Showing 261001 words to 264000 words out of 322641 words
Chapter 88 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
koma can atsakaninsu suna cigaba da qulla plan dinsu na yadda zasu hada Deen da ainahin ahalinshi.
*2 WEEKS LATER*
"Kaka kinyi shiru" yafada yana kallonta da oily eyes dinshi
Ajiyar zuciya ta sauke sannan tadago ta kalleshi
"kyakyawana me zance?"
"Kaka kifadi Abinda ke ranki, kinsan koma menene kika fada ya zauna ni Kawai izininki nake nema idan kuma baki bani ba zan haqura"
"kyakyawana, bawai hanaka nakesonyi ba, kasan yadda banason kanayin nesa dani koyayane, kodayaushe nafison najika kusadani"
"nima Kaka, kullum burina mu kasance atare amma kema kinsan yanayin aikina yanzu, tafiye2 naciki don hakan na daya daga alamomin nasarar aikin"
"amma baka ganin wannan yasha banban da dukkan tafiye tafiyen dakake? kamal bafa garin zaka bari ba, qasar zaka bari gabadaya. wakasani acan? tayiwu masu satan mutane nema sukeson yaudararka da sunan aiki"
Deen kasa dakatar da dariyar data kufcemashi yayi hakan yasashi darawa ganin hakan yasa Kaka Dan hade rai
"au, wato dariya ma nabaka"
"to Kaka saceni fa kikace za'ayi, kamar wani toy?"
"koma dai menene, ai baka girmi sacewa ba indai wurin wadannan marassa imanin yan kidnafin ne? yo su ina ruwansu da yaro da babba? ai sunma fison babba"
murmushi Deen yayi
"Kaka anan Nigeria ke akwai kidnappers nikuma barin qasar zanyi gabadaya, Kuma wannan tafiyar ba daka zan tafi ba, Alhaji Bashir yasan komai akan tafiyar nan Kuma yabada goyon baya Kuma beyi hakan ba saida yayi bincike sosai sannan kuma shi ainahin wanda zanje wurinshi nasanshi, Dan Nigeria ne amma acan yake dazama shida iyayenshi wadanda sai daga baya nasan cewa ashe sunsan juna da Alhaji Bashir don mahaifin yaron tsohon abokin Alhaji Bashir ne tun yarinta"
"shi mahaifin yaron ne abokin Alhaji Bashir?" inji Kaka
"eh, nima sai daga baya Alhajin ke gayamin bayan namashi magana yasa an bincika, Kuma yaron yanada kirki sosai dukda sau biyu muka ta6a haduwa dashi lokacin sunzo Nigeria harnayi ma mahaifiyarshi waqa kuma dukda yakoma can din zumuncinmu be yanke ba don kodayaushe muna ta6o juna via media"
buga tagumi Kaka Kawai tayi tana kallonshi batace komai ba, tarasa dalilin dayasa kwata2 tafiyarnan bata kwanta mata arai ba
"amma Kaka idan bakyason tafiyar babu komai saina fasa nabasu hqr dama bawai amsa nabasu ba tsayayya"
"A'a niba wai tafiyar ce banaso ba Kawai tunanin kewarka dazanyi nake"
"Kaka kwana uku Kawai zanyi fa, kuma zamu dinga waya ga Lailah ma nan nasan zata dinga zuwa tana debemiki kewa tunda dama tasaba zuwa bare yanzu datasan bananan"
"hakane.. to allah yasa hakan shiyafi alhairi. ai tunda Alhaji ya yarda nasan baza'a samu matsala ba insha allah amma fa ka kula kuma dakaga Abinda beyimaka ba kajuyo gida"
murmushi Deen yayi cikin jindadi
"insha allah Kaka, babu Abinda zai faru sai alhairi insha allah"
"allah ya yarda, dakai da habibun zaku?"
"eh dashi zamu insha allah"
"to allah ya tabbatar da alhairi" inji Kaka
"amin summa amin kakata" yafada yana Dan jawo kaffafunta data miqar saman tutu yana Dan tattausa mata suna cigaba da firarsu wanda yashafi tafiyar tashi
A daren ranar Deen yaba Ahmad tsayyayar amsa akan samun hallartar taron daya gayyaceshi don yayi musu performing.
sosai Ahmad yayi farinciki yakuma bayyanama Deen irin farincikin daya shiga abin haryaso yayi yawa
Nan suka tattauna sosai akan Abinda yashafi tafiyar Inda firr Deen yaqi yarda da zancen Ahmad na ya sauka gidansu ya nace akan shidai zaiyi lodging a hotel
babu yadda Ahmad ya iya haka ya haqura suka cigaba da tattaunawar.
Shirye shiryen tafiyar Deen yashiga yi Inda da taimakon Alhaji Bashir wato mahaifin Lailah akayi musu visa dashi da manager kuma abokinshi Habeeb
cikin qanqanin lokaci komai nasu na tafiya ya kammala ya kasance ranar kawai ake jira
A bangaren Kaka har lokacin bawai tafiyar ta kwanta mata bane kawai dai hakanan take pretending kamar ta yarda amma deep down batason tafiyar jitake kamar idan yatafi ya tafi kenan, sau dayawa saitaji kamar tacemashi afasa tafiyar amma ganin kamar shi yanason tafiyar yasa take hqr badon taso ba.
Acikin wadanda basason tafiyar harda Lailah, tasan zatayi kewarshi sosai dukda koda yananan ba kullum take sanyashi a ido ba amma the thought of zai tafi wata qasar yanasa jin wani iri, kamar zatayi loosing dinshi ko wani abu makamancin haka.
ahaka dai akaita rarrafawa har ranar daren dazasuyi tafiyar
ranar da daddare kasa isashen barci Kaka tayi, juyi kawai taitayi har gari yawaye.
washegari kuma duk tayi wani iri har hakan ya daga hankalin Deen
tambayar duniyar nan yayimata akan meke damunta amma taqi sanardashi, ganin hakan yasa da farko cewa zaiyi cancelling din tafiyar indai tafiyar ce bataso don bazai iya tafiya against her wish ba
dafarko tayi tunanin dawasa yake fadin hakan amma ganin ya tubure akan yafasa yasata komawa lalla6ashi don lokacin har 10am gashi 12pm jirginsu zai tashi
ganin yaqi yarda din yasa Kaka yima Alhaji Bashir waya Inda ta zayyanemashi komai
babu shiri shima alhajin ya iso gidan Inda anan suka hadu dakyar suka shawo kanshi ya yarda da tafiyar don shima a lokacin zuciyarshi tafara bashi akwai wani baqon al'amari dake shirin faruwa dashi
Har airport suka rakasu Inda nan ma da taimakon Alhaji sukayi settling komai don yafisu sanin takan komai awajen tunda daga Deen din har Habeeb wannan ne fitarsu qasar waje nafarko.
cikin qanqanin lokaci akafara sanarwa Inda ake buqatar passengers sufara boarding jirgin
Sosai jikin Kaka yayi lakwas lokacin dasuke bankwana amma ganin yadda Deen ke kallonta keenly yasa taqi bayyana hakan don shima da alamu asanyayen yake
addu'o'in tsari suka yimasu sosai sannan sukayi sallama Deen namasu alqawarin dasun sauka zai chanza layi yakirasu
ahaka suka rabu Inda suka wuce sukabi ayarin passengers dake boarding jirgin
wasu hawaye ne suka zoma Kaka lokacin da Deen ya 6acemata yayinda wani feeling na emptiness ya mamaye zuciyarta
a bangaren su Deen kau shigewa jirgin sukayi Inda duk suka nemi seat number dinsu suka zauna.
shiru Deen yayi ya jinginar da kanshi jikin kujerar dayake akai yana sauraron 6a66atun Habeeb dayaqi qarewa
haka kawai yakejin wani feeling azuciyarshi wanda bazai iya pointing finger akai ba
ahaka akafara sanar da tashin jirgi and in few minutes jirgin ya tashi ya lula sararin samaniya✈️
Ummin Fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*081*
*jiya nasha kira😆 am sorry naso nayimuku jiya amma page dinne banason gutsira muku, Ku ma nasan zakufi son long page, to yaudai ga long page💃🏻*
Qarfe 8:00pm daidai jirginsu Deen yayi landing a babban filin jirgin sama na babban birnin Abu dhabi
fara saukowa passengers din jirgin sukayi aciki hardasu Deen dasukayi matuqar gajiya due to the long journey
kasancewar darene yasa koina yake tarr da haske yadda kasan ba dare ba gashi sai hada hada akeyi gwanin sha'awa
saida suka gama clearing din komai suka amshi luggages dinsu sannan suka fito suna tafe suna qarewa wajen kallo Acikin zuciyarsu suna yaba kyau da tsarin qasar.
basu sha wahala ba suka samu cab wanda zata kaisu hotel din da Ahmad yariga ya kamamasu tunkafin zuwansu suka shige suka kama hanya
A gaban qayyataccen hotel din aka saukesu suka shiga bayan sun sallami mai cab din
basu sha wahalar locating masaukinsu ba don dama Ahmad yariga yayi settling komai kuma yaturomasu information about komai don haka Kawai zuwa sukayi aka tantancesu sannan aka rakasu dakinsu.
kasancewar agajiye suke sosai yasasu yin wanka Kawai suka rama sallolin da'ake binsu sannan kowanne yabi lafiyar gado.
*WASHEGARI*
Tunda safe Deen yafita ya chanzo masu layi don babu Abinda yakeson ji a lokacin kamar muryar kakarshi
he missed her so much don jiyake kamar yayi wata daya baya tareda ita ne
setting komai yayi sannan ya zauna zaman jiran lokacin da aka dibarma SIM din kafin yafara aiki
to whine away time saiya ciro laptop dinshi yafara yan dube dube aciki, duk Abinda yakeyi habeeb nacan nade kan gado don shi dama tun bayan sallar asuba yakoma ya kwanta bemasan lokacin da Deen yafita nemo layi ba.
yana zaune yana aikinshi a laptop yana sipping tea dayasa aka kawomashi wayarshi tayi beeping
ajiye mug din hannunshi yayi ya dauki wayar yaduba, gani yayi sms ne na companyn SIM card din alamun yana iya amfani dashi yanzu
gyara zama yayi yafara saka number wayar Kaka cikin zumudi yanajin wani dadi a zuciyarshi.
ko kwakwarar ringing biyu batayiba aka daga kiran kamar dama ita akejira
"kyakyawana?.." yaji muryar Kaka daga dayan bangaren
wani sanyi yaji ya ratsa zuciyarshi lokacin da muryarta ta doki kunnenshi hakan yasashi sakin kyakyawan murmushinshi
"Kaka ta"
"kyakyawana, kasan tun yaushe nake jiran kiranka? meyasa baka kirani ba sai yanzu?" yaji tafada muryarta.na dan breaking
"Kaka sai yanzu layin yafara aiki, nima naqosa nakiraki naji muryarki, nayi kewarki"
"nima kyakyawana, ni sai yanzu nake danasanin barinka yin tafiyar nan. ina kewanka sosai ga mafarkai da naitayi jiya... yanzu dai yaushe zaka dawo?" tafada cikin muryarda kanaji kasan tana cikin damuwa sosai
"mafarkai? mafarkan me Kaka?"
"babu komai, insha allah alhairi ne. yanzu dai yaushe zaku dawo?"
murmushi Deen yayi
"Kaka duka yaushe mukazo? jiya fa mukazo"
"nidai na qagara kadawo ne"
"zamu dawo kaka insha allah, kinga saima fa gobe ake taron, yau dai zamu hadu da mutumin muyi shirye shiryen daya kamata, gobe muje muyi masa aikinsa jibi mu juyo insha allah"
Ajiyar zuciya Kaka tasauke ahankali sannan tace
"to allah ya yarda ya bada sa'a yakuma maidoku lfy"
"amin kakata, kinga bamu gaisa bama ko? fatan jiya kinyi barci lfy kinkuma tashi lfy"
"hmm ai jiya barci rabi da rabi nayi, kwata2 gidan babu dadi idan babu kai aciki"
"nikuma jiya barci harda minshari, dakyar nasamu sallar asuba ma" yafada cikin sigar tsokana
"ja'iri, dama nasan bawani sona kake ba, wato ni inanan nakasa barcin kirki saboda kai kaikuma kana can kana barcinka hankali kwance"
dariya Deen yayi
"to Kaka me yafi raina, wai kinga qaton dakin damuke kuwa? ga a.c ai dole na shari barci na" yafada cikin dariya cikin son lighting up mood din Kaka
"ah lallai, gwara kau kashari barcinka.. ina habeebun ko batare kuke ba?"
dagowa Deen yayi yakalli habeeb dake nade cikin bargo har lokacin yadan ta6e baki yace
"gayacan nade yanata sharar barci"
"barcin lafiya yanzu Qarfe tara koko ku nan dare ne?"
"A'a, to mu nan Qarfe goma ma, Kawai lallaci ne tunda muka dawo sallar asuba yabaje ko motsi bayayi"
"to kodai a.cn nasu na daban ne shiyasa idan mutum ya kwanta beson tashi? kaima fa cewa kayi saida ka makara da asuba"
dariya Deen yayi cikin tsokana yace
"yo dama tayaya zaki hada a.c din turai dana Nigeria? sanyinshi ma na dabanne har wani feshi feshi ruwa masu qamshi yake"
"A.cn?!!" inji Kaka tana kwalalo idanu
dariyar da Deen yafashe daita ne yasata gane ashe shaqiyanci Kawai yake mata
"zakaci qaniyarka ne, badai ka maidani kakarka ba?" tafada tana kwafa
"to dama mecece?" yafada cikin dariya
ahaka suka shiririce sunata kwasar fira yadda kasan ba kudinsu suke qonewa ba
saida suka jima suna wayar sannan sukayi sallama kowanne farinciki fall zuciyarshi
yana gama wayar da Kaka yakira Alhaji Bashir Inda shima ya sanardashi isarsu
suma sundan dade suna waya sannan sukayi sallama
daga shi sai ya juya akalar kiran zuwa ga Ahmad
ya sanarda Ahmad isowarsu tun jiya anan Ahmad kecewa yana kan hanya ma don shima tun jiya yake baza idanun ganin kiranshi shiru, Jin hakan yasa Deen cewa to saiya shigo din sukayi sallama ya katse kiran
sake kallon Inda habeeb yake kwance yayi ya girgiza kai yamiqe yanufi gadon
yaye bargon dayayi rufa dashi Deen yayi wanda hakan yasashi bude idanu babu shiri
"kasan allah? zan fita nayimaka booking flight kakoma Nigeria tunda barci yakawoka nan din" inji Deen yana hade cikkakun giranshi
murza idanu habeeb yashigayi yana qoqarin tashi zaune
"wannan ne kuma bazai yiwuba, idan kaga nabar qasarnan saina gama zagaye koina lungu da saqo nacikinta sannan, ca6! inzo qasar waje jiya inkoma yau? wasama kenan"
sakin bargon Deen yayi yana kwafa yanufi toilet yana cewa
"wasa kake gani, zaka gane ne"
da haka yashige toilet don freshen up.
Babu jimawa Ahmad ya qaraso, direct dakinsu yanufo don dama shi ya kamamasu dakin, lokacin har sunyi wanka duk sun shirya
cikin farinciki Ahmad ya tarbesu yanamasu sannu dazuwa
yadda Ahmad yanuna farincikin zuwansu har mammaki yaba Deen don shidai yana mammakin irin wannan soyayyar da wannan gayen kemashi.
anan suka zauna suka shiga tattaunawa akan event din gobe
sosai suka baje suna fira don daga Ahmad har habeeb ba'asan gwani ba a surutu gwara gwara ma Deen din don ko rabin d'iminsu bayadashi
saida sukaji anfara kiraye kirayen sallar zuhr sannan dik suka tashi suka fita masjid din hotel din sukayi sallah suka dawo
anan Ahmad yayi suggesting idan sunaso saiya dan zaga dasu gari to whine time away
da Deen yace A'a amma da habeeb yanace akan don allah sutafi din ya haqura ba don yasoba don shi becika son saurin shishigewa mutum ba yafison ya tsaya matsayinshi
shiryawa sukayi suka chanza kaya sannan suka fito
amotar da Ahmad yashigo daita suka shiga Inda Ahmad ne ke tuqin, suka fice daga hotel din.
***
A bangaren zee kau tafara adapting da wannan sabon halin nata data tsiro dashi
yanzu batada wani buri daya wuce ta tsaida hankalinta waje guda itama tayi wani abin kirki koda guda ne
ta dade tana 6atama kanta lokaci batareda tasani ba yanzu batason wasting any single second abanza Kuma
ita sai yanzu dawowarta Dubai kebata haushi, akan wani banzan dalili tabar qasarta ta nisanci iyayenta takuma datse karatunta
idan tatuna da bata baro Nigeria ba da wannan shekarar zatayi graduating saitaji wani baqinciki ya mamaye zuciyarta
akanshi tabar makarantarta lokacin da takusan gamawa kuma anan din ma saboda shi taita canje canjen school while shi yanacan yana gina rayuwarshi hankali kwance, idan ta tuna hakan ba qaramin zafi takeji a zuciyarta ba
shiyasa yanzu ta zage damtse bata barin komai yayi distracting dinta komai qanqantarshi, sotake itama tazama wani abu, she want to made it also, she want to move on.
hakan yasa yanzu ta tattara hankalinta kacokam ta maida ga karatunta, bata wasa dashi ko kadan, ta maida dukkan attention dinta akai shiyasa wani lokacin bata cika sanin Abinda ke wakana a gidan ba.
yau ma kamar kullum tana zaune cikin dakinsu a tsakiyar gadonsu littatafai takoina tana aiki
tsabar yadda hankalinta ya dauku ko sanin shigowar batool batayiba sai jitayi an fige pen din hannunta
saurin dagowa tayi adan tsorace, ganin batool ce sai tadanyi tsaki tana girgiza kai
hayewa kan gadon batool tayi tana cewa
"bookworm, ke shikenan idan kika samu littafi bakyaji bakya gani, dama haka kikeda tsoron exams? is better kiragewa kanki don munan bamada tsaurin exams kamar can qasarku dazakiyita abu guda kamar cin qwan makafi"
harararta zee tayi
"wake tsoron exams?"
"ke mana, tunda exam ya gabato kinwani addabi kanki da karatu kullum abu daya ko gajiya babu, gwara ki sassautawa.kanki don kanki bursting zaiyi abanza ingayamaki"
ta6e baki zee tayi tace
"to naji bani pen dina Kuma ni ba don exams nake karatu ba don exams be ta6a tsoratani,ba saboda akodayaushe ashirye nake ba kamar kuba dakuke bari sai yazo gab sannan kuyita tsalle tsalle" ta qarashe tana fige pen dinta daga hannunta taduqa tana cigaba da rubutunta
ta6e baki tayi tace
"kyaji dashi... wai kinsan wani abu?"
batareda ta kalleta ba ta girgiza kai
"dazu mukayi waya da habiby" tafada tana farr da idanunta
mere baki zeetayi tace
"iyee? shagali"
"yacemin he's very busy yau don yanzu haka yana tareda wani babban baqo ne" inji batool tana kallon zee dake sauraronta absent-mindedly
"allah sarki" inji zee tana cigaba da Abinda take
"Kuma kinsan wani abu?" batool tasake tambaya
rolling idanu zee tayi cikin qosawa sannan tadago ta kalleta
"don allah don annabi batool spare me, wai bakiga abinda nake ba ne? don allah ki kyaleni hakanan sai distracting dina kike da labarai marassa ma'ana" tafada cikin qosawa
riqe ha6a batool tayi tana kallonta harta gama sannan ta kada kai Kawai ta miqe batareda tace mata komai ba tafice daga dakin fuuu
binta da kallo zee tayi tadanyi shiru na wani lokaci saikuma ta daga kafadu tajuya ta maida hankalinta akan abinda takeyi
***
sunyi yawo sosai agarin Inda Ahmad ya shiga dasu wurare daban daban qayattatu na garin.
sosai sukaji dadin wannan fitar don sun kashe kwarkwatan idanunsu ba dan kadan ba
daga qarshe saida Ahmad yabiya dasu gidansu Inda sukaje suka gaida su umma
sosai sukayi musu tarba na musanmman don harda baban Ahmad suka tadda gidan
anan suka qarashe wunin sai gab da magrib sannan suka kamo hanyar hotel din
wannan yar fitar dasukayi ba qaramin sabo yajawo ba tsakanin gayun uku don lokacin dasuka dawo ma sun dade suna fira kafin Ahmad yatafi akan sai goben idan sun hade wajen event din
Bayan tafiyar Ahmad Deen yasake bude laptop dinshi yana qara shiri na aikinsu na gobe
sosai mutuncin ahalin Ahmad ya burgeshi shiyasa shima yaji yanason yimasu aiki na burgewa
haka yakusan raba dare yana aiki Inda habeeb uban rakad'i tun yana damunshi da 6a66atunshi na santin zaga garin dasukayi har barci yaci qarfinshi ya bugas yabarshi anan
shima saida barcin yafara cin qarfinshi sannan ya haqura ya kwanta zuciyarshi cikeda tunanin event din na gobe
*WASHEGARI*
Kasancewar yau Saturday yasa bayan sallar asuba duk komawa barci sukayi musanmman zee data kusan raba dare jiya tana karatu don da asuba ma dakyar batool ta iya tadata tayi sallah takoma tasake bin lafiyar gado
ahankali tafara motsi da idanunta dake arufe saboda hasken rays din rana dayayi reflecting fuskarta
Dan yamutsa fuskar tayi tana yin juyi agadon tana lallube involuntaryly
Jin bata ta6o komai ba yasata qara miqa hannu tana lallubawa nan ma wayam hakan yasata fara bude idanunta dabasu gaji da barcin ba ahankali
waiwaigawa tayi taga dagaske ita kadai din ce adakin hakan yasata miqewa zaune tana miqa agajiye
ahankali take bin dakin dake wani qamshin dadi da kallo ganin yadda yake fess fess tana wondering yaushe aka gyarashi, kardai ace ranan barci tayi sosai
duba yar qaramar agogon dake kan bedside locker tayi taga duka Qarfe tara ne da yan mintuna Kuma a irin wannan ranakun na weekend suna kaiwa har 10 kwance
lallai yau batool yan aikin ke bisa kai tunda harta tashi dawuri haka hardasu gyaran daki.
sauko qaffafunta tayi daga kan gadon tana qara miqar da gajiyayyun ga6o6in jikinta sannan ta tashi tawuce hanyar toilet
brush tafarayi sannan tayi wanka sannan tafito cikin bathing robe
Dan dakatawa tayi daga bakin qofar toilet din ganin gadon data tashi tabari ayamutse yakoma tsaff tsaff kamar ba'a ta6a kwanciya akai ba gawani qamshi da dakin yaqara dauka
da mammaki tabi koina na dakin da kallo taga bakowa hakan yasata ida qarasowa dakin walking slowly
to waya shigo yagyara gadon daga shigarta wanka? tambayar datayiwa kanta kenan
ganin Babu mai bata amsa yasata wucewa closet dinsu tazaro wata light silky gown kalar yellow ta shirya acikinta a gurguje sannan tadan shafa roll on mai sanyin qamshi tazura takalmin soso ta bude kofar tafice
ahankali take saukowa a stairs din tana qarewa gidan kallo saboda wani extra kyallin dayake
gidan yasaba zama cikin gyara da