qaraso bakin kofa tana ma Aymaan kallon mammaki
"Akhie, badai wajen nan zaku ba?" ta tambaya a mammakince
"eh can ne ko kinada saqo?" inji Aymaan
"but Akhie.."
"baki dashi kenan, sai mun dawo" yayi gaba abunshi
Zee ta sauke sigh of relieve sannan itama ta bi bayanshi batareda tabi takan batool dake binsu da kallo cikeda mammaki ba
A parking space ta tarar dashi harya budemata Front seat kamar yadda yasaba
Zuwa tayi ta shiga sannan ya maida kofar ya rufe ahankali sannan ya zagaya yashige shima ya rufo kofar sannan ya tada motar yayi reverse sukazo suka fice daga gidan.
Tafiya suke silently babu mai cewa komai acikinsu har suka qarasa park din jiya.
Fitowa sukayi gabadaya suka rurrufe kofar sannan suka fara tafiya, Aymaan a gaba zee a bayanshi
Saida suka fara sayen ticket sannan suka shiga ciki
Kamar dai jiya yau ma wajen acike yake da mutane sunata kai kawo
Zee ce agaba yanzu Aymaan a bayanta suka shiga bin ko ina suna dubawa kamar dai jiya.
Duk namijin da zasu hadu dashi sai zee ta kalli fuskarshi Koda baya ya juyamata saita san yadda zata shawo gabanshi taga fuskarshi
Haka sukaita zagayen park din kamar dai jiya
Gajiya iya gajiya sunyi amma Aymaan ko kadan be nuna ba Binta kawai yakeyi yadda takeso
Saida taji daga kafa na neman gagararta sannan ta nemi wani kujerar swing ta zauna yana sauke numfashi ahankali
Cikin kulawa Aymaan ya dan duqo yana kallonta
"Are you ok?" yafada ahankali
Kada mashi kai tayi sai kuma ta share hawayen daya sulalo mata
"don Allah mu jirashi, nasan qila bekai da zuwa bane, Inaji ajikina zaizo don Allah mu zauna mu jirashi, kaji Yaya Aymaan?"
Murmushi ya su6uce mashi, wai yaya Aymaan, dama yaushe tafara kiranshi yaya?
"haba karki damu sister, mu jirashi din nima Inaji ajikina zaizo, no p kinji?" yafada still yana murmushi
Dadi taji ya kamata, dama haka gayen nan keda sauqin kai?
Shima zama yayi a kujerar dake kusada ita yayi folding hannu a qirjinshi yana kallon masu kai kawo kamar yadda takeyi itama
This is crazy! Anya kau wannan yarinyar soyayya bata haukatata ba?
Tayaya zata sa su tsaya jiran gawon shanu? Mutumin da batada ma tabbacin ta ganshi din
Amma dayake Aymaan mutum ne matuqar haquri da kuma saukin kai plus yadda yake jinta a zuciyarshi sosai yasa yaqi nuna komai suka cigaba da jira.
Wasa wasa sune har bayan asr zaune suna jira sallah kawai ke tadasu, a inda suke suna iya hango gate so duk masu shige da fice a kan idonsu
Dukda Aymaan be duba wayarshi ba yasan akwai tarin missed calls dayawa dama Saida ya maidata silent tun a gida don kar kira yayi distracting dinshi
Ya riga yasa a ranshi yadda ita tasa suka zo nan to komawar ma saita nemi sukoma din zasu koma don shi mutum ne me bama mutum damar gano bullewar hanyar daya dauko da kansa kamar yadda yanzu yake son tagano haukanta da kanta
Maida kanta tayi kan gwiyagunta jin anfara kiraye kirayen sallar magrib
Sosai zuciyarta ke mata suya kamar ana soyata a tafasashen mai
Ta dan jima ahakan sannan ta dago batareda ta kalli Aymaan ba tace
"mutafi"
Yi yayi kamar bejita ba hakan yasata qara cewa
"ka maidani gida"
Sai a lokacin ya dago ya kalleta
"tun yanzu?" yafada yana kallonta
Miqewa tsaye tayi ahankali tana Rataya jakkarta
"eh mutafi"
"ok, mufara sallah tukkuna" yafada yana miqewa tsaye shima
Saida suka wuce masjid akayi sallar dasu sannan suka fito daga wajen suka hau mota suka kama hanyar gida.
Kamar yadda suka zo yanzu ma silently suka koma babu mai cewa komai kowa da abinda yake sakawa a zuciyarshi
Yana iya ganin yadda take dauke hawayenta akai akai ta gefen idonshi, Ajiyar zuciya ya dan sauke yana dan girgiza kanshi ranshi a mugun jagule.
Koda suka isa gida sai suka tararda su ummy tsaitsaye hankula a tashe
Zee dai tana zuwa tayi sama dagudu cikin kumshe kukan dake neman kufcemata
Hakan yasa suka maida hankalinsu akan Aymaan
Fada sosai suka shiga yimashi akan meyasa zai biyemata sutafi suyi wannan zaman bayan yasan ba lallai bane ace da gaske shi din tagani ba, mezai kawoshi dubai mutumin dake Nigeria
Beyi mammakin yadda akayi suka san da zancen ba don yasan batool ce zata gayamasu Hakan yasa yayi shiru suka qaraci fadansu suka gama ya basu haquri sannan ya wuce sama yashige dakinshi shima.
A ranar babu wanda yafito dinner da zee da Aymaan din
Kowannensu is in a very sad mood Saidai za'a iya cewa na Aymaan yafi don zee ita ke wahalar amma yafita jin zafin abin, jiyake kamar yayi me don takaici.
Ranar dai da daddare barci Saidai sukayi rabi da rabi shima marar dadi
Washegari ma haka suka tashi so moody don dukkansu ransu a cinkushe yake musanmman zee, shi Aymaan ma yana gama abinda zaiyi a gidan ya fice ya wuce gidansu abokinshi Ahmad Junaid
A bangaren zee kuma haka ta wuni cikin rashin walwala, duk yadda batool taso sata feeling better Saidai ta haqura ta kyaleta itama.
Ahankali Zainab takoma gidan jiya, always moody, magana inba takama dole ba batayi, Dariya kuma rabonta dayi tun ranar kafin abin yafaru
Sosai wannan chanjin ya damu su ummy dasuka fara murnar warwarewarta da farko.
Wani sa'in haka zasu zaunar daita suyita yimata nasiha da rarrashinta amma a banza, kwata2 takasa komawa normal self dinta kuma
Aymaan kau shima yana cikin damuwa tunda abin yafaru musanmman daya lura da halin datake aciki yanzu amma dayake gwanin iya 6oye damuwa ne babu wanda yasan abinda yake ciki don Kodayaushe idan ka kalli fuskarnan zaka ganta da qayattacen murmushi akai.
*AFTER TWO WEEKS*
Haryanzu zee bata ida komawa daidai ba Saidai tarage moodiness dinta sosai
Yanzu takan zauna ayi fira daita amma ba mai tsayi ba don haryanzu bata ida healing daga famin datayi ba na raunin zuciyarta
Yau saturday, babu aiki don haka a gida Aymaan ya wuni
Batool bata gida taje ganin wata classmate dinta da batada lafiya
Babu yadda batayi da zee akan ta rakata ba taqiya dole ta tafi ita kadai.
Suna zaune falo da ummy da zee suna dan fira Aymaan ya sauko daga sama cikin shirin shi na fita
Qarasowa yayi falon cikin fara'arshi ya zauna suka dan qara labarin dashi sannan ya miqe yana cewa ummy zaije wajen aikin Abbu amso saqo, shi ya kirashi yaje
Adawo lfy ummy tayimashi itakuma zee takama kallonshi kamar tace zata bishi don itama zaman gidan yafara isarta don jitake wama yace taqi bin batool
Ganin kallon datake mashi yasashi yimata tayin ko zata rakashi?
Da sauri ta Kada kai kamar dama jira take sai kuma ta kalli ummy ta sadda kai
Murmushi ummy tayi tace to ta tashi su shirya sutafi ko babu komai taga gari zata kuma ga ma'aikatarsu Abbu.
Cikin zumudi ta tashi ta haye sama don chanzawa suka bita da kallo fuska dauke da murmushi
Cigaba da firarsu su ummy sukayi harta sake saukowa cikin shirin ta.
Ganin Hakan yasa Aymaan tashi daga zaunen dayake sukayi sallama yayi gaba zee tabishi a baya
Motar Aymaan suka shiga shi a mazaunin driver ita a gefen shi suka fice daga gidan.
Ma'aikatar su Abbu din suka shiga, Aymaan yafita yabarta a motar yashige ciki
Be dade ba sai gashi sun fito tareda Abbu
Qarasowa sukayi wajen motar Hakan yasa zee fitowa suka gaisa da abbu yana tsokanarta kamar yadda yasaba.
Saida suka dan jima ahakan sannan sukayi sallama da juna, Abbu yakoma ciki sukuma suka Kamo hanyar dawowa
Tafiya suke cikin shiru babu mai magana sai waqar dake tashi a background din motar ahankali
Can sai Aymaan yadan juyo ya kalleta sai kuma ya maida kallonshi akan titi
"muje shopping?"
Juyowa itama tayi ta kalleshi
Daga mata girarenshi yayi sannan yayi murmushi yana sake maida hankalinshi akan titi
"No" tafada ahankali
"why? Bazamu dade ba ai, kawai zamu siya some stuffs ne saimu juya, ni akwai abubbuwan danake buqata ne nasan kema bazaki rasa ba"
Shiru tayi kawai bata ce komai ba
"I'll take your silent for yes" yafada tareda karya kan motar ya dauki corner da zata kaishi supermarket na kusa kusa.
Parking yayi a parking space din supermarket din sannan ya fito ya zagayo ya bude mata itama ta fito
Rufe motar yayi sannan suka nufi cikin shopping mall din atare.
Zuwa yayi inda ake daukan shopping basket ya dauki biyu ya bata daya shima ya riqe dayan
"zan shiga session din maza, idan kin rigani gamawa ki jirani anan" inji Aymaan
Kada kai tayi kawai Hakan yasashi Juyawa ya wuce ya barta nan
Ta dan jima a tsaye saikuma ta sauke Ajiyar zuciya sannan itama ta wuce session din mata
Yan sayayya tayi wanda bata kai ta kawo ba wanda mostly turarrika ne masu kyau da tsada sai yan kayan maqulashe da ba'a rasaba.
Ta rigashi gamawa shiyasa tazo ta tsaya inda yace din riqe da basket dinta tana jiran shi
Wayarta dake jakkarta ta dauki ruri Hakan yasa ta ajiye basket din agabanta ta bude jakkar ta fiddo wayar
_*sis batool* taga na yawo a screen din.
Dan murmushi tayi sannan ta daga ta kara a kunne
Dagowar da zatayi sai ta sauke idanunta akanshi
Zuciyarta tayi wata muguwar wuntsilawa
Wara manyan idanunta tayi sosai a kanshi kamar zasu fado daga socket dinsu
"hello.. Hello" taji anayi a kunnenta amma ina? Batama san meye kare a kunnen nata ba, hankalinta ya tafi, ya tafi gabadaya
Ahankali ta rintse idanunta ta bude amma still yana nan, tsaye hannunshi daya zube a aljihun wando daya riqe da waya yana daddanata wani na yimashi magana
Kafeshi tayi da idanu kamar wata hallita take gani daban ba mutum ba irin ta
Sanye yake da black american suit idanunshi toshe cikin da baqin shade, lallausar baqar sumarshi s gyare sai salqi take
Ahankali taga yafara motsa bakinshi yana magana still kanshi hankalinshi akan wayar hannunshi saikuma ya dago ya kalli mutumin dake gefenshi yanata Kada kai cikin girmamawa ga dik abinda yace
Wata maganar yasakeyi sannan ya amshi wata takarda a hannun mutumin ya duba ya miqa hannu baya, wani dake bayanshi shima sanye da suit yayi saurin bashi pen
Dan rubutu yayi a takardar mai kama da file sannan ya rufe ya miqama mutumin
Cikin russunawa mutumin ya amsa yanata washe baki yana qara russuna mashi yana magana wanda bazata iya jin abinda yake cewa ba daga inda take
Sai gani tayi ya juya batareda yabi takan mutumin ba ya nufi hanyar waje cikin wani taku
Hakan yasata dawowa firgigit daga duniyar kallonshi data lula
Sakin wayar da haryanzu ke kare a kunnenta tayi batareda ta saniba
"DEEN!!!" tafada da qarfi tana nufar shi da sauri
"Zainab!" inji Aymaan da yakusan qarasowa inda take amma ina bataji ba hartayi gaba
Saurin ida Qarasowa inda ta jefar da wayar yayi ya dauka saikuma shima yayo hanyar waje
Fitowa zee tayi a gigice tafara waige waige cikin fitar hayyaci can ta hangeshi sun nufi wata mota waya kare a kunnenshi
"DEEN!!!" ta qara qwalamashi kira sannan tayi wajen da sauri sauri gudu gudu.
Bude mashi kofar baya akayi still yana making call
Ahankali ya duqa zai shiga yaji an kamo mashi gefen suit dinshi da qarfi
Dakatawa yayi daga yunqurin shigar dayayi batareda ya juyo ba
Itama zee data damqo gefen rigar kallonshi take tana sauke numfashi mai nauyi
Guards din wajen kau shock ya hanasu ta6uka komai sai tsayawa dasukayi suna kallonta baki bude
"Deen??" tafada cikin wata iriyar karyayar murya
Ahankali kamar wanda ake controlling da remote yashiga juyowa harya qarasa juyowa ya fuskanceta
Kallon kallo suka shiga yima juna dukda shi nashi idanun na lullu6e da shade
"Deen.." tasake fada cikin sarqewar murya tana jin numfashinta na qara yimata nauyi... ✍️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:40 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*058*
*WHO IS WHO?*
Ahankali yasa hannu ya cire shade din dake manne da idanunshi, oily eyes dinshi suka bayyana.
Sauke idanunshi yayi kan hannunta dake riqeda gefen suit dinshi haryanzu sannan yasake Dagowa yana Binta da wani irin kallo
Sosai kallon dayake binta dashi ya sake hautsina mata ciki hakan yasa batasan sadda tasaki rigar ba
"Deen? Baka ganeni ba?" tafada tana kallonshi babu kyaftawa
Kafin ya ko motsa Guards dinshi sukayo gaba zasu taso mata
Daga masu hannu yayi, still idanunshi akan zee da itama takasa dauke nata akanshi, ba komai yasa Hakan ba sai irin kallon dayake binta dashi wanda bata ta6a sanin Deen dinta dashi ba
Duk tsayawa sukayi Cak sanadin dakatar dasu da yayi
Ahankali ya shiga zame suit dinshi na sama a qyamace still idanunshi cikin nata, ganin Hakan yasa wani guard dinshi Qarasowa bayanshi yana taimaka mashi har suka sa6ula rigar
Batayi aune ba taji saukar rigar a fuskarta
Wani masculine qamshi dake jikin rigar ya bugi hancinta Hakan yasa ta lumshe idanunta ta bude sannan tasa hannu ta Janye rigar daga fuskarta Ahankali
Gani tayi ya juya yana niyyar shiga motar again Hakan yasa ta cafki hannunshi tana tsaida shi daga yunqurin shiga again
"Deen.." tasake fada muryarta na rawa sosai
Wani qololon abu ya tsaya mashi a wuya.
How dare her! How dare her zata ta6ashi da wannan dirty hannun nata
Juyowa yayi again yana mata kallon da yasata jin kamar ta narke don tsoro amma dukda Hakan taqi Sakin hannun
"Deen? Meyasa kake min wannan kallon? Nice fa, zee.. Your Zainab" tafada cikin rawar murya sosai
Cikin quluwa ya fizge hannunshi daga riqonta wanda Hakan yasa tadanyi loosing balance tayi