Showing 183001 words to 186000 words out of 322641 words
Chapter 62 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
kamar zata fadi Saidai bata fadin ba
Sudai Guards dinshi nasu ido don tunda ya dakatar dasu dazu idan bashi yabasu umarnin yin wani abu ba bazasu yi gigin yin wani abin ba
Juyawa yasakeyi zai shiga taqara Kamo hannunshi ido rufe
"No Deen, please don't do this, don’t reject me for the second time, I can't take it, i'll die" tafada cikin kuka sosai hankalinta a matuqar tashe
A matuqar fusace ya sake juyowa, beyi wata wata ba ya daga hannu da niyyar shararawa fuskar mari sai yaji an cafe hannun a iska da qarfi
Zee data tamke idanunta gamm tana sauraron saukar marin taji shiru Hakan yasa ta bude idanun ahankali
Aymaan tagani tsaye gefenta riqe da hannun Deen a iska suna bin juna da fierce kallon kallo
Saurin qarasawa wajen Aymaan tayi
"Aymaan ka kyaleshi, Deen ne fa, shine. Please ka sakeshi kar yayi fushi" tafada tana riqo hannun Aymaan daya riqe hannun Deen dashi
Juyowa yayi ya kalleta cikin matuqar quluwa
"zaki saki hannuna kosai na fasamaki baki?!" Yafada cikin qaraji, fuskarshi na bayyana tsantsar 6acin ran dayake ciki
Sosai zee ta girgiza da yanayin Aymaan wanda bata ta6a saninshi dashi ba Amma so ya riga ya rufe mata ido Hakan yasa taqi saki
"naji, ka fasamin kai ma idan ka tashi just leave him, ina ruwanka da rayuwata!!" itama tafada cikin daga murya
Idanunshi dasukayi mugun kadawa ya kafeta dasu saikuma ya saki hannun Deen din ahankali
Ganin Hakan yasata qara saurin nufar Deen din
"Deen am sorry, besan ko waye kai ba, am very sorry" tafada tana niyyar sake kama hannunshi Hakan yasashi Janye hannun sannan ya turata baya a fusace
Baya baya tasakeyi tana gasping don tasan wannan karon dole takai qasa kuma idan takai qasa saitaji jiki
Jitayi an tareta ta baya an tsaidata daga faduwar
A tsorace tasake bude idanun sai tayi arba da fuskar Aymaan dake kallonta da rinnanun idanunshi
Bata iya cewa komai ba sai kallonshi itama datake numfashinta na qara yin nauyi
Miqar da ita yayi tsaye sannan ya saketa yayi wajen Deen dake tsaye fuskarshi tayi jaa don fushi
Guards ne sukayi saurin tareshi suna kakkama hannunshi
Zuciyarshi ce ta qara harzuqa Hakan yasa ya wuntsilar dasu da iya qarfinshi duk suka sakeshi batareda sun shirya ba sukayi baya baya
"you dog!" Yafada yana shaqo kwalar Deen qirjinshi sai sama da qasa yakeyi alamun zuciyar yan mazan ta tashi
Bïñ hannun da Aymaan ya shaqi kwalarshi Deen yayi da kallo suprisingly sannan ya dago yana kallonshi shima jijjiyoyin jikinshi na tashi
Cikin harshen larabci Aymaan yafara magana
"waye kai?! Waye kai da zaka dora hannu akanta?!!"
Afusace Deen yasa hannu ya kwa6ar da hannun Aymaan daga qwalar rigar tashi, kafin Aymaan yayi recovering daga haka yaji saukar naushi a gefen kumatunshi
Qara Zee tasa tana kiran sunan Aymaan
Baya baya Aymaan yayi saikuma ya dakatar da kanshi daga faduwar dayaso yi
Hannu yasa ya taba gefen bakinshi ya duba sai yaga jini
Sake kallon Deen dake huci yayi sai yayi kukan kura ya nufeshi
Saidai tun kafin ya qarasa gunshi guards dinshi suka tareshi, basuyi wata wata ba suka tarar mashi suka shiga jibga.
Qara Zee tasake saki tana rufe baki hankali a mugun tashe, kuka takeyi kamar zata shide jikinta na wani mugun 6ari
Gaskiyar hausawa dasuka ce sarkin yawa yafi sarkin qarfi don tun Aymaan na iya maida martanin har yakoma kare kanshi har daga baya ma yakasa kare kanshi din.
Ganin Hakan yasa zee nufar Deen dake tsaye yana kallonsu ta Kamo hannunshi
"Deen na roqeqa, kace subari zasu kasheshi"
Wani irin fizge hannunshi yayi wanda har Saida takai qasa
Juyawa yayi zai wuce wajen motar shi tayi saurin rarumo qafarshi daya
"Deen! No! Karka tafi zan mutu!" tafada tana rungume qafar da dukkan qarfinta
A matuqar hasale ya fizge kafar itama yana ja baya yana kallonta da bloodshot idanunta sannan yana nuna ta da yatsarshi datake karkarwa saboda yadda jikinshi ke tsuma don 6acin rai
Sai kuma ya juya ya bude kofar baya na motar ya bude wani akwati ido rufe ya fiffido wrappers din kudinsu nacan ya farka wrappers din yashiga watsamata kudadden ajiki, tsayawa tayi Cak da kukan tana kallon yadda yake warwatsa nata kudadden akai, da wani yaqare Sai ya farka wani har Saida ya qarar da wrappers biyar akanta
"Go away, you brat!!" Yafada cikin hargowa sannan ya juya ya shige motar ya rufo da qarfi.
Ganin Hakan yasa guards din kyale Aymaan da suka yima lilis suka rugo wajen mottocin suka shishiga suka tayar suka bar wajen a 360 suna badesu da qura
Ahankali Aymaan ya bude idanunshi dasukayi mashi mugun nauyi yabi motocin dasuka fita a harabar wajen da kallo sannan ya maido kallonshi akan zee dake zaune har lokacin bata ko motsi
Maida idanunshi yayi ya lumshe cikin azaba yana kiran sunan allah under his breath.
Saida yayi yunqurin tashi sau biyu ya kasa, ana uku yasamu ya tashi zaune Dakyar yana cije lip dinshi na qasa
Koina na jikinshi ciwo yakeyi kamar ana dandaqarsu ga bruises a jikinshi sunyi jaa abinka da fatar hutu dama
Ahankali yasake bude ido ya sake kallon zee dake a sitting position dinta har lokacin
Bude bakinshi yayi Dakyar yafara magana
"kin gani.. Ko? Kinga.. Abinda kika jawo ko?"
Shiru
Shaqar numfashi yayi sannan ya fesar yafara yunqurin tashi, sosai jikinshi yayi laqwas don babu qarya ya jibgu don shi tunda yayi wayau bazai iya recalling lokacin da aka ta6a yimashi irin wannan dukan ba
Ganin bazai iya tashin ba yasa ya qara Dagowa ya kalleta yaga still wuri guda take kallo sai jiyayi ranshi ya kuma 6aci
"ki tashi mutafi" yafada yana kallonta but still bata motsa ba
"Zainab! Am talking"
Nanma shiru
Shima shiru yayi ya tsaya yana kallonta yana qoqarin gano wani abu
Abinka da medical doctor nan take ya gano
Wara idanunshi dasuka tattaso yayi sannan yayi saurin rarrafawa gabanta
"Zainab" yakira sunanta yana waving a gaban fuskarta amma bata ko kyafta idoba
"zee?" yafada yana dan ta6ata kawai sai yaga tayi baya baya
Ba don yayi saurin tarota ba da tasha qasa
"Zainab! Zainab!!" Yafada yana jijjigata amma shiru
Tara yatsarshi yayi a hancinta sannan ya dora kunnen shi daidai zuciyarta yana feeling heartbeat dinta
A rikice ya dago ya karkata ya zaro wayar shi dake aljihunshi still tana jikinshi
Lalubo number Ahmad yayi ya danna mashi kira
Saida takusan katsewa sannan aka daga
"hey!" inji Ahmad daga wancan bangaren
"Ahmed kana ina?"
"lafiya?" inji Ahmad jin muryar Aymaan wani iri
"answer the damn question!" inji Aymaan yana qara jijjiga zee dake sheme ajikinshi
"ina gida, meya faru naji voice dinka wani iri?"
"kazo Ni'ima shopping mall, urgently please"
Daga Hakan ya katse kiran ya maida hankalinshi kanta
"Zainab! Zainab!! Wake up zee!" Yafada yana dan marin fuskarta amma shiru
Waige waige yafara, kasancewar babu mutane sosai a wajen ga kuma motoci dayawa dasuka kakkaresu shiyasa tunma lokacin dasu Deen ke nan ba'a gansu ba.
Ahankali ya maida ta ya kwantar daita sannan ya tashi Dakyar yafara dangyasawa ya fito fili
Waige waige yafara can ya hangi securities, daya na bude gate daya na a zaune
Da dingishi ya qarasa wajensu, tun daga nesa dasuka hangoshi suka fara kallonshi harya qaraso gabansu Dakyar
I.D card dinshi yafara nunamasu, Ganin ko waye yasasu saurin tashi suna tambayarshi lfy suka ganshi haka
Briefly yayi musu bayanin he's attacked By some thugs shi da sister shi dake can unconscious sannan ya gayamasu abinda yake buqata don yimata taimakon gaggawa.
Cikin sa'a aka samu most abubbuwan daya lissafo suka koma wajen zee dake sheme har lokacin
Dukda yadda yakejin kamar kanshi zai rabe gida biyu don sarawa haka ya daure yafara bata taimakon gaggawa
Suna haka Ahmad ya iso supermarket din.
Kasancewar Aymaan dama yariga ya fadamasu wani nanan tafe wajensu yasa yana isowa aka rakoshi wajensu
Sosai hankalin Ahmad ya tashi ganin halin dayaga Aymaan dama zee dake unconscious har lokacin
Cikin qarfin hali Aymaan yace ma Ahmad ya kaisu hospital
Da taimakon Ahmad aka saka zee back seat sannan sukuma suka dawo gaban seat, Ahmad ya tada motar yayi reverse suka fice daga supermarket din.
Asibitin da Aymaan ke aiki suka zarce.
Tun kafin su iso Aymaan ya bugama wani colleague dinshi waya ya sanar dashi Zuwansu shiyasa Koda suka isa akayi saurin kar6ar zee aka shige daita
Da farko Aymaan qin yarda yayi ayi treating ciwukkanshi har Saida ya tabbatar da sun ceto rayuwar Zainab from danger sannan Dakyar su Ahmad suka samu suka lalla6ashi ya yarda.
***
Kwance yake bayan angama treating dinshi idanunshi a lumshe kamar mai barci amma ba barcin ba yake
Shi kadai ne dakin don tunda nurse tagama treating dinshi suka fita suka bashi wuri don ya huta sosai
Qarar bude kofa yaji amma Hakan besa ya bude lumssasun idanunshi ba
"bismillah ummy" yaji Ahmad na cewa Hakan, Hakan yasashi bude idanun babu shiri ya juyo yana kallon saitin kofar
Ummy yagani agaba sai batool a bayanta sai Abbu a bayansu
Yunqurin tashi zaune yafara sai ummy tayi saurin Qarasowa tana taimaka mashi ya ida tashi zaune ta karamashi pillow a baya
Dagowa yayi yana kallonsu sai yaga suma shi suke kallo cikin tausayawa
"sannu Akhie" inji batool kamar zatayi kuka
Dan murmushi yayi mata sannan ya kalli su ummy
"ummy, waya gayamaku?"
"Ahmad ne habiby, muna can hankalinmu Kwance ashe babu lafiya"
Dagowa yayi ya watsama Ahmad mugun kallo shikuma yayi murmushi yana daga kafadarshi
"sannu son, allah ya kyauta gaba amma nayi mammaki ace thugs a supermarket, how come?"
Shiru Aymaan yadanyi sai kuma ya sauke Ajiyar zuciya
"Abbu nidai bansan ya Hakan yafaru ba, kawai nagama siyayya ta nafuto saina hangeta inda nace ta jirani
Amma kafin na qaraso sai naji qarar faduwar abu daga hannunta sai kuma naga tayi wajensu dagudu
Na kwalamata kira amma bata saurareni ba shiyasa nima na qaraso wajen da sauri sai naga ashe wayarta ce ta saki
Saina dauketa na tashi nabita lokacin harta fita waje
Nima saina bita Saidai Koda nafita ban ganta ba don har titi saina nakai amma banga wulginta ba
Dawowa nasake yi da niyyar komawa ciki again sainaji kamar magana a ta parking space din wajen
Saina zagaya, kawai saina hangeta daidai wani ya tureta
I thought faduwa zatayi amma sainaga bata fadi ba, sai nayi saurin nufar wajen
Ina qarasawa wajen ya daga hannu zai mareta saina dakatar dashi..."
Duk tsit mutanen dakin sukayi ya cigaba da basu labarin har kawo yanzu dasuke asibitin nan
Duk salati suka shiga yi cikin tsantsar mammaki da alhini
"innallilahi waina ilaihi rajiun, to shi mutumin waye? Kawai daga ganin mutum sai tace shine Deen? Haka fa tayi muku a park rannan ko?"
Ajiyar zuciya kawai Aymaan ya sauke don shi kadai yasan abinda yakeji a zuciyarshi
"to Gaskiya ya kamata nakira yaya na fadamashi, idan aka tafi Hakan akwai matsala, ace duk wanda tagani tace Deen ne, idan ta qara gamuwa da muggai kamar na yau fa babu wani dazai iya taimakonta a kusa fa?"
"A'a, be kamata a kirasu ba, hankalinsu ne zai tashi sosai, kawai mu nemo mafita da kanmu" inji Abbu
"nima Gaskiya am scared Abbu, gwara asan yadda za'ayi don nima abubbuwan datake yi sunfara bani tsoro, haka fa rannan ta dage akan ita dole shi tagani tasamu mukaita zagaye a banza" inji batool
"kai, amma dai yaron nan ya cuceta wlh, cutar da dole sai allah ya sakamata, daga wannan sai wannan? Sai abu yayi kamar yafara warwarewa sai kuma yaqara ta6ar6arewa, kullum abu beci baya sai gaba?" inji ummy hawaye na taruwa a idanunta
"Addu'a yakamata mu dinga tayata dashi Abbu, allah ya kawo mata rangwame a halin datake ciki" inji Ahmad da Tundazu bece komai ba
Kada kai kawai duk sukayi cikin amincewa da Maganarshi
Shidai Aymaan bece komai ba sai kafe waje guda dayayi da ido kawai, allah kadai yasan meke kai kawo a qwalwarshi
Ranar aka sallamesu suka koma gida
Zee ta farfado and she's ok physically amma karka bincika zuciyarta
Zuciyar tata data samu ta lilliqeta da gum tun bayan rarratsata da Deen yayi tasake Fashewa, fasuwar da mawuyacine taqara iya yimata paci kamar yadda tayimata da farko
Tun daga ranar ta chanza, chanzawar da tafi duk na baya
Bata cin abinci sai an tsareta an tilasta mata to anan zataci kadan
Kuma ko zaka yini kanta kana magana bazata cemaka komai ba har ka gaji don kanka ka kyaleta
Daga baya kuma saita fara zazza6i, irin zazza6innan mai zafi sosai
Dr Aymaan ne kullum mai treating dinta, yana iya qoqarin shi na ganin ya bata dukkanin kulawar datake buqata amma a banza, kullum cikin ciwo take ga wani bushewa datakeyi a tsaye
Sosai wannan ahalin suka sake shiga damuwa mai tsanani
Suna son su sanar dasu daddy na Nigeria amma Aymaan ya hana yana cewa it's not proper gwara suyi iya qoqarinsu akanta basai sun sanar dasu halin da ake ciki ba.
Haka Aymaan dama sauran ahalin gidan sukaita iya bakin kokarinsu akanta
Duk safiya bayan sallar asuba zasu shigo dakinsu zee din su zauna tilawar alqur'ani kowa da nashi a hannu itama a bata nata tana dubawa while su suna karantawa
Sosai Hakan yayi tasiri sosai akanta don duk lokacin da suke wannan karatun takan tsinci kanta cikin nutsuwa, zuciyarta ta ragemata zugin data keyi
Da rana kau wuni suke garden da batool wanda zataita iya qoqarinta wajen sanyata nishadi
Da daddare kuma Aymaan zaizo ya fara karanta mata littatafai masu dadi masu sanya nishadi
Haka sukaita iyakar bakin qoqarinsu akanta suna kuma hada mata da addu'a don tabbas lamarinnan sai an hada da addu'a
Wata rana jikinta yasake tashi, zazza6i mai mugun zafi ya rufe ta.
Ranar kowa na gidan beyi barcin kirki ba Haka suka tare wajenta Aymaan na iya bakin qoqarinshi akanta a matsayinshi na qwararren likita
Dakyar suka samu jikin ya lafa tasamu barci drip maqale da hannunta
Su ummy da batool sai dauke hawaye sukeyi akai akai shikuma Aymaan idanunshi sun Kada sosai, jiyake da shima zai iya kuka da yayi mata
Haka yafita dakin ya barta dasu ummy da anan zasu kwana wajenta
A ranar besamu rintsawa ba, haka ya zauna ya kafe waje guda da ido
Tunanuka kala2 ke kai kawo akanshi
Ko yatafi Nigeria neman Deen?
Ko yaje a chanza mashi fuska irinta Deen?
Me zaiyi? Me zaiyi dazai dauke ma zee abinda takeji?
Shi da yasan yadda zai dauke mata abinda takeji a zuciya shiya dinga ji da yayi Hakan, daya jure kowanne irin wahalar da zaisha muddin zai dauke mata wahalar
Yadda yaga rana haka yaga dare, asuba nayi ya miqe ya fice massalaci
Koda ya dawo dakinsu yafara shiga ya tarar da har lokacin barci take
Sake dubata yayi sannan ya cire mata qarin ruwan don yaqare sannan yafita
A gaggauce yayi shirin asibiti ya fita don dama kwana biyu be cika zaman asibitin ba saboda tattara hankalinshi dayayi akan zee
Yauma wani emergency aka kawo wanda lallai ana buqatarshi a aikin shiyasa ya shirya a gaggauce yayi sallama da mutanen gidan yatafi
Bashi ya fito daga asibitin ba sai wajajen 3pm Hakan yasa ya wuce gida kawai don duk hankalinshi yayi gida kuma yanason yaje yaga wane hali zee din ke ciki
Koda ya shigo gidan parking space yashiga yayi parking sannan ya fito
Kamar kullum yau ma lapcoat dinshi riqe take a hannunshi ya fito ya rufe qofar sannan ya fito daga parking space din
Hangen batool yayi ta fito daga garden tayi hanyar cikin gida batareda ta lura dashi ba
Ganin Hakan ya tabbatar mashi cewa zee tana garden din itama don Mafi yawancin lokaci irin wannan can suke zama don sudan debe kewa.
Hakan yasa ya chanza akalar tafiyar tashi zuwa garden din don dama babu wanda yakeson gani kamar ita yanzu
Cikin takunshi ta nutsuwa ya taka zuwa garden din
Tun daga nesa ya hangota zaune bisa wata yar doguwar kujerar garden din ta juya mashi baya so be ganin fuskarta itama kuma batasan da shigowarshi ba garden din
Wasu yan moli moli take kallo dake tsaye a kan wani reshen bishiya suna dan tsuwarsu suna ra6ar juna
_*look*_
Ta tuna abinda Deen yace wancan ranar da suka gansu a school
_*A Good example of us, ko?*_
Lumshe idanu tayi akansu ta bude sannan ahankali tafara waqa
_the word around town.._
_is that you're back in town_
_and I tried not to think about you_
_I tried_
_but it's been so long.._
_and I thought I moved on.._
_but now I really doubt it_
_I do_
_I wonder why you even come_
_it's almost like you're having fun with me_
_and though if I set my eyes on you, it's on avoidable_
_how come oh boy?_
_I thought you've gone for good_
_so how do you!.._
_have to pull me back!"
_I thought you said, you won't be coming back_
_then why did you?!_
_this is really bad!_
_I thought you said you're gone for Good_
Dakatawa Aymaan yayi daga tafiyar dayakeyi yana kallonta cikin wani irin yanayi
_what you did is wrong_
_cos you know all along am doing ok without you_
_you don't want me to.._
_try to move on.. Try oh_
_the heart is too strong_
_can't be with you and can't be without you_
_the truth is that I.._
_wonder why you even come_
_is almost that you're having fun with me_
_and though if I set my eyes on you, it's unavoidable_
_how come oh boy?_
_I thought you've gone for good_
_so why did you?!_
_have to pull me back?!_
_I thought you said, you won't be coming back_
_then why did you?_
_this is really bad!_
_I thought you said you're gone for Good_
Ahankali yafara takawa da baya baya still idanunshi akanta making sure be ankarar daita dashi ba
Saida yayi nisa sannan ya juya yayi saurin barin garden din
Saboda rufewar idanunshi baya ma ganin gabanshi clearly wanda Hakan yasa yaci karo da batool a bakin kofar shiga falo
Daga mata hannu kawai yayi ya wuce don ga yadda yakeji dinnan yasan ko yayi maganar bazata fito ba
Binshi da kallon mammaki batool tayi, kamar ta bishi sai kuma tafasa don wataqila 6ata mashi rai akayi kuma tasanshi idan yana cikin 6acin rai beson kowa ya ra6eshi, Hakan yasata juyowa kawai ta koma garden