Showing 231001 words to 234000 words out of 322641 words

Chapter 78 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6190

Ahmad yake, cikin qanqanin lokaci ya isa wajen

Fitowa yayi daga cikin elevator din ya wuce office dinshi Direct


Kwankwasawa biyu yayi aka bashi izinin Shigowa

Murda handle din yayi ya tura kofar yashiga

Dagowa Ahmad yayi daga laptop din gabanshi, Ganin Aymaan ne yasashi saurin tashi tsaye yana cewa

"omg! Tun dazu sai yanzu ka iso?" Sai kuma ya lura da yanayin Aymaan da shigarshi


"Are you ok? Meya samu kayan ka? And your face, ya naga duk bruises?"

Zama Aymaan yayi a opposite dinshi ya harde hannayenshi a qirji
"inajinka" yafada a taqaice

"meya sameka wai Aymaan?"

"idan bakada abin fada zan tafi" inji Aymaan yana eyeing dinshi

"A'a nikau keda abin fada, bari kagani" yafada shima yana zama har wani kyarma yakeyi Wurin zaman


"inada wani mugun surprise for you" yafada yana kallon Aymaan

"uhun?" inji Aymaan yana kallonshi

"bari na faro maka daga farko

Kaga valentine is approaching, kowa yanzu shirye shiryen abubbuwan da zaiyi ya burge masoyiyarshi yake, shine nima nafara tunanin me ya kamata nayi na burge *B-baby* na"


Tunda yafara magana Aymaan ke Binshi da wani matsiyacin kallon haushi

Be lura ba hakan yasashi cigaba da cewa
"saina fara tunanin me ya kamata nayi saina yanke shawarar hada sunana da nata inyi creating video dinsu insamu waqa mai dadi ta soyayya inyi amfani daita..."

"Are you crazy? Wannan ne banzan surprise din daka dameni nazo nagani?" inji Aymaan a fusace

"Kash! Matsalata dakai rashin haquri"

"gudawa ne ni" inji Aymaan a qule


"koma dai Menene kabari nakai aya mana, na yarda idan nakai aya babu abinda yayi making sense aciki kayimin dik abinda kaga dama"


Shiru Aymaan yayi be tanka ba hakan yasa ya cigaba da cewa

"Hakan yasa na yanke shawarar nemo mana waqa mai dadi wanda zata hau da love mood din kuma inason tazamo ta hausa mai ratsa zuciya

Shine na dauki laptop nahau website nafara browsing waqoqin hausa na soyayya masu tashe.


Nasamu guda goma duk na kunnasu nafara sauraronsu daya bayan daya harna saurari duka.

Acikinsu daya tafi kwanta min kuma tahau da abinda nakeson hada mana
Sunanta *kalmar so*


Saboda dadinta na saurareta yafi sau goma, sai daga baya naji inason ganin video din waqar sai nayi downloading din videon.

Bari ka gani" yafada yana sungumo laptop din ya zagayo wajen Aymaan dake kallonshi Tundazu cike da takaici

Jawo wata kujera yayi ya zauna kusada shi ya shiga lalubo waqar cikin sauri

Dan Tsaki Aymaan yaja ya kauda kai yana jin wama yasashi zuwa tun farko gashi yana qara mashi akan abinda yakeji a zuciyarshi

Kida yaji yafara tashi acikin laptop din alamun harya kunna sannan aka fara waqar


_kalmar so tana nufin abinda zuciya tasoo_


_amma anawa 6angaren rai ne da rayuwa_

_so ne lagwan mutane biyu inda shaquwa_

_mai kama dan Adam da aljan da deguwa_

_Domin mu gane so, sai mun qara nutsuwa_

_don dole dole so shike kaimu koguwa_


Juyowa Aymaan yayi ahankali don kallon videon don waqar ta shigeshi shima dukda he's not in the mood, amma waqar ta ta6ashi a zuciya


Wani wawan jada baya yayi da kujerar lokacin dayaci karo da abinda ke kan screen din laptop din

Tashi yayi tsaye yana kallon screen din idanu awaje kamar zasu fado

_so sam beda tausayiii_

_so sam beda tausayii_

_inyai ta6argaza amsar saita bada nayi_

_ba tsoro yake ba shima_

_sannan be gudun husuma_

_zai iya tada yan Adam duk tsaye don yanada girma_

Qara jada baya Aymaan yayi yana kallon fuskar kan screen din

Fuskar da be dade dagani ba yanzu

Fuskar da ya nannausa yan Mintuna dasuka wuce

Mutumin da dazu dazun nan aka 6an6areshi Dakyar daga jikinshi

_mussadiq?_

Girgiza kai yayi

Mussadiq bayajin hausa, ko zo na yankaka da hausa bayaji

_Deen?_

Kanshi ne yayi wani mugun sarawa har Saida yayi saurin dafewa

Kallon smiling face din mutumin dake cikin screen din yayi yana cigaba da waqar guitar a rataye a wuyanshi yana kadawa


Baki na rawa yace
_*"DEEN"*_✍️







alhamdullilah! πŸ’ƒπŸ’ƒ Anan zan dakatar da Deen mutafi hutun ramadan πŸ’ƒπŸ’ƒ inda zamu cigaba insha allah bayan sallah idan allah yakai ranmu


Masu Deen! Deen!! To Deen is back!!! Yadawo da wani salo mai ban mammaki, ya dawo muku da bazata kala kala, kudai ku biyoni zuwa bayan sallah muji yadda chakwakiyar zata kaya.

Qaqa qara qaqa! Ga Aymaan ga mussadiq, ga kuma Deen ya fado From nowhere. Yanzu wasan zai fara, ku kasance da Ashaaaaanty dinku Domin jin yadda xa'a qarqare chakwakiyar nan


Allah kabamu ikon yin ibadunmu lafiya, Allah kasadamu da alhairan wannan watan mai albarka (amin summa amin)

Ina mai neman gafarar duk wanda na 6atamawa da sani na ko bada sanina ba, nima na yafewa kowa.


Ma'asallam! Sai mun hadu bayan sallah 😘😘😘



Ummin fasihu πŸ§šπŸ»β€β™€οΈπŸ§šπŸ»β€β™€οΈπŸ§šπŸ»β€β™€οΈπŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:42 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEENπŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*














*071*






*THE MUSICIAN🎼*




*barkanmu da dawowa daga hutun azumi, fatan kowa yayi ibadunshi cikin qoshin lafiya, allah yasa dukkanin ibadunmu kar6a66u ne, yakuma maimaita mana🀲🏻*








Qara qurawa gayen kan laptop din idanu Aymaan yayi zuciyarshi na bugu sosai



Tabbas inhar wannan gayen ba mussadiq bane to tabbas DEEN ne



Tashi Ahmad yayi shima ya qaraso inda Aymaan ke tsaye haryanzu kamar statue



"kaima kaga abinda nagani ko?" inji ahmad



sai alokacin aymaan ya iya motsawa ta hanyar juyowa ya kalleshi saidai yakasa cewa komai don yawun bakinshi ma sun kafe gabadaya


dakyar ya kalato wasu bussasun yawu ya hadiye sannan yace
"who is this?"


Dan buda idanu ahmad yayi
"haryanzu tambaya kake?"


girgiza kai aymaan yafara
"karka cemin wannan shine...Deen"



"masu irin wannan fuskar biyu ne duk fadin duniyarnan
Mussadiq da Deen.
kenan wannan is either Mussadiq ko Deen, kuma ni dakai munsan wannan ba mussadiq bane"





"but.. this can't just be, how... I mean yaushe Deen yaxama mawaqi?" inji aymaan confused


"watanni biyar dasuka gabata" Ahmad yabashi amsa


cikin rashin fahimta aymaan yace
"wata biyar? ban ganeba"


Ajiyar zuciya Ahmad ya sauke sannan ya gwadamashi kujera yace
"mufara zama tukun"



Dan jimm aymaan yayi kamar bazai zauna din ba saikuma yaja kujerar ya zauna yana jin yadda zuciyarshi tayimashi jingim




shima Ahmad jan kujera yayi ya maidota kusadashi ya zauna ya dago ya kalli aymaan dake kallonshi shima


"nima nashiga rudani fiyeda yadda kashiga lokacin danayi tozali da wannan fuskar.

abun kamar al'mara, kallo daya nayimashi kwanyata ta burkuce, fuskar Sir Mussadiq sak nake gani a screen din saidai yaren dayake sam ba nashi bane, hakan yasa wani abu ya gifta kwalwata.

domin kore tantama ta sai na jawo laptop din hannu na rawa nashiga searching din sunanshi and this appear..."


sake jawo laptop din Ahmad yayi ya juyota gabanshi yashiga danne2, shidai aymaan kallonshi Kawai yakeyi bece komaiba har yagama ya sake juyomashi laptop din gabanshi


janye idanunshi aymaan yayi daga kanshi yamaida kan laptop din.



kafe sunan dake qasan hoton mai fuskar Mussadiq din yayi nawasu daqiqu sannan ahankali ya bude baki yace" *BALARABE?*"


"yes, balarabe. wannan sunan yasameshi ne a wajen abokanshi da fans dinshi wanda hakan yayi sanaddiyar 6acewar ainahin sunanshi, don dayawa basusan real name dinshi ba, sunfi saninshi da wannan sabon sunan wato *BALARABE*.

Bari kaga full name dinshi..."
yafada yana scrolling laptop din


*KAMALDEEN MUHAMMAD a.k.a BALARABE*


Abinda ya bayyana kenan a screen din


kafe sunan aymaan yayi da idanunshi babu ko kyaftawa


cigaba da scrolling Ahmad yayi yana karanto mashi content din kamar haka


"KAMALDEEN MUHAMMAD,also known as BALARABE shahararren mawaqi ne mai zamani wanda yayi fice a fagen waqoqin nanaye wanda duk suka ta'alaqa ne akan soyayya.


BALARABE yayi fice kuma yayi suna a wannan harkar cikin dan qanqanin lokaci da baigaza wattani biyar ba, abinda ba'a ta6a samu ba a record din wani mawaqi ba.


Abin mammakin bewuce yadda wannan mawaqin yasamu kar6uwa tun awaqarshi tafarko mai taken *KECE* Waqar datayi nasarar bayyanashi ga duniya inda har takaishi ga matsayin dayake ayanzu.


BALARABE yasamu nasarar xama fittace ba iya Arewa ko Nigeria kadai ba hatta wasu qasashen na qetare sunsan da zamanshi


A kuma binciken da akayi BALARABE yana daya daga cikin sannanun Celebrities na Arewa inda yakeda tarin mabiya a shafukanshi na sada zumunta.."


Dan dakatawa Ahmad yayi daga karatun dayakeyi yawaigo yakalli aymaan dake bin karatun shima tundazu.


"Bari kaga nashiga shafinshi na Instagram"


shiga yayi din sannan yaqara karkato da fuskar laptop din gun aymaan wanda haryanzu besake furta komaiba


Gasping Ahmad yayi
"kalla.. over 4million followers! OMG! wlh mutuminnan is famous.. ji pics dinshi... see likes.. kalli millions of comments! cewa akayi idan yayi posting abu koda ordinary picture dinshi ne baya samun likes qasa da million


kalli shows dinshi, duk jiya nayi downloading dinsu..."

Kunna mashi daya daga cikin videos din shows din yayi


Deen ne tsaye cikin wasu tsaddadun fararen qanannun kaya, wuyanshi rataye da guitar yana kadawa ahankali


Abinda zaifi daukar hankalinka a wajen shine tarin mutanen wajen, yadda kasan tururuwa sai ihu suke da whistling yayinda shikuma ke rero waqarshi cikin cool voice dinshi cikeda nutsuwa


kafeshi da idanu Aymaan yayi yana kallon kamillaliyar fuskarnan tashi ma'abociyar fara'a, dakuma yadda dimple dinshi ke lo6awa gwanin sha'awa


waqa yake cikeda qwarewa yayinda sautin waqar ba iya kunne take shiga ba direct cikin zuciya take wucewa tana wanzar da shauqi acikinta.


lumshe idanu Aymaan yayi ahankali yana sauke numfashi ahankali


Ganin hakan yasa Ahmad dannama vidiyon pause ya kalleshi

"ya kagani? Deen is Back!" yafada cikin jindadi



bude idanunshi Aymaan yayi ahankali ya kalleshi

"And what's good about that?" inji Aymaan yana mashi wani kallo


Dan wara idanu Ahmad yayi
"kamar yaya what's good about that? watanni nawa muna nemanshi? yanzu mun sameshi kana fadin haka?"



Maida kanshi aymaan yayi ya jinginar da kujera yasake maida idanu ya lumshe sannan ya bude

"eh, haka nace. what's good about ganinshi? dubi fuskarshi, yayi kama da mai wata damuwa? nace yayi kama da mai wata damuwa!" ya qarashe maganar a fusace


"haba aymaan..."


"yayinda ya jefa wata a tasku, yayi sanaddiyar qauracewar farinciki a rayuwarta, shi yanacan cikin jindadi da walwala yana cin duniyarshi da tsinke! how cruel?" ya katse Ahmad cikin zafin rai


"Aymaan, karka yanke hukunci akan abinda baka.."


"karna yanke hukunci akan abinda ban sani ba? gayamin meye ban sani ba.
akan wannan mutumin rayuwar mutane da dama suka dagule ciki harda tawa!
ya yaudari diyar mutane wanda tasoshi da dukkan zuciyarta ta kuma kafe kai da fata akan sai shi batareda tayi la'akari cewa shi ba kowa bane! taso bijirewa mahaifinta duk don shi! qarshe me yayi? bad'a mata qasa yayi a idanu ya tafi ya barta lokacin datafi buqatarshi

hakan dayayi ya chanza komai a zuciyarta? ya ta6a soyayyar datake mashi? A'a saima qara haukacewa datayi akanshi inda ta dauki dukkan lamuranshi tayi uwa maqar6iya inda kullum da tunanin yadda zata inganta rayuwarshi take kwana take tashi, batada buri sai ganin rayuwarshi ta dawo daidai kamar ta kowa, ta sadaukar da abubbuwa da dama kuma tana kan sadaukarwa duk saboda shi, duk saboda wannan butulun da yanzu nasan ko sunanta baya iya tunawa"
yadda yake maganar Kawai ta isa kagane ranshi a matuqar 6ace yake don har jijiyoyin wuyanshi tashi sukeyi don masifa, he can't believe mutumin dasuke hauka akanshi yana can hankalinshi kwance bayada wata damuwa





"haba Aymaan, meyasa zaka yanke hukunci akan abinda bakada tabbaci akai? dama ana judging book by it's cover ne? don kaga mutum yafito daidai hakan na nufin har cikinshi daidai yake? yayinda wasu murmushi kezama ado agaresu wasu malullu6i ne, mallulu6i na lullu6e ainahin halin dasuke aciki.

Zainab was heartbroken and always in pain, hakan ya hanata murmushi ko dariya ko wasu harkokin na gabanta?

wasu suna fara'a ne domin 6oye ainahin halin dasuke aciki, wasu suna murmushi ne don sunga kowa nayi bawai don hakan na zuwa daga can qasan zuciya ba.

yadda zee ke kwana tana tashi dashi arai shima hakan take a wajenshi

Zainab na maqale a zuciyar Deen kuma zan gwadamaka hujja"


Yana kaiwa nan yasake jawo laptop din yayi yan danne2nshi sannan ya juyoma Aymaan yana cewa
"wannan wata firace da akayi dashi a gidan wani television ko wata daya ba'ayi ba"


danna play botton yayi wanda hakan yaba vidiyon damar farawa



Deen ne zaune kan kujera yana facing presenter din gidan t.v din

sanye yake cikin wata dakkakiyar sky blue shadda wacce tayi mugun hawanshi takuma qara fiddo mashi qwarjininshi da haiba

kanshi babu hula sai lallausan gashinshi dayayi trimming dake kwance luff luff gwanin sha'awa

yaqara haske da kyau ga cute lips dinshi dasukaqara yin pink fiyeda da


kallon presenter din yakeyi dake yimashi tambaya fuskarshi asake

"Mallam balarabe zaka iya gabatar ma masu saurare kanka?"


murmushi Deen yadanyi sannan yace
"insha allah, sunana KAMALDEEN MUHAMMAD amma anfi sanina da BALARABE yayinda wasu kuma ke kirana Deen"


"masha allah, Mallam balarabe zamuso sanin yadda akayi kasamu wannan sunan na BALARABE, koko dama kai balaraben ne Don ana yada jita jitan qila ka hada jini da larabawa duba da yadda kayo ruwansu"


murmushi Deen yayi
"ban hada komai da larabawa ba kamar yadda ake hassashe, ni cikkaken bahaushe ne, sunan BALARABE kuma na sameshi ne awajen abokai na, nickname ne Kuma sai yabini" yafada cikin cool voice dinshi


"masha allah, to Mallam balarabe meye yaja ra'ayinka har kafara wannan harka ta waqa?" inji presenter din


"eh to, dafarko nafara waqa ne ba don nasan inada talent din ba, Kawai ina yine don yaxama Abin debemin kewa duk lokacin da nakejina so boring, sai daga baya aka fahimtar dani talent dina akan waqa sannan aka kwadaitamin bayyana wannan talent din nawa ta hanyar shiga harkar waqar"

"masha allah, yanzu tun lokacin daka fara waqa zuwa yanzu aqalla kayi guda nawa? kana iya qayyadesu"

dan murmushi deen yayi
"waqoqin danayi kuma suka fito adadinsu 27 yayinda akwai wadanda nake aiki akai kuma suna gab da fitowa suma insha allah"


"to masha allah, mallam balarabe zaka iya fadamana nasarorin daka samu sanaddiyar waqa?"


"Alhamdullilah, babu abinda zance a wannan ga6ar sai godiya ga Allah (s.w.t) don nasarori kam na samesu sosai a wannan harkar ta waqa, ciki harda famousity, a sanaddiyar waqa sunana ya zaga wuraren da qila har inmutu bazanje wajen ba, takuma sa ansan dani Kuma nima nasan mutanen da ban ta6a mafarkin zan sansu su sanni ba
bayan hakan kuma tazama garkuwa gareni inda take a.matsayin sana'a agareni wanda nake samun rufin asiri sosai acikinta, Alhamdullilah"


"to Mallam balarabe qalubale fa? kasan duk nasara tana tareda qalubale, wadanne irin qalubale ka fuskanta a wannan harkar ta waqa?"


kada kai Deen yayi
"gaskiya ne, kowanne nasara yana tattare da qalubale.
gaskiya qalubalen dana fuskanta bawata mai yawa bace, a lokacin da nayanke shawarar fara waqa nakuma tuntu6i kakata akan hakan taso hanani don a ganinta babu Abinda yake cikin harkar sai tarin shiririta da shirme amma da taimakon uban gidana muka samu muka shawo kanta har ta amince takuma sanyamana albarka akai wanda inada tabbaci albarkar ke bibbiyarmu haryanzu" ya qarashe murmushi a fuskarshi


shima presenter din murmushi yayi
"ka ambaci ubangida, zaka iya fadamana waye ubangidanka ko jagoranka wato role model dinka a wannan harkar?"


jimm Deen yadanyi saikuma yadanyi slight murmushi

"eh... inada role models biyu... da wanda da taimakonshi nashiga wannan harkar sai wadda tasani nayi realising talent dina.."

saikuma yayi shiru staring in space


Ganin hakan yasa presenter dan muskutawa sannan yace
"wacce tasaka realizing talent dinka? wacece?"


nanma shiru yadanyi still staring blankly at space saikuma yayi wani guntun murmushi yana sauke idanunshi qasa

Ahankali yaqara dagowa ya kalli presenter din still murmushin bebar fuskarshi ba

"wata ce... wata" yafada ahankali yana kallon fuskar presenter din saidai a zahiri ba fuskarshi yake gani ba,.wata fuskar yake gani daban


"Idan aka ambaci kalmar *waqa*.. ita ke fara zuwa raina. Idan nashiga studio da niyyar yin waqa inajin presence dinta ajikina, dana lumshe idanu na don nafara ita nake gani tana min rad'ar waqar daxanyi nikuma nashiga binta ahankali.

itace dalilin komai na career dina, itace dalilin nasarata a duniya, itace dalilin zuwana matsayin danake aciki yanzu, itace nasarata.


*waqa tana zuwa ne daga zuciya, duk waqar datazo directly daga zuciya zakaga tafi wadda za'a zauna a tsara*
wannan kallaman nata sune sukeyin guiding dina a kodayaushe"

"dafarko na dauki hakan kamar abu marar yiwuwa yayinda nasha qoqarin qirqirarta da abinda yake a zuciyata amma daga baya sai nayi realizing gaskiyar maganarta lokacin da nake rero abinda ke zuciyata batareda sanina ba.


Duk waqar dazanyi tana zuwa ne daga can qasan zuciyata kuma kowacce is reffering to her..."

dan murmushi yasake yi absentmindedly sannan in a whisper yace
"my role model"


shiru ya ratsa wajen na wasu daqiqu, can presenter din yace
"to Mallam balarabe, zaka iya fadamana ko wacece wannan role model din taka? dakuma matsayinta a wajen ka"


Nan ma saida yadanyi shiru sannan yadanyi guntun murmushi

"she's an angel, angel of light and beauty, duk inda ta gifta tana barin walwalin haskenta awajen, hasken daxai cigaba da haskaka wadanda tabari awajen.

she's innocent, straightforward, mean, honest, stylish and fun to be with.

tanada baiwar da duk inda taje komin qanqantar zamanta awajen sai tabar memories, sweet brainsticking memories"

presenter din dake enjoying moment din cikin doqi yace
"wacece agareka? girlfriend?"


dagowa Deen yayi yakalleshi na wani lokaci wanda expression din fuskarshi yasa murnar presenter din fara komawa ciki

sauke idanunshi yayi a qasa sannan ya girgiza kai

"A'a..." sai kuma yayi shiru

can kuma ya dago yaqara kallon presenter din
"Actually.. a halin yanzu kowanne na rayuwa ne a wata duniyar tashi daban... and... mun haramta ga juna.. ta haramta gareni"
sauke kanshi yaqara yi qasa yana lumshe oily eyes dinshi

shiru wajen ya dauka, shi kanshi presenter din jikinshi yayi sanyi

be daddara ba yasake cewa
"ta haramta agareka kamar yaya?"


Ajiyar zuciya Deen ya sauke sannan ya dago yakalli presenter din yana murmushin qarfin hali

"I'll be glad Idan mukayi dropping wannan topic din, it's something personal, I dont want to discuss it" yafada politely


jin hakan yasa shima,presenter din dropping topic,din ya cigaba da yimashi wasu tambayoyin daban.




Ajiyar zuciya Aymaan ya sauke ya maida kanshi ya jinginar da kujera tareda lumshe Hazel eyes dinshi


jiyake kamar kanshi zai rabe gida biyu ga wani abu dake tasomashi a qasan zuciya mai dacin gaske


shima Ahmad bece komaiba sai kallonshi dayake yana jiran jin me zaice kuma


Jan kujerar dayake akai Aymaan yayi baya sannan ya miqe tsaye

binshi dakallo Ahmad yayi ga mammakinshi sai gani yayi ya juya ya nufi kofa


sakin baki Ahmad yayi yana kallonshi har yakai bakin kofa sannan cikin qarfin hali ya kira sunanshi

dakatawa Aymaan yayi daidai lokacin daya kai hannu kan handle batareda ya juyoba


tashi tsaye Ahmad yayi
"ya zaka tafi just like that?"


batareda ya juyo ba yace
"what again? akwai wani abu bayan wannan ne?"


qara wara idanu ahmad yayi cikin mammaki
"bangane ba, aren't we suppose to discuss about this?"


sai a sannan Aymaan yajuyo

"discuss about what? there is nothing to discuss about"

"amma..."


"baka jishi ba? he said sun haramta da juna, ni wanene dazan halarta haram?" Aymaan ya katseshi da hakan


kasa cewa komai Ahmad yayi sai bin Aymaan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login