Showing 183001 words to 186000 words out of 322641 words

Chapter 62 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6219

kamar zata fadi Saidai bata fadin ba


Sudai Guards dinshi nasu ido don tunda ya dakatar dasu dazu idan bashi yabasu umarnin yin wani abu ba bazasu yi gigin yin wani abin ba


Juyawa yasakeyi zai shiga taqara Kamo hannunshi ido rufe

"No Deen, please don't do this, don’t reject me for the second time, I can't take it, i'll die" tafada cikin kuka sosai hankalinta a matuqar tashe


A matuqar fusace ya sake juyowa, beyi wata wata ba ya daga hannu da niyyar shararawa fuskar mari sai yaji an cafe hannun a iska da qarfi


Zee data tamke idanunta gamm tana sauraron saukar marin taji shiru Hakan yasa ta bude idanun ahankali


Aymaan tagani tsaye gefenta riqe da hannun Deen a iska suna bin juna da fierce kallon kallo

Saurin qarasawa wajen Aymaan tayi
"Aymaan ka kyaleshi, Deen ne fa, shine. Please ka sakeshi kar yayi fushi" tafada tana riqo hannun Aymaan daya riqe hannun Deen dashi


Juyowa yayi ya kalleta cikin matuqar quluwa

"zaki saki hannuna kosai na fasamaki baki?!" Yafada cikin qaraji, fuskarshi na bayyana tsantsar 6acin ran dayake ciki


Sosai zee ta girgiza da yanayin Aymaan wanda bata ta6a saninshi dashi ba Amma so ya riga ya rufe mata ido Hakan yasa taqi saki

"naji, ka fasamin kai ma idan ka tashi just leave him, ina ruwanka da rayuwata!!" itama tafada cikin daga murya


Idanunshi dasukayi mugun kadawa ya kafeta dasu saikuma ya saki hannun Deen din ahankali


Ganin Hakan yasata qara saurin nufar Deen din

"Deen am sorry, besan ko waye kai ba, am very sorry" tafada tana niyyar sake kama hannunshi Hakan yasashi Janye hannun sannan ya turata baya a fusace

Baya baya tasakeyi tana gasping don tasan wannan karon dole takai qasa kuma idan takai qasa saitaji jiki


Jitayi an tareta ta baya an tsaidata daga faduwar


A tsorace tasake bude idanun sai tayi arba da fuskar Aymaan dake kallonta da rinnanun idanunshi

Bata iya cewa komai ba sai kallonshi itama datake numfashinta na qara yin nauyi

Miqar da ita yayi tsaye sannan ya saketa yayi wajen Deen dake tsaye fuskarshi tayi jaa don fushi

Guards ne sukayi saurin tareshi suna kakkama hannunshi


Zuciyarshi ce ta qara harzuqa Hakan yasa ya wuntsilar dasu da iya qarfinshi duk suka sakeshi batareda sun shirya ba sukayi baya baya

"you dog!" Yafada yana shaqo kwalar Deen qirjinshi sai sama da qasa yakeyi alamun zuciyar yan mazan ta tashi


Bïñ hannun da Aymaan ya shaqi kwalarshi Deen yayi da kallo suprisingly sannan ya dago yana kallonshi shima jijjiyoyin jikinshi na tashi

Cikin harshen larabci Aymaan yafara magana
"waye kai?! Waye kai da zaka dora hannu akanta?!!"

Afusace Deen yasa hannu ya kwa6ar da hannun Aymaan daga qwalar rigar tashi, kafin Aymaan yayi recovering daga haka yaji saukar naushi a gefen kumatunshi


Qara Zee tasa tana kiran sunan Aymaan

Baya baya Aymaan yayi saikuma ya dakatar da kanshi daga faduwar dayaso yi


Hannu yasa ya taba gefen bakinshi ya duba sai yaga jini

Sake kallon Deen dake huci yayi sai yayi kukan kura ya nufeshi

Saidai tun kafin ya qarasa gunshi guards dinshi suka tareshi, basuyi wata wata ba suka tarar mashi suka shiga jibga.


Qara Zee tasake saki tana rufe baki hankali a mugun tashe, kuka takeyi kamar zata shide jikinta na wani mugun 6ari


Gaskiyar hausawa dasuka ce sarkin yawa yafi sarkin qarfi don tun Aymaan na iya maida martanin har yakoma kare kanshi har daga baya ma yakasa kare kanshi din.


Ganin Hakan yasa zee nufar Deen dake tsaye yana kallonsu ta Kamo hannunshi

"Deen na roqeqa, kace subari zasu kasheshi"


Wani irin fizge hannunshi yayi wanda har Saida takai qasa

Juyawa yayi zai wuce wajen motar shi tayi saurin rarumo qafarshi daya

"Deen! No! Karka tafi zan mutu!" tafada tana rungume qafar da dukkan qarfinta


A matuqar hasale ya fizge kafar itama yana ja baya yana kallonta da bloodshot idanunta sannan yana nuna ta da yatsarshi datake karkarwa saboda yadda jikinshi ke tsuma don 6acin rai


Sai kuma ya juya ya bude kofar baya na motar ya bude wani akwati ido rufe ya fiffido wrappers din kudinsu nacan ya farka wrappers din yashiga watsamata kudadden ajiki, tsayawa tayi Cak da kukan tana kallon yadda yake warwatsa nata kudadden akai, da wani yaqare Sai ya farka wani har Saida ya qarar da wrappers biyar akanta

"Go away, you brat!!" Yafada cikin hargowa sannan ya juya ya shige motar ya rufo da qarfi.


Ganin Hakan yasa guards din kyale Aymaan da suka yima lilis suka rugo wajen mottocin suka shishiga suka tayar suka bar wajen a 360 suna badesu da qura




Ahankali Aymaan ya bude idanunshi dasukayi mashi mugun nauyi yabi motocin dasuka fita a harabar wajen da kallo sannan ya maido kallonshi akan zee dake zaune har lokacin bata ko motsi


Maida idanunshi yayi ya lumshe cikin azaba yana kiran sunan allah under his breath.


Saida yayi yunqurin tashi sau biyu ya kasa, ana uku yasamu ya tashi zaune Dakyar yana cije lip dinshi na qasa


Koina na jikinshi ciwo yakeyi kamar ana dandaqarsu ga bruises a jikinshi sunyi jaa abinka da fatar hutu dama

Ahankali yasake bude ido ya sake kallon zee dake a sitting position dinta har lokacin


Bude bakinshi yayi Dakyar yafara magana
"kin gani.. Ko? Kinga.. Abinda kika jawo ko?"

Shiru

Shaqar numfashi yayi sannan ya fesar yafara yunqurin tashi, sosai jikinshi yayi laqwas don babu qarya ya jibgu don shi tunda yayi wayau bazai iya recalling lokacin da aka ta6a yimashi irin wannan dukan ba


Ganin bazai iya tashin ba yasa ya qara Dagowa ya kalleta yaga still wuri guda take kallo sai jiyayi ranshi ya kuma 6aci

"ki tashi mutafi" yafada yana kallonta but still bata motsa ba

"Zainab! Am talking"

Nanma shiru


Shima shiru yayi ya tsaya yana kallonta yana qoqarin gano wani abu


Abinka da medical doctor nan take ya gano


Wara idanunshi dasuka tattaso yayi sannan yayi saurin rarrafawa gabanta

"Zainab" yakira sunanta yana waving a gaban fuskarta amma bata ko kyafta idoba

"zee?" yafada yana dan ta6ata kawai sai yaga tayi baya baya

Ba don yayi saurin tarota ba da tasha qasa

"Zainab! Zainab!!" Yafada yana jijjigata amma shiru

Tara yatsarshi yayi a hancinta sannan ya dora kunnen shi daidai zuciyarta yana feeling heartbeat dinta


A rikice ya dago ya karkata ya zaro wayar shi dake aljihunshi still tana jikinshi


Lalubo number Ahmad yayi ya danna mashi kira


Saida takusan katsewa sannan aka daga

"hey!" inji Ahmad daga wancan bangaren

"Ahmed kana ina?"

"lafiya?" inji Ahmad jin muryar Aymaan wani iri

"answer the damn question!" inji Aymaan yana qara jijjiga zee dake sheme ajikinshi

"ina gida, meya faru naji voice dinka wani iri?"


"kazo Ni'ima shopping mall, urgently please"

Daga Hakan ya katse kiran ya maida hankalinshi kanta


"Zainab! Zainab!! Wake up zee!" Yafada yana dan marin fuskarta amma shiru


Waige waige yafara, kasancewar babu mutane sosai a wajen ga kuma motoci dayawa dasuka kakkaresu shiyasa tunma lokacin dasu Deen ke nan ba'a gansu ba.


Ahankali ya maida ta ya kwantar daita sannan ya tashi Dakyar yafara dangyasawa ya fito fili


Waige waige yafara can ya hangi securities, daya na bude gate daya na a zaune

Da dingishi ya qarasa wajensu, tun daga nesa dasuka hangoshi suka fara kallonshi harya qaraso gabansu Dakyar


I.D card dinshi yafara nunamasu, Ganin ko waye yasasu saurin tashi suna tambayarshi lfy suka ganshi haka

Briefly yayi musu bayanin he's attacked By some thugs shi da sister shi dake can unconscious sannan ya gayamasu abinda yake buqata don yimata taimakon gaggawa.


Cikin sa'a aka samu most abubbuwan daya lissafo suka koma wajen zee dake sheme har lokacin

Dukda yadda yakejin kamar kanshi zai rabe gida biyu don sarawa haka ya daure yafara bata taimakon gaggawa


Suna haka Ahmad ya iso supermarket din.


Kasancewar Aymaan dama yariga ya fadamasu wani nanan tafe wajensu yasa yana isowa aka rakoshi wajensu


Sosai hankalin Ahmad ya tashi ganin halin dayaga Aymaan dama zee dake unconscious har lokacin


Cikin qarfin hali Aymaan yace ma Ahmad ya kaisu hospital


Da taimakon Ahmad aka saka zee back seat sannan sukuma suka dawo gaban seat, Ahmad ya tada motar yayi reverse suka fice daga supermarket din.




Asibitin da Aymaan ke aiki suka zarce.

Tun kafin su iso Aymaan ya bugama wani colleague dinshi waya ya sanar dashi Zuwansu shiyasa Koda suka isa akayi saurin kar6ar zee aka shige daita


Da farko Aymaan qin yarda yayi ayi treating ciwukkanshi har Saida ya tabbatar da sun ceto rayuwar Zainab from danger sannan Dakyar su Ahmad suka samu suka lalla6ashi ya yarda.





***



Kwance yake bayan angama treating dinshi idanunshi a lumshe kamar mai barci amma ba barcin ba yake


Shi kadai ne dakin don tunda nurse tagama treating dinshi suka fita suka bashi wuri don ya huta sosai


Qarar bude kofa yaji amma Hakan besa ya bude lumssasun idanunshi ba

"bismillah ummy" yaji Ahmad na cewa Hakan, Hakan yasashi bude idanun babu shiri ya juyo yana kallon saitin kofar


Ummy yagani agaba sai batool a bayanta sai Abbu a bayansu


Yunqurin tashi zaune yafara sai ummy tayi saurin Qarasowa tana taimaka mashi ya ida tashi zaune ta karamashi pillow a baya

Dagowa yayi yana kallonsu sai yaga suma shi suke kallo cikin tausayawa

"sannu Akhie" inji batool kamar zatayi kuka


Dan murmushi yayi mata sannan ya kalli su ummy

"ummy, waya gayamaku?"

"Ahmad ne habiby, muna can hankalinmu Kwance ashe babu lafiya"


Dagowa yayi ya watsama Ahmad mugun kallo shikuma yayi murmushi yana daga kafadarshi


"sannu son, allah ya kyauta gaba amma nayi mammaki ace thugs a supermarket, how come?"

Shiru Aymaan yadanyi sai kuma ya sauke Ajiyar zuciya


"Abbu nidai bansan ya Hakan yafaru ba, kawai nagama siyayya ta nafuto saina hangeta inda nace ta jirani

Amma kafin na qaraso sai naji qarar faduwar abu daga hannunta sai kuma naga tayi wajensu dagudu

Na kwalamata kira amma bata saurareni ba shiyasa nima na qaraso wajen da sauri sai naga ashe wayarta ce ta saki


Saina dauketa na tashi nabita lokacin harta fita waje

Nima saina bita Saidai Koda nafita ban ganta ba don har titi saina nakai amma banga wulginta ba


Dawowa nasake yi da niyyar komawa ciki again sainaji kamar magana a ta parking space din wajen

Saina zagaya, kawai saina hangeta daidai wani ya tureta

I thought faduwa zatayi amma sainaga bata fadi ba, sai nayi saurin nufar wajen

Ina qarasawa wajen ya daga hannu zai mareta saina dakatar dashi..."


Duk tsit mutanen dakin sukayi ya cigaba da basu labarin har kawo yanzu dasuke asibitin nan


Duk salati suka shiga yi cikin tsantsar mammaki da alhini

"innallilahi waina ilaihi rajiun, to shi mutumin waye? Kawai daga ganin mutum sai tace shine Deen? Haka fa tayi muku a park rannan ko?"

Ajiyar zuciya kawai Aymaan ya sauke don shi kadai yasan abinda yakeji a zuciyarshi


"to Gaskiya ya kamata nakira yaya na fadamashi, idan aka tafi Hakan akwai matsala, ace duk wanda tagani tace Deen ne, idan ta qara gamuwa da muggai kamar na yau fa babu wani dazai iya taimakonta a kusa fa?"


"A'a, be kamata a kirasu ba, hankalinsu ne zai tashi sosai, kawai mu nemo mafita da kanmu" inji Abbu


"nima Gaskiya am scared Abbu, gwara asan yadda za'ayi don nima abubbuwan datake yi sunfara bani tsoro, haka fa rannan ta dage akan ita dole shi tagani tasamu mukaita zagaye a banza" inji batool


"kai, amma dai yaron nan ya cuceta wlh, cutar da dole sai allah ya sakamata, daga wannan sai wannan? Sai abu yayi kamar yafara warwarewa sai kuma yaqara ta6ar6arewa, kullum abu beci baya sai gaba?" inji ummy hawaye na taruwa a idanunta

"Addu'a yakamata mu dinga tayata dashi Abbu, allah ya kawo mata rangwame a halin datake ciki" inji Ahmad da Tundazu bece komai ba

Kada kai kawai duk sukayi cikin amincewa da Maganarshi

Shidai Aymaan bece komai ba sai kafe waje guda dayayi da ido kawai, allah kadai yasan meke kai kawo a qwalwarshi




Ranar aka sallamesu suka koma gida


Zee ta farfado and she's ok physically amma karka bincika zuciyarta


Zuciyar tata data samu ta lilliqeta da gum tun bayan rarratsata da Deen yayi tasake Fashewa, fasuwar da mawuyacine taqara iya yimata paci kamar yadda tayimata da farko


Tun daga ranar ta chanza, chanzawar da tafi duk na baya


Bata cin abinci sai an tsareta an tilasta mata to anan zataci kadan

Kuma ko zaka yini kanta kana magana bazata cemaka komai ba har ka gaji don kanka ka kyaleta


Daga baya kuma saita fara zazza6i, irin zazza6innan mai zafi sosai


Dr Aymaan ne kullum mai treating dinta, yana iya qoqarin shi na ganin ya bata dukkanin kulawar datake buqata amma a banza, kullum cikin ciwo take ga wani bushewa datakeyi a tsaye


Sosai wannan ahalin suka sake shiga damuwa mai tsanani


Suna son su sanar dasu daddy na Nigeria amma Aymaan ya hana yana cewa it's not proper gwara suyi iya qoqarinsu akanta basai sun sanar dasu halin da ake ciki ba.


Haka Aymaan dama sauran ahalin gidan sukaita iya bakin kokarinsu akanta


Duk safiya bayan sallar asuba zasu shigo dakinsu zee din su zauna tilawar alqur'ani kowa da nashi a hannu itama a bata nata tana dubawa while su suna karantawa


Sosai Hakan yayi tasiri sosai akanta don duk lokacin da suke wannan karatun takan tsinci kanta cikin nutsuwa, zuciyarta ta ragemata zugin data keyi


Da rana kau wuni suke garden da batool wanda zataita iya qoqarinta wajen sanyata nishadi


Da daddare kuma Aymaan zaizo ya fara karanta mata littatafai masu dadi masu sanya nishadi


Haka sukaita iyakar bakin qoqarinsu akanta suna kuma hada mata da addu'a don tabbas lamarinnan sai an hada da addu'a



Wata rana jikinta yasake tashi, zazza6i mai mugun zafi ya rufe ta.



Ranar kowa na gidan beyi barcin kirki ba Haka suka tare wajenta Aymaan na iya bakin qoqarinshi akanta a matsayinshi na qwararren likita


Dakyar suka samu jikin ya lafa tasamu barci drip maqale da hannunta


Su ummy da batool sai dauke hawaye sukeyi akai akai shikuma Aymaan idanunshi sun Kada sosai, jiyake da shima zai iya kuka da yayi mata


Haka yafita dakin ya barta dasu ummy da anan zasu kwana wajenta


A ranar besamu rintsawa ba, haka ya zauna ya kafe waje guda da ido


Tunanuka kala2 ke kai kawo akanshi

Ko yatafi Nigeria neman Deen?

Ko yaje a chanza mashi fuska irinta Deen?

Me zaiyi? Me zaiyi dazai dauke ma zee abinda takeji?


Shi da yasan yadda zai dauke mata abinda takeji a zuciya shiya dinga ji da yayi Hakan, daya jure kowanne irin wahalar da zaisha muddin zai dauke mata wahalar


Yadda yaga rana haka yaga dare, asuba nayi ya miqe ya fice massalaci


Koda ya dawo dakinsu yafara shiga ya tarar da har lokacin barci take


Sake dubata yayi sannan ya cire mata qarin ruwan don yaqare sannan yafita


A gaggauce yayi shirin asibiti ya fita don dama kwana biyu be cika zaman asibitin ba saboda tattara hankalinshi dayayi akan zee

Yauma wani emergency aka kawo wanda lallai ana buqatarshi a aikin shiyasa ya shirya a gaggauce yayi sallama da mutanen gidan yatafi



Bashi ya fito daga asibitin ba sai wajajen 3pm Hakan yasa ya wuce gida kawai don duk hankalinshi yayi gida kuma yanason yaje yaga wane hali zee din ke ciki



Koda ya shigo gidan parking space yashiga yayi parking sannan ya fito

Kamar kullum yau ma lapcoat dinshi riqe take a hannunshi ya fito ya rufe qofar sannan ya fito daga parking space din


Hangen batool yayi ta fito daga garden tayi hanyar cikin gida batareda ta lura dashi ba

Ganin Hakan ya tabbatar mashi cewa zee tana garden din itama don Mafi yawancin lokaci irin wannan can suke zama don sudan debe kewa.


Hakan yasa ya chanza akalar tafiyar tashi zuwa garden din don dama babu wanda yakeson gani kamar ita yanzu


Cikin takunshi ta nutsuwa ya taka zuwa garden din


Tun daga nesa ya hangota zaune bisa wata yar doguwar kujerar garden din ta juya mashi baya so be ganin fuskarta itama kuma batasan da shigowarshi ba garden din


Wasu yan moli moli take kallo dake tsaye a kan wani reshen bishiya suna dan tsuwarsu suna ra6ar juna

_*look*_
Ta tuna abinda Deen yace wancan ranar da suka gansu a school

_*A Good example of us, ko?*_


Lumshe idanu tayi akansu ta bude sannan ahankali tafara waqa


_the word around town.._

_is that you're back in town_

_and I tried not to think about you_

_I tried_


_but it's been so long.._

_and I thought I moved on.._

_but now I really doubt it_

_I do_


_I wonder why you even come_

_it's almost like you're having fun with me_

_and though if I set my eyes on you, it's on avoidable_

_how come oh boy?_

_I thought you've gone for good_


_so how do you!.._


_have to pull me back!"


_I thought you said, you won't be coming back_


_then why did you?!_

_this is really bad!_


_I thought you said you're gone for Good_


Dakatawa Aymaan yayi daga tafiyar dayakeyi yana kallonta cikin wani irin yanayi

_what you did is wrong_

_cos you know all along am doing ok without you_

_you don't want me to.._

_try to move on.. Try oh_

_the heart is too strong_

_can't be with you and can't be without you_


_the truth is that I.._

_wonder why you even come_


_is almost that you're having fun with me_


_and though if I set my eyes on you, it's unavoidable_


_how come oh boy?_


_I thought you've gone for good_


_so why did you?!_


_have to pull me back?!_


_I thought you said, you won't be coming back_


_then why did you?_

_this is really bad!_


_I thought you said you're gone for Good_



Ahankali yafara takawa da baya baya still idanunshi akanta making sure be ankarar daita dashi ba


Saida yayi nisa sannan ya juya yayi saurin barin garden din


Saboda rufewar idanunshi baya ma ganin gabanshi clearly wanda Hakan yasa yaci karo da batool a bakin kofar shiga falo

Daga mata hannu kawai yayi ya wuce don ga yadda yakeji dinnan yasan ko yayi maganar bazata fito ba


Binshi da kallon mammaki batool tayi, kamar ta bishi sai kuma tafasa don wataqila 6ata mashi rai akayi kuma tasanshi idan yana cikin 6acin rai beson kowa ya ra6eshi, Hakan yasata juyowa kawai ta koma garden


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login