Showing 225001 words to 228000 words out of 322641 words

Chapter 76 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6133

dimple dinshi

"kinga, am here for something different gashi kina samu muna wata maganar daban, you're wasting my precious time"


Kasa magana tayi saboda haushi, wai ita kema 6atamashi lokaci


"nasan shi ya fiddaki a school din saboda wani banzan dalilinshi na kareki, abinda besaniba shine am limitless, ina keta duk inda naga dama a lokacin da naga dama, the guy is so full of himself bayan babu abinda yasani sai hauka, maybe shiyasa tun farkon haduwata dashi naji beyimin ba, it's better ki bashi shawara tunda kunfi kusa akan yasan dawa dawa zaija da don sahun giwa ya take na raqumi, yayi kadan yaja dani, daga mashi kafa nake and I don’t think zan cigaba da daga mashi Ita"

Dakatawa yayi yaji ko xatace wani abu saiyaga batada niyyar cewa komai don bama shi take kallo ba

Hakan yasashi cigaba
"secondly, maganar dakika fadamin ranar a office is still stocked in my brain, bansan ma'anarta ba Amma I bet you zan sani, zan gano Saidai ina baki shawarar don’t try to play cunny plays with me don am a turtle itself, slow but cunny. Kifita daga harkata for your own Good"

Qara Dakatawa yayi yaji me zatace Saidai still tayi mashi shiru Hakan yasa yasan maidashi fool tayi wanda dama best answer dinshi shine shiru, Saidai Hakan be dameshi ba tunda dai taji duk abinda yace kuma dama ba wadannan magangganun kadai suka kawoshi ba harda wani dalili nashi daban so be damu ba.


Tashi yayi tsaye yana maida shade din hannunshi a idanu

"fatan kin fahimci dukkan magangganuna kuma zakiyi amfani dasu.. For your own Good... Have a wonderful day" Yana kaiwa nan ya juya yabar lab din in his usual majestical steps



Ajiyar zuciya zee ta sauke, lallai mutumin nan ya cika dan rainin hankali, ita duk acikin magangganunshi babu wanda tayi mata ma'ana

"mtcheew, aikin banza kawai" tafada tana miqewa tsaye itama ta fita daga lab din




Daga ranar kuma bata sake ganin ko mai kama dashi ba a school din.


Everything keep going smoothly har kwatsam watarana ta tashi da text din Aysha a wayarta


*_Am sick, ki tayani da addu'a, I don’t know if I can survive it_*


Sosai hankalin zee ya tashi lokacin dataga text din.

Sukan kwana biyu yanzu basuyi waya ba don sun rage waya ba kamar da ba kuma zee na kyautata zaton har lokacin fushi take saboda tabar Annur don tun a lokacin tadan ja baya kadan da ita, suna yin waya amma not very often kamar da


Babu 6ata lokaci ta kira number tata Saidai bata shiga Hakan yasa hankalinta qara tashi


Koda tagayama batool saita bata shawarar su gwadawa ummie suji ya zatace


Koda suka gwadawa ummie itama ummie ta nuna damuwar ta akai sosai sai tace ya kamata suje su dubota

Jin Hakan yasa zee qwalalo idanu

Da farko taso qin yarda amma sai Ummu batool ta nunamata muhinmmancin yin Hakan kuma bayan Hakan Aysha nada kirki sosai ta yaba da hankalinta kuma tunda har ta iya yimata text tana a halin ciwo be kamata tayi watsi daita ba

Da Hakan zee ta yarda da zuwan amma deep down a tsorace take, babu wanda take fargabar haduwa daita kamar ummie don ko muryarta taji ta waya sai tajita wani iri bare ace taganta a zahiri.


Ahakan suka yanke shawarar gobe insha allah zasuje don dama zee tasan address dinsu don Aysha ta dade da bata complimentary card dinta.


Washegari daya kama saturday suka shirya wajajen bayan la'asar suka fita suka hau cab don motar batool tasamu matsala tana wajen gyara ga Aymaan tunda safe yafita don kwanan nan he's always busy.



Cab suka tsaida suna fadamashi unguwar dazasu yace su shigo don unguwar sannaniyar unguwa ce a garin.

Shiga sukayi sannan yaja motar suka shilla





Tunda suka shigo unguwar suke kalle kalle ta window, unguwar is so silent ga street din very smooth ga gidaje masu shegen kyau sunata wucewa

Ahaka har sukaji Motarsu ta tsaya

Kallon kofar tangamemen gidan dasuka tsaya sukayi sannan suka kalli juna

Batool ce tafara bude murfin kofar tafita sannan itama zee ta fito

Tsayawa sukayi kallon kofar gidan cikin shagaltuwa

Saida mai cab yayi masu horn sannan suka tuna basu sallameshi ba

Zee ce ta zuge jakkarta ta sallameshi sannan ta dawo wajen batool suna cigaba da kallon tangamemen gate din gidan

Su tunaninsu ma ta ina zasu fara bubbuga gate din


Qarasawa sukayi bakin qaramar kofar dake maqale da gate din batool tashiga kwankwasawa


Basu dade suna kwankwasawa ba aka bude wani dan taga dake daga saman qaramar kofar gate din ana leqosu

"yes? Kusu wanene?" inji mai leqen

Kasancewar da larabci yayi magana batool ce ta amsa

"mu qawayen Aysha ce, munzo ganinta fatan nan ne gidansu"


Shiru yayi yana kallonsu, can yace

"bari nakira na sanar, suwaye za'ace?"

"kace da Zainab da batool ne"

Be sake amsawa ba ya maida Wurin ya rufe

Kallon juna sukayi

"kaji manya" inji batool tana chuckling

Dan ta6e baki zee tayi batace komai ba


Suna ahaka sukaji alamun za'a bude kofar Hakan yasa suka maida hankali kanta


Kofar gabadaya aka bude yanzu mutumin dazu yasake bayyana

"bismillah, kushigo ciki"

Batool ce tayi gaba zee na biye daita suka shiga gidan

Dan Wara idanu sukayi ganin tafkeken qayattacen gidan dasuka tsinci kansu aciki

"muje" inji wani daban mai irin shigar wanda ya bude masu gate

Binshi sukayi abaya suna taka shinfidaddiyar kwalta din wajen suna bin silent street din wajen da kallo da yadda aka qawata koina da furrani.


Sun danyi tafiya sannan suka qarasa main entrance din


Door bell mutumin daya rakosu ya danna, can bayan some seconds aka bude kofar wata maid ta bayyana

Sannu da zuwa tayimasu sannan ta kauce tayimasu iso ciki


Yanzu ma batool ce tafara shiga zee na bayanta gabanta banda faduwa babu abinda yakeyi.


Wow! Kowanne yayi gasping a zuciyarshi ganin irin haduwa da tsaruwar da falon yayi.

Fadar irin qayatuwar da falon yayi 6ata baki ne Saidai mai karatu ya hasaso ma kanshi


Iso maid din tayimasu tana wucewa Wurin stairs

Cigaba da binta sukayi suna yi suna yan kalle kalle a falon


Hawan stairs din suka shiga yi wanda shima kanshi abin kallo ne suka cigaba da bin maid din har suka isa sama


Wani falon suka sake iskewa sama wanda tsakaninshi dana qasa sun rasa wane yafi kyau, abu daya kawai suka sani, wancan na qasan yafi girma.


Cikin girmamawa maid din ta nuna masu wajen zama duk suka yima kansu matsugguni a kan dakkakun kujerun falon


Kan kace me? Har anfara cika masu gabansu da kayan motsa baki sannan aka tafi aka barsu bayan angayamasu suyi making kansu comfortable


Kasa ta6a ko daya daga cikin abubbuwan da aka ajiyemusu agaba sukayi sai kalle kallen dasuka cigaba dayi suna jinjina dukiyar da aka narkar wajen qera wannan qerarren gidan


Ahaka sukaji sallamar ummie cikin cool muryarta, muryar data sanya gaban zee faduwa


Amsawa duk sukayi suna Dagowa.

Gaban zee yasake yankewa ya fadi

Wasu irin emotions ne suka shiga building up a zuciyarta still idanunta akan matar da take Deen sak ajikinta


Harta qaraso ta zauna idanunta na kanta

Gani tayi tana magana fuskarta dauke da murmushi amma batasan me tace ba, hankalinta yayi nisa

Mintsinin da batool tayimata ya maido ta daga duniyar kallon ummie data tafi

Sai a lokacin taga ashe batool ta zamo qasa tana gaidata Hakan yasa itama zamowa qasa tana gaidata cikin rawar murya

Amsawa ummie tayi tana cewa su tashi su koma kan kujera amma sukaqi

Zee najin batool na Tambayarta ya jikin Aysha itakuma tana amsa mata da sauki sosai tana ma daki

Duk maganar dasukeyi zee kanta na qasa tana battling da hawayen dake son kwacemata

"wacece takwarata acikin ku?" inji ummie cikin fara'a

Batool ta nuna zee cikin murmushi

"Zainab.."

Dagowa zee tayi ahankali tasake kallonta

Miqomata hannu ummie tayi alamun tazo

Kamar wanda aka ingiza sai gani tayi ta rarrafa wajenta da sauri ta riqe hannun nata ta damqesu ta dora fuskarta akai hawayen datake riqewa suka 6allemata


Sosai Hakan yaba ummie mammaki don harda sheshekarta

To meya sata kuka? Ko tunani take jikin Aysha yayi tsanani? Tambayar da ummie tayiwa kanta kenan

Hakan yasata dago fuskarta tana share mata hawayenta fuskarta dauke da murmushi

"karki damu diyata, ai Ayshar ma jikin yayi sauqi, kibar kuka"

Wasu sabbin hawayen suka sake gangaromata

Wannan wane marar imani ne? Wane mai qonnaniyar zuciya ne ya raba uwa da danta na tsayin shekaru batareda kowannensu yasan da wanzuwar dayan ba? Wane marar imani yayi Hakan?


Jitayi ta tadota tsaye tana cewa sutaho takaisu su ganta don ita harga allah tayi tunanin ciwon Aysha din takema kuka


Tare suka jera suka tafi har suka isa bakin kofar dakin Aysha

Kwankwasawa ummie tayi sannan ta Murda handle din kofar tashiga hannunta jaye dana Zainab


A zaune Aysha take kofin shayi a hannunta da alamu shi take sha, ga hannun daure da cannular da alamun Saida akayi mata qarin wani abu ajikinta


Sosai Aysha ta wara idanu ganin su zee don bata ta6a zaton zatazo ba

Da sauri ta ajiye cup din hannunta ta Wara mata hannu zee tayi sauri ta qaraso itama suka rungume juna cikin shauqi suna Fashewa da kuka atare, kowanne da ma'anar kukan shi

Zee kukan da bata ida ba na dazu ne itakuma Aysha nata na daban ne.

"Ummie, na rabu dashi... Narabu da Umar.. Finally na rabu dashi" inji Aysha cikin kuka

Jin Hakan yasa zee Saurin dagota tana kallonta da mammaki

"kin rabu dashi?" inji zee cikin mammaki

Kada kai Aysha tayi hawaye nasake gangaromata

"eh, nima na gano Gaskiya ummie, Umar baya sona, Finally zuciyata ta yarda da Hakan. Ni kadai nake hauka na, Finally na gane Gaskiyar dakike son ganar dani, and I decided to let him go, Narabu dashi har abada Koda Hakan na nufin rasa rayuwata"

"bazaki rasa rayuwarki ba Aysha, ba akan wannan mutumin ba.. Don be cancanci Hakan ba, be cancanci Koda digon hawayenki ba, insha allah zakiyi farinciki without him, you'll move on zaki samu wanda nan gaba zaki waiwaya rayuwarki tabaya dashi kiyi murmushi kice gwamma da akayi"


Sake rungumeta Aysha tayi gam tanajin sauqin abinda takeji a zuciyarta a sanadin magangganun zee.


Murmushi ummie tayi sannan tajuya tabar dakin tana qara jin qaunar Zainab har cikin zuciyarta

Batool ce ta qaraso wajensu itama ta zauna ta kamo hannun Aysha Hakan yasa ta dago ta kalleta

"kiyi hqr Aysha, wani abin muna sonshi ne amma ba alhairi bane a garemu, wanda allah ya taqaitama wahala sune suke gane Hakan da wuri, Kiyi hqr kiyita addu'ar allah yasa Hakan shiyafi alhairi kuma ya za6a miki Mafi alhairi"


Haka sukaita bata shawarwaru da kwantar mata da hankali

Sai gashi taji sauqin zuciyarta sosai sanadin qarfin gwiwar dasukayita bata

Sai gashi daga baya ummie tashigo ta iske suna fira cikin nishadi Aysha harda Dariya

Sosai abin yabata mammaki, yarinyar da yau kwana uku kenan ko magana batayi sai hawaye

Dadi sosai ummie taji tafita tasa aka aika musu da abinci

Tare suka ci suna fira wanda Hakan ba qaramin taimaka ma Aysha yayi wajen rage nauyin zuciyarta.


Ganin magrib takusa yasa suka fara haramar tafiya

Duk yadda Aysha taso qara tsaidasu qiyawa sukayi don Saida ummie dama ta bige musu warning kan karsuyi dare.


Tare suka fito da Aysha falon saman suna tafe suna Dariyar firarsu

Qamshin turaren da zee taji yasata dagowa ta kallo falon idanunshi suka gauraya


Zaune yake gaban ummie aqasa yana dan mammatsa mata qafa

Saurin Janye idanunta tayi akanshi suna ida Qarasowa falon

Ganinsu yasa ummie fara washe baki

"tafiya zakuyi tun yanzu?" inji ummie

"wlh kau ummie, ance karmuyi dare ne" inji batool

"Gaskiya kam, Hakan yayi sosai ai mun gode qwarai, zuwanku ya samar da abinda kwana uku kenan muketa fama bamu samu ba, Allah yasaka da alhairi, allah yayimaku albarka"

Cikin jindadin addu'arta suka shiga amsawa da amin

Kallon mussadiq da kanshi ke qasa haryanzu yana cigaba da tausa kafarta ummie tayi tace
"kaga qawayen Aysha ko? Suna zuwa ta warware"


Dagowa yayi yaimasu kallon seconds 2 yace
"oh? Mungode"


"takwara wannan shine yayan Aysha, mussadiq"

Murmushi zee tayi sannan ta dan kalleshi
"Good evening" tafada tana dauke kai

"evening" ya amsa a taqaice batareda ya kalleta ba

"Good evening yaya" inji batool

Dagowa yayi ya kalleta sannan itama ya amsa a taqaice ya cigaba da abinda yakeyi


"bunnaya, ka tashi hakanan kaje ka saukesu gida kaga dare yafara" inji ummie

Atare duk suka kallo ummie cikin dan Wara idanu

"na kaisu? Basuzo da mota ba?"

"bazuso daita ba, ko?" ta maida akalar Tambayar kan zee

"eh.. Amma ai zamu samu cab, babu damuwa" tafada hoping bazata matsa masu yakaisu din ba, she dont want to have any thing to do with him again


"samun abin hawa anan unguwar ba qaramin wahala bane don basu cika Shigowa ba kuma idan kukace sai kunfita daga unguwar dare zakuyi, kubari yakaiku kawai, ai dama shima fita zaiyi yanzu"

"ummie.. Driver yakaisu mana. Ni inada urgent meeting dazanyi yanzu"

"nasan da Drivern nace ka kaisu ai, idan baxaka kaisu ba kafito ka fadamin sai nasan abunyi"

Sunkuyar da kanshi yayi don yasan haushi taji sai yace
"to ummie"

Dan hararar shi tayi sannan ta maida kallonta kan su zee tana cewa
"yauwa 'yayana kubari yakaiku kunji? Ina zuwa"

Daga haka ta tashi ta nufi dakinta

Shima tashi mussadiq yayi bayan wucewarta yanufi hanyar fita yana cewa
"Don't waste my time"


Binshi da kallo sukayi sannan batool da zee suka kalli juna sai zee taga kumshe Dariya ma take Hakan yaqara quleta saita dauke kai cikeda haushi

Ummie ce tasake fitowa riqeda yar shopping bag a hannunta tabasu

Dakyar tasasu amsa suna mata Godiya sannan suka rakosu har qasa har inda mussadiq ke jiransu cikin mota

Batool ce tayi saurin wucewa ta bude back seat tashiga leaving zee da only option din Shiga front seat

Badon taso ba ta bude kofar gaban ahankali tashiga itama

Daga masu hannu ummie da Aysha suka shiga yi suna masu fatan tsari suma suna maida masu martani ta hanyar daga musu hannu

Saida ummie taja mashi kunne akan gudu a titi sannan yaja motar suka bar gidan.



Tunda suka hau kwalta babu mai cewa komai sai motar tayi tsitt kamar babu mutane ciki

Dukda ummie tayi mashi gargadin gudu da mota Saida yayi dukda shi nan ba gudu yake ba Sosai, Saidai su zee a tsorace suke da speed din motar musanmman batool Saidai babu wanda yayi mashi magana allah allah kawai suke sukai gida ya saukesu

Abin mammaki sai gashi batareda sun mashi kwatance ba yabi dasu hanya tiryan tiryan har cikin unguwarsu kuma har kofar gidansu

Abin yabasu mammaki sosai don basu ta6a sanin yasan gidan ba.

Lokacin har duhu duhun magrib yafara

A kofar gidan yaja ya tsaya da motar daidai itama motar Aymaan tana danno kai opposite dinsu

Hango motar yasa gaban zee faduwa tayi saurin fara qoqarin bude kofar Saidai tajita gamm alamun a kulle take

Juyowa tayi ta kalli mussadiq a fusace daidai lokacin da Aymaan ya dallo hasken motarshi saitinsu


Saurin Juyawa tayi tana kallon Aymaan ta cikin motarshi wanda yayi mutuwar zaune yana kallonsu suma... ✍️






Ummin fasihu 🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:42 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?*










*070*








*RIVALRY*









Komai na Aymaan ne ya tsaya lokacin da idanunshi suka hango mashi su


Ahankali ya Runtse idanunshi yasake budesu hoping zaiga wani abin daban amma still sune.


Zainab da wannan marar mutuncin a mota, a qarqashin rufin mota daya.



Wani abu da besan ko Menene ba yazo ya tokare mashi qirji wanda Hakan yasa yaji numfashinshi na bashi wuya Wurin fizgowa.


A bangaren su zee ma mutuwar zaune both ita da batool dake baya sukayi suna kallonshi


Zuciyarta ce tashiga racing sosai ganin yadda ya kafesu da idanu babu ko kyaftawa fuskarshi expressionless


Saurin sake kai hannu tayi Wurin lock din tana qoqarin budewa Saidai still gamm yake Hakan yasa tajuyo akan mussadiq dayayi balancing a fusace

"mallam meye haka wai? Ka budewa mutane kofa"


Dan kallonta yayi sai yayi murmushi yace
"saboda me?"


"saboda zan fita, am suffocating" tafada tana dan satar kallon Aymaan hoping zai iya jiyo abinda suke cewa kar yayi musu wata fassarar


"motata ce, lock dinane ba yanzu naga damar budewa ba, ai bani nace ku liqemun akan dole saina kawoku ba"

"muma cemaka akayi don son ranmu muka biyoka? Saboda ummie ta fadi Hakan kawai yasa muka biyoka if not ko kallo kasan baka ishemu ba"


"then sai kuyi hqr dani kokuma better still ku 6alle murfin kofar kufita"

Hakan yaqara harzuqa zee Saidai kafin tasake magana taji alamun tashin mota Hakan yasa ta waiga taga motar Aymaan ne tazo tawuce gate tayi horn

Ba'a dade ba aka bude mashi kofa ya danna kan motar ciki yashige.


Maida idanun zee tayi ta lumshe cikin wani yanayi Yayinda shikuma mussadiq yadanyi murmushin gefen baki


Qarar cire lock taji wanda ke nufin ya bude kenan


"out" yafada yana hada rai

Jin sautin bude kofa sukaji abaya batool ta fita

"Are you deaf?" mussadiq yaqara fada

Sotake tajuyo ta gaggayamashi magangganu amma qululun daya tokaremata qirji ya hana Hakan yasa kawai tasa hannu ta bude murfin motar tafita tabar mashi ita abude tawuce


Binta da kallo yayi harta shige don batool dama tana sauka taqara gaba don itama ta tsorata da yanayin Aymaan


Bude kofar nashi side din yayi shima yafito daga motar riqeda ledar da ummie tabasu wanda 6acin rai yasa zee mance ta


Gate din gidan yanufa inda maigadi ke qoqarin rufe qaramar kofar gate din


Miqamashi ledar yayi mai gadin ya amsa fuskarshi dauke da alamun tambaya

"na yanmatan dasuka shigo ne" Yana gama fadin Hakan ya juya ya nufi motarshi yashige ya tadata yajanyeta yabar kofar gidan yana jin wani nishadi a zuciyarshi





Zee data kusan kaiwa kofar main entrance taji kamar maigadi na qwalamata kira Hakan yasa ta dakata daga tafiyarta tajuyo tana kallonshi harya qaraso

Ledar hannunshi ya miqo mata yana cewa gashi inji wanda ya saukesu

Kallon ledar tayi taga wanda ummie tabasu ne, kamar karta amsa taji amma sai kuma ta amsa tayimashi Godiya sannan ta juyo da niyyar tafiya


Wani irin bugawa zuciyarta tasakeyi lokacin da sukayi ido hudu da Aymaan dake


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login