Showing 123001 words to 126000 words out of 322641 words

Chapter 42 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

4304

da kalar furucin da zaiyi akanki marar dadi, maimakon ayimiki jaje sai allah kara?

Sai naji kin bani tausayi, sai kuma naji ba dadi kasancewar nine silar Hakan

A ranar danaje na gayawa kaka saita cemun idan nazo school washegari nabaki hqr

Da qudurin Hakan nazo school din amma bakizo ba

Washegari ma haka, Washegari ma haka.

Sai naji banji dadi ba da tunanin qila nine silar rashin zuwanki din


Kwatsam ranar monday ina zaune ina karatu naganku kamar daga sama keda qawayenki

Na tashi ina kallonki ganin yadda kike bina dawani irin kallo, duk sai naji badadi don nasan dole kiji haushi na


Naso baki hqr a lokacin sainaga a matuqar fusace kike kuma kinqi bani damar magana sai tsawar da banso kike yimin Hakan yasa nafara gano dalilan dayasa mutane basa sonki, bakida kirki


Qawayenki sunyimin barazanar ko nazama errand boy dinki ko kisa akamani wai kawunki commander sojane uncle dinki kuma commissioner of police


A lokacin na yarda da Hakan ne ba don tsoro ba A'a sai don nabaki damar hucewa"


"qawayenki dama ke kanki kunamin kallon psycho nikuma saina biku ahaka dukdon mu rabu lafiya

A cikin kwanakin dakika maidani errand boy dinki da ida gano dalilan dayasa mutane basa sonki

Ranar da kika watsamin coke kuma ya ida tabbatar min da bakida kirki


Amma kuma saina kasa gayawa kaka ainahin abinda yafaru kawai nabar abin a matsayin tsautsayi nakuma yi alqawarin fita daga hanyarki gabadaya Saidai kuma a qasan zuciyata Koda yaushe kina fadomin a rai in dinga wondering ya kike, banji haushin abinda kika yimin ba a lokacin don ke kallon mahaukaci kikemin tayaya zaki yarda da abinda na rubuta? Saina maida laifin kaina saboda nasan da ban ta6a miki kayaba da duk Hakan be faru ba"


"saina yanke shawarar fita harkarki kwata2 wanda Hakan yasa Koda nadawo school nabar zama mazauni na nafara zaman library, nayi kwana uku da dawowa, Kwatsam sai gaki kin shigo library din kema

Naso intashi inbar wajen amma saina kasa sai naita kallon ki inajin wani feeling da bansan kona menene ba, inajin wata kewa taki wanda bansan dama inayi ba

Sai kema kika dago idanu muka hada ido Hakan yasa gabana yafadi

Sai naga kema kin kafeni da kallo Hakan yasani jin uneasiness saina tashi na fita

Bansan kin biyoni ba sai gani nayi ansha gabana

Gabana yasake faduwa saboda bansan dame kika zo dashi ba kuma a lokacin saboda nariga tayi entitled dinki a matsayin marar kirki

Amma jin kina bani hqr yayi matuqar bani mammaki

Ban ta6a zaton Hakan ba don nayi tunanin wata tijarar zakiyimin sai naga akasin haka, kika bani hqr kuma fuskarki ta nuna you're sorry din har cikin zuciyarki

Sai naji kin burgeni, saina qaryata daya daga cikin magangganun da mutane keyi akanki, Girman kai.

Saina qaryata Hakan don da kinada girman kai bazaki ta6a bani hqr ba

Saina hqr muka zauna muka fara magana, a lokacin kuma saina lura you are so simple don dukda a lokacin bansan ko ke wacece ba na fahimci ke yar manya ce amma kuma kika saki jikinki dani

Anan kika gayamin abinda ke tsakaninku da mr ibrahim

Tun anan Naso na nuna miki kuskurenki na gaba da malami amma kuma saina fasa saboda ba lallai bane ki fahimceni

Sainaji inason taimakonki a subject din don naga kamar kina fargabar faduwa sai nayi maki tayin Hakan kuma kika kar6a hannu bibbiyu, anan kuma naqara tabbatar da rashin girman kanki"

"ahankali ahankali naita fuskantar halayenki wanda sai nakusa dake kawai zai san su saina fuskanci kyawawan halayenki sunfi marasa kyan yawa

Daga baya kuma na fuskanci ashe rashin qawayen kirki yasa kike wasu abubbuwan ganin daga baki shawara akan gabarki da mr ibrahim kika nuna damuwarki kema akai kika kuma nuna kinason ku shirya, Hakan ya tabbatar min cewa eh daga qawayen ne don a dan lokacin damukayi tare naga kamar su babu ruwansu da karatu, they're not serious at all shiyasa nima na kawar da hankalinki daga kansu ta hanyar baki lokacina da gudunmawa gwargwadon ikona don ganin kinyi nasara"


Dakatawa yayi ya dago yana kallonta yaga itama shi take kallo babu ko kyaftawa

"Bansan sadda nafara sonki ba, abinda nasani shine kina burgeni amma bansan sadda Hakan ya rikide zuwa so ba.


Na fuskanci Hakan ne a zamanmu na asibiti, a lokacin nasan na kamu da makauniyar sonki, a lokacin da aka sallamemu Sainaji kamar Kada a sallamemu kamar muyi ta zamanmu a asibitin muddin zaki dinga zuwa sau biyun nan ina ganin ki, ranar da aka sallamemu sosai jikina yayi sanyi, najini so empty kamar wanda kika tafi mashi da wani abu mai matuqar muhinmmanci...."


Cigaba yayi da bata labarin yadda yayi missing dinta kamar yadda nakawo a last page har kawo ranar datazo gidansu da yadda beji dadin yanayin datazo dashi ba da kuma fasa niyyar amsar number ta dayayi, ya gangaro zuwa kiran dayasa kaka taita yiwa mummy don yaji muryarta har zuwa lokacin da akace tayi tafiya har zuwa lokacin resuming dinsu da abinda yafaru har zuwa kawo yanzu dasuke zaune.


Shiru yadanyi saikuma ya saki Ajiyar zuciya

"Zainab, am not begging love From you, nasan bazan ta6a samuba saboda bankai matsayin Hakan ba, Kiyi hqr naci amanar abota, kin riqeni a matsayin aboki nikuma na chanza tawa manufar gareki"

"meyasa kake ganin bakakai matsayin ba?" inji zee karo na farko tunda suka zauna

"saboda ta koina akwai banbanci atsakanina dake"

"meye banbancin?" inji zee again

"zee, ke diyar masu kudi ce, you're born with a sliver spoon in your mouth, nifa?"

Dan murmushi tayi sai ta kada kai tace
"bayan wannan fa?"

Shiru yayi yana tunani saikuma yace
"family, kinada families masu sonki sosai, nifa? Kaka ce kawai"

"kakan ba family bace? Kaka kawai ce? Soyayyar kaka ba soyayya bace?"

Shiru yayi yana kallonta

Ajiyar zuciya ta sauke tace
"tunda muka zauna nan kake fadamin dalilan dayasa kafara sona mun dauki kusan 30mins kana lissafosu dakuma bayyana yadda kakeji aranka game dani amma dakazo akan dalilan da zaisa ka haqura dani sai naga ko minti daya bakayi ba, hasalima duka dalilai ne guda biyu kacal, marassa tushe"

Shiru yayi still yana kallonta batareda ya iya cewa komai ba

"miye banbanci na dakai? Meye banbancin mai kudi da talaka, atsakaninmu mu yan Adam ke akwai banbanci amma a wajen Allah fa?"

Girgiza kai yayi sannan ahankali yace
"babu... Sai wanda yafi tsoron allah"

Murmushi tayi sannan tace
"families kuma, dama kasan wasu families dinane banida labari? A tunanina mummy da daddy kawai ka sani koko don kai bakadasu kake jin kamar bakadasu? Daga sama ka fado? Kaima dole kanada baba da mama kuma sun rasu, ba Haka kaceba?

Yakuma za'ayi kace bakadasu? Ina kaka? Ita ba family bace? Ko bata kai matsayin a kirata da Hakan ba?"

Shiru yayi nan ma yana jin zuciyarshi na wani iri

"soyayya babu ruwanta da mai kudi, marar kudi, mai kyau, marar kyau, yare, qabila, addini... Babu ruwanta

Makauniyace, marar dan jagora duk abinda tasamu kaimashi wafta take ta damqe gamm

Mai so na asali bazaiyi fargaba akan banbancin komai ba tsakaninshi da abinda yake so zai soshi ne yakuma tsaya tsayin daka akan Hakan no matter what

Amma tunda abotarmu ne bakason ya wargaje, fine mu tafi a Hakan, Abokai" tafada tana murmushi

Saita fara yunqurin tashi, saurin rigarta tashi yayi yana cewa

"yes, yes nagane, nagane Hakan Zainab, I was so stupid to think of that, a lokacin babu abinda nake hasasowa idan na tunkareki sai rabuwa, rabuwa na har abada kuma Hakan shine abu na qarshe da zanso yafaru damu because... I LOVE YOU"

Dagowa tayi tana kallonshi

"yes I love you, I love you! I love you!! Please give me a chance, give me a space no matter how tiny it is in your heart, please love me back, give me a chance... Please"


Tunda yafara take kallonshi babu kyaftawa tanajin zuciyarta na kumburi don shauqi

Kallon pleading face dinshi tayi data koma abin tausayi saita miqe ta dauki jakkarta da wayarta ta rataye jakkar

Binta da kallo yayi tayi zuciyarshi na bugawa da qarfin gaske

Dagowa tayi ta kalleshi taga shima ita yake kallo babu kyaftawa

"idan ban baka space ba a zuciyar tawa fa?"

"zan roqi kibani dama nayi jaraba kutsawa har nasamu nasarar yin Hakan watarana" yafada ahankali

"idan nabaka kuma fa?"

"zanfi kowa farinciki a duniya" yafada still yana kallonta zuciyarshi kuma bata bar bugu ba


Wani kayattacen murmushi tayi sannan tace
"Go ahead, kafi kowa farinciki a duniya"

Saita juya ta nufi hanyar fita

Dan yamutsa fuska yayi cikin rashin fahimta

Yafi kowa farinciki kuma?

Wani abu ya gifta mashi a qwalwa

Yace zaifi kowa farinciki a duniya idan ta amince dashi
Kuma tace yafi kowa farincikin

Kenan?

Ta amince?

Dagowa yayi saurin yi saigani yayi harta fice

"OMG! Ta amince! Ta amince!!!"... ✍️


Ummin fasihu πŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:37 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEEN πŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*














*042*











*DEEZEENπŸ’ž*








Saurin tashi yayi ya fita Saidai ya waiga ta koina babu ita.

Duba agogon hannunshi yayi sai yaga har 1pm ta dan gota kuma dama tanada lecture qarfe 1


Murmushi yayi ya saka hannu yana dan yamutsa gashin kanshi ya nufi hanyar department dinsu.


Tun daga nesa ya hango alamun class din karatu ake amma dukda Hakan be hqr ba ya zagaya ta dayan side din class din yafara bin bango ahankali kamar wani qwararren dan F πŸ˜’



Koda yazo wajen window saiya leqo ta gefe ahankali yana scanning din iya inda yake iya hangowa amma be ga ko wulginta ba


Hakan yasashi yin qasa ya rarrafa don kar aganshi ta window yawuce dayan windown sannan ya miqe ahankali ya jingina da bango yasake leqawa ahankali ta gefen windown


Qara bin iya inda zai iya gani da ido amma be ganta ba


Har zai qara gaba sai kuma yaga windown gaba ai na masu zama baya ne kuma ya tabbata Zainab bata zama baya

Hakan yasa yaqara dan leqawa yana dan wurwurga idanu ta koina

Saikau gashi ya ganta a row din tsakiya zaune Littafi kan desk dinta ta buga tagumi da hannu daya tana taunar gindin biron hannunta hankalinta akan lecturer din

Murmushi ne ya su6uce mashi saiya qara gyara tsayuwa yana cigaba da leqenta


Jin wannan feeling din tayi wanda takeji idan yana kallonta Saidai bata wani maida hankali akai ba don tasan bayanan


Tunani tayi ko ya gane hausarta dazu? Sai kuma tayi murmushi tana cigaba da taunar biron hannunta, allah yasani yau tana cikin farinciki, farinciki marar musaltawa


Kamar ance ta waigo ta windown gefen damarta sai taga kamar abu na leqowa yana komawa

Hakan yasa ta kurawa wajen ido

Shikuma ganin ta kallo wajen yasashi dan qara leqowa sosai yadda zata ganshi


Wara idanu tayi ganin shine sai kuma tayi saurin kauda kai tana kallon lecturern dake koyar dasu

Lallai ma Deen, baya tsoron ko aganshi ma?
Tambayar da tayiwa kanta kenan


Haka aka cigaba da lecture din rabin hankalinta akan lecturer rabi kuma akan Deen


Duk lokacin da zata juyo ta kalloshi sai taga yamata murmushi ya daga mata hannu saita kauda kai kuma


Ahaka har lecture din ya qare lecturern ya fita


Ganin Hakan yasashi zagayowa da sauri shima don tarbonta

Zee daketa sauri ta fito itama taci karo dashi a waje

"har kun gama?" yafada yana qarasowa yana mata murmushi

Murmushi kawai itama tayi mashi tana lura da yadda wasu ke kallonsu

"kai zan tambaya, harka gama la6en?" tafada tana nufar hanyar fita

Shima Binta yayi suka jera yana cewa
"eh, amma fa nasha wuya, bayana ciwo" yafada yana 6ata rai

Ta6e baki zee data kasa hada ido dashi tun dazu tayi tace
"dakyau"

"hakama zakice?" yafada yana marairaicewa

Murmushi kawai tayi ta kauda kai, shi bemasan kunyarshi take jiba

Tare suka nufi masjid don har ankusan kabbarawa

Kowa nashi nashen yayi, basu dade da shiga ba aka tada iqama


Kusan tare suka fito don Deen na fitowa itama tana fitowa


Tare sukaje cafteria sukayi siyayyar abinda zasu dan ci kowa daidai aljihunshi sannan suka wuce usual Wurin zamansu idan basa library



Zama sukayi Deen yafara bude masu ledar chips dinshi suka shiga ci tare


Shiru wajen ya dauka na wani lokaci bakajin komai sai sanyayar iska dake kadawa sai kukan tsintsaye dake kai kawo

Deen daga kai yayi yana kallon wasu balbelu dasuka zo suka wuce ta gabansu

"look" yafada yana nuna mata da yatsa

BΓ―Γ±su da kallo itama tayi

"suna tayamu murna suma" yafada yana murmushi

Itama saita tsinci kanta da murmusawa

"the birds are also singing, suma suna tayamu murna... Kalli can"

BΓ―Γ± inda ya nuna tayi da kallo sai taga yan moli moli ne guda biyu mace da namiji bisa kan wani reshen bishiya

"A good example of us, right?" yafada yana kallonsu yana murmushi

Itama su take kallo fuskarta dauke da murmushi, ahankali tace
"so beautiful"

"yes, love is beautiful and amazing" yafada sannan ya maido kallonshi akanta Hakan itama yasa ta juyo tana kallonshi shima



"Nagode Zainab, Nagode da kika bani damar jan ragamar zuciyarki, I promised you bazaki ta6a danasaniba. Zan jagora agareki, jagora dazai jagoranceki zuwa duniyar farinciki, zan iya sadaukar da komai akanki zee na, komai"

"promise" inji zee ahankali

"promise you'll never let me down, no matter what" tafada tana kallonshi tanajin hawaye na neman taruwa a idanunta

Kama hannunta yayi cikin nashi ya matse
"nayi, nayi alqawari my zee, I'll never let you down insha allah don letting you down is equal to letting myself down, down to grave"

" If I could chose between loving you and breathing I would use my last breathe to say I LOVE YOU." Sai kuma yayi interlocking din yatsunshi da nata ya dago hannun yana kallo

Itama kallonsu tayi dukda tasan be dace ba Amma takasa hanashi

Murmushi yayi ya kalleta, itama shi ta kalla not saying anything

"yanzu nagane dalilin space dake a tsakanin yatsu na da naki

Anyisu ne don yatsunmu su maye gurbinsu, kamar haka" yafada yana dan daga hannayen nasu


Murmushi tayi sosai tanajin wani dadi na ratsa zuciyarta, Gaskiya soyayya dadi gareta musanmman kaso aka soka, wayyo dadi 😍


Zame yatsunta tayi daga nashi ta duqa zata dauki juice din gabanta

Saurin riganta yayi ya dauko mata ya miqamata

"ki dinga fadamin duk abinda kike so idan ina kusa, kibar wahalar da kanki, feel free wajen sakani komai, dama ni errand boy dinki ne"

Murmushi tayi kawai ta amsa ta dan kur6a don harya bude mata


Haka sukaita zama wajen Deen nata tarairayarta, wasu abubbuwan ma har mammaki yake bata don batasan ya sansu ba, a ganin ta babu abinda ya iya a faggen love, batasan yan shiru shiru dinnan akwai iya buga loveπŸ₯°

Suna ahaka har drivernta yazo

Saida ya rakota har motar, kafin bala yama zagayo shi ya bude mata kofa, babu abinda ya dameshi ko lura da kallon da daidaikun mutane ke masu beyi ba

Shiga zee tayi ya sunkuya ya maida mata yar jelar rigarta da bata ida shigewa ba sannan ya rufo mata kofar ahankali

Bala daya saki baki yana kallon ikon allah ya lalla6a yakoma cikin motar gulma fall ranshi

Sunkuyowa yayi jikin glass din Hakan yasata wining din glass din qasa

Murmushi suka yima juna

"bye.. Ki kulamin da zuciyata"

Murmushi tayi sannan tace
"nima haka"

"kema me?"

Blushing tayi tana dauke kai tace
"yadda kace"

Murmushi yayi
"to shikenan, qila maganar ke miki wuya amma na gane ai, zan kula miki daita sosai and please.. A taimaka a daga wayata yau.. Please"

Kallonshi tayi taga yadda yawani marairaice

Murmushi kawai tayi tafara wining din glass din motar sama tace
"bye"

"bye.. Godiya nake"

Jin an tada motar yasa yadanja da baya yana kallonta dukda baya hangenta amma yasan itama shi take kallo

Ganin xa'aja motar yasashi fara daga mata hannu yana murmushi har motar ta daga ta nufi hanyar gate

Bebar daga hannun ba har Saida suka fita daga school din

Ajiyar zuciya ya sauke yana jin zuciyarshi sakwat kamar an rabashi da wani mai nauyi aka, tabbas ya yarda zee ce farincikinshi kuma idan yana tareda ita zaiji dadi da sallamar zuciya da ruhi.



Ajiyar zuciya itama zee tayi sai takoma jikin kujerar motar ta lafe tana murmushi, murmushin dayaqi barin fuskarta tun jiya


Wani irin dadi takeji marar musaltawa, she can't believe yau ita Deen ke furtawa kalaman soyayya, she can't believe yanzu Deen natane

Dama kenan shima yana sonta tuntuni shine baya gwadawa kwata2? Kai amma ya gama daita, duk wannan sleepless nights din da damuwa ashe wanda takeyi don shi shima tana can a ranshi? Dakau tasan da Hakan da ba zata ta6a damun kanta ba irin haka, amma nevertheless yanzu ma alhamdullilah, ta godewa allah daya kawomata abin da sauqi, dama wannan itace babbar matsalar wato kaso aqi sonka amma muddin soyayyar ta kowacce bangare ce to duk abinda zai biyo baya mai sauqi ne.


Ahankali ta dago hannunta tana kallo

_*yanzu nagane dalilin space dake tsakanin yatsu na da naki*_


_*anyisu ne don yatsunmu su maye gurbinsu, kamar haka*_

Murmushi tayi tareda runtse hannun ta lumshe idanunta cikin jindadi




A bangaren Deen ma bata dade da tafiya ba shima yafito feeling himself on top of the world

Be dade ba yasamu abin hawa suma suka shilla



Koda ya dawo gida kaka tayi mammaki sosai ganin yadda kai kawo cikin nishadi, murmushi yaqi barin fuskarshi sa6anin dasafe daya fita kamar yayi kuka yana komai sumi sumi

Koda ta tambayeshi lfy? Ko tsintuwa yayi? Sai yakama Dariya kawai yana cewa eh tsintuwa yayi, a zuciyarshi kuma yace *Tsintuwar soyayya ba*



Haka wadannan bayin allahn suka qarasa Wunin su cikin nishadi da annushuwa kowanne Saida aka ganemashi a gida don fara'ar yau ta dabance




πŸ’– πŸ’– πŸ’– πŸ’– πŸ’– πŸ’– πŸ’– πŸ’–



"wow! Wow!! Wow!! Dole na kwaso shokiiiπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ" inji saqon Feenah via whatsapp


Dariya zee tayi afili sannan tayi typing
"kai Aunty, yaushe kika zama motar yansanda?πŸ˜†"


"har tarakta ma ina iya zama, wayyo dadi πŸ’ƒ amma na tayaki murna πŸ₯°"


Murmushi zee tayi sannan tace

"thanks Aunty 😍"

"shikenan kuka yaqare ko 😏"


"dama wani ke kuka 🀨"


"qaniyarki, shegiya kin manta lokacin da kike kuka hawaye da majina kina wlh Aunty idan be soni ba mutuwa zanyi😩 yar rainin hankali kawai πŸ˜’"


"😳kai Aunty yaushe akayi haka? Wlh adai dinga tsoron allah 😫"


"kyaji dashi... Yanzu shikenan harkin amince? Bawani jan aji ba komai?πŸ˜’"


"shi ajin wani kalan abinci ne


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login