Showing 273001 words to 276000 words out of 322641 words

Chapter 92 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6169

afusace

"su suka buqaci hakan"

"su wa?"

"Mussadiq"

"mtcheew, idan mukaje me xamuyi musu? ni wlh banason irin wannan tunda anyi mai wuyar ba shikenan ba?"

ta6e baki Ahmad yayi yace
"wannan Abbu ya kamata ka fadamawa mallam, saida yatafi sannan zakaita.tada jijiyoyin wuya, wannan ai ihu bayan hari ne"


wata uwar harara aymaan ya makamashi yakoma ya zauna cikeda takaici

dariya Ahmad yayi yace
"saika shirya don't keep us waiting" yana kaiwa nan yafice

tsaki aymaan yaja cikeda takaici, sosai yaji haushin binsu dazaiyi don shi yanzu haka shirin tafiya gida yake don ganin wane hali zee take don tun jiya take ranshi daita ya kwana gashi ankawo mashi kwafsi

shi bega dalilin binsu ba, is not as if basusan hanyar gida bane, kwata2 bega amfanin binsu ba.

haka yaita dacin rai shikadai a office din yanajin kamar yayi bindiga




acan ward dinsu Deen kuwa Deen keta kallon Mussadiq daketa waya yana bada order daban daban

azahiri kallon Mussadiq yake amma a badini hankalinshi ma ba akanshi yake ba, tunaninshi yayi nisa daga duniyar dasuke ciki

jiyayi anja hannunshi hakan yasashi dawowa daga duniyar tunanin daya lula yakalli mai kama mashi hannu yaga Aysha ce tana mashi wannan cool murmushin nata irin nashi

shima murmushin ya maida mata yana damqe hannunta itama sukayi interlocking yatsunsu

ko mintuna shabiyar basu qaraba ordern da Mussadiq yabada suka iso

sabbin qannanun kaya ne kala biyu iri daya

kala daya ya dauka yaba Deen daya don shima ya chanza don duk kayan jikinsu sunyi squeezing

cikin dan qanqanin lokaci suka chanza suka fito

sakin baki mutanen dakin sukayi lokacin dasukayi arba dasu biyun ganin yadda suka fito a ainahin identical twins din

komai nasu daya baka ta6a banbancewa, Abinda ma yasa yan dakin suka iya babancesu shine sumar kansu Inda na Mussadiq yafi na Deen yawa, baya ga wannan Babu wani banbanci.

cikin qanqanin lokaci suka gama shirinsu sukayi shirin tafiya bayan wani Dr ya rubuta masu sallama.

atare duk suka fito Inda saida Ahmad yayi excusing kanshi don zuwa tahowa da aymaan.

saida aymaan ya6atama Ahmad rai da shiririta kafin yafito suma suka nufi parking space din

wata shegiyar danqareriyar mota qirar Lamborghini suka gani awajen Inda ganin habeeb agabanta yasasu sanin aciki zasu

dafarko aymaan yaso qin binsu cikin motar yace zai biyo bayansu Acikin tashi amma daga baya ya haqura saboda yadda Ahmad yaita lalla6ashi

duk sunyi wannan abin ne kafin su qarasa wajen motar

koda suka isa exchanging pleasantries sukayi tsakanin juna babu yabo babu fallasa suka shishiga motar Inda ta kwashesu duka saboda girmanta

koda wasa aymaan be kalli gefen Mussadiq ba kamar yadda shima hakan take a 6angarenshi

saima dai Aysha da idanunsu ke yawan hadewa Inda da hakan yafaru kowa zaiyi saurin kawar dakai


haka sukayi wannan tafiyar in silent for fifteen minutes kafin su isa unguwarsu Mussadiq.


tun a farko farkon unguwar zaka fahimci kashigo unguwar manyan mutane sakamakon manya manyan gidajen dasuketa wutowa

ahaka har motar ta tsaya a bakin wani tangamemen gate

basuyi one minute da tsayuwa ba aka wangale musu qaton gate din motar ta danna kai ciki.

tafiya sosai sukayi yadda kasan ba gidan suka shigo ba sannan motar ta tsaya.

guards ne takoina suka rurrugo suka tsaya agaban motar

acikinsu wani yabude musu kofar duk suka dare suna basu hanya don saukowa

da daddaya suka fara saukowa daga motar har suka gama fitowa

sosai mammaki ya bayyana afuskokin guards din lokacin dasukayi arba da Mussadiq da Deen

sai kallonsu suke dasun kalli wannan saisu kalli wannan saidai babu damar magana

"welcome home akhie" inji Aysha tana ma Deen daketa bin harabar gidan murmushi

Jin kalmar 'HOME' yasa Deen jin wani iri a zuciyarshi ga yadda bugun zuciyarshi ke qara tsananta at every passing minute

"shall we?" inji Mussadiq yana kama hannun Deen


daidai entrance aka kawosu so basai sunsha wahalar yin wannan uwar tafiyar ba don daga gate zuwa ainahin gidan akwai tafiya sosai

hakan yasa nan da nan suka isa bakin kofar shiga

doorbell Mussadiq ya danna sau biyu sannan yaqara juyowa yana kallon Deen da kejin wani uneasiness ajikinshi ga wasu gumin dasuka fara tsatsafomashi a saman goshi, tunda yake beta6a shiga halin nervousness irin na yau ba

murmushin qarfafa gwiwa Mussadiq yayi mashi yana dan bugun shoulder dinshi daidai nan aka bude kofar.

ganin Mussadiq yasa maid din data bude kofar saurin jabaya tana russunawa cikin girmamawa tana musu sannu dazuwa

shigewa yayi still riqeda hannun Deen suka shiga qayyataccen falon

daya bayan daya kingin ma suka shiga Inda aymaan ne qarshen shigowa

duk sannu dazuwa maid din dake cikin uniform takemusu cikin girmamawa har suka gama shigowa sannan tayi saurin qarasowa falon tana nunamasu wurin zama duk suka zazzauna and within a twinkle of an eye anfara shigomasu da kayan ciye ana diddirewa

Aysha taso yin sama dagudu tun shigowarsu amma Mussadiq ya hanata saidai ya tabbatar kowa ya zazzauna sannan yayi excusing kanshi ya haye sama domin iske ummie can.

tun bayan tafiyar ummie falon yadauki shiru, Deen dai a zaune yake amma baya cikin nutsuwarshi kwata2 don ko a yanayin yadda yaketa gyara zama zaka gane hakan

zuciyarshi bugu take kamar ganga jiyake kamar zai mutu saboda nervousness

ahankali yaturahannayenshi biyu tsakiyar cinyoyinshi dake amiqe ta takure yana kallon qasa


sunkusa mintuna biyar ahakan kafin sufara Jin tafiya natahowa daga saman stairs

bugun zuciyar Deen yaqara speed nan take gumi suka fara tsatsafomashi takoina

be dago ba amma yana jin yadda sautin tafiyar keqara kusanto falon ga faint voices dayakeji suna tunkarosu


duk daga kai mutanen falon dasuka qagara suga ummie sukayi banda Deen suna kallon su ummie dasuke saukowa daga stairs din

kallo daya wadanda basu ta6a ganinta ba sai yau sukayi mata suka san cewa tabbas itace ummie, ko mahaukaci ya laluba zai tabbatar saboda mugun kammanin dake tsakaninsu kamar tayi kaki

tundaga nesa tafara sakamasu murmushi tana saukowa Mussadiq abayanta

dukda bata shaida kowa ba acikinsu hakan be hanata tarbarsu da fafadan murmushinta ba har suka ida saukowa stairs din

cikin larabci tafara musu lale marhaban cikin sanyayyar muryarta datadan manyanta

tunda muryarta ta daki dodon kunnen Deen kanshi yaqara kwancewa, inner jikinshi yafara rawa ahankali

qara cusa hannayenshi yayi tsakankanin kaffafunshi yana matsesu cikin rikicewa.

ida qarasowa cikin dakin sukayi Inda Mussadiq yayiwa ummie masauki a kujerar dake facing dinsu

cikin larabci tashiga sake yimasu sannu dazuwa fuskarta fall fara'a

sosai tayimasu kwarjini hakan yasa duk suka sunkuyar dakai suna murmushi

dan rad'a Mussadiq yayimata akunne hakan yasata yin Dan dariya sannan cikin harshen turanci tasake yimasu sannu dazuwa tana tambayarsu sun iso lfy?

duk amsa mata suka shigayi cikin girmamawa suna gaidata daya bayan daya tana amsawa tana kallonsu

idanunta ne ya sauka kan Deen da har lokacin kanshi ke akasa ya makure wuri guda kamar maijin sanyi

Dan tsiramashi ido tayi sannan takalli Mussadiq dake kusada ita

cikin tsokana a harshen turanci don Mussadiq ya gayamata akwai wadanda basajin larabci tace
"shikuma wancan d'an nawa fa? tsoron mutane yake?"

yar dariya duk sukayi sai Mussadiq yace
"da alama"

shidai Deen bedago ba saima lumshe idanun dayayi yana sauraron bugun zuciyarshi

"d'ana? wai dagaske tsoron.mutane kake?" inji ummie tana kallonshi keenly tana lura da yanayi da dama dake kamanceceniya dana wani wanda tasani

haka Kawai taji itama zuciyarta na halbawa tun lokacin data dora idanu akanshi

soyake ya dago amma yakasa, tsoro yakeji yakuma rasa na menene

"ummie da alamu dai tsoronki yakeji" inji Mussadiq yana murmushi

"ni?" inji ummie a mammakince

"ga alama nan" yafada yana kallon Deen fuskarshi fall murmushi

sake kallon Deen da ina part dinshi kerawa sosai tace
"d'ana dago ka kalleni kaji?"


zuciyarshi ce tabada damm! lokacin dayaji ta kirashi da d'anta

ahankali yashiga dago kanshi kamar mai tsoro cikin bin umarninta harya ida dagowa

idanunsu ne suka sarqe dana juna wanda yayi daidai da bugawar zuciyarsu alokaci guda


kafe juna sukayi da idanu Inda Deen ke kallon fuskar mahaifiyarshi for the first time in his life yayinda ummie afarko kallonshi take blankly kamar wanda hankalinta yagudu na wucin gadi saikuma ahankali tadawo daidai

ahankali idanunta suka shiga warawa akanshi kamar kuma wanda aka tsikara tayi saurin juyowa ta kalli Mussadiq da har lokacin ke kusada ita


maida kallonta tayi akan Deen dahar lokacin kallonta yake babu kyaftawa atsorace saikuma taqara kallon Mussadiq

qara kallon Deen tayi dasauri sannan taqara kallon Mussadiq kamar wata zarrariya

ahankali tafara qoqarin tashi jikinta na rawa, ganin hakan yasa Aysha saurin qarasawa wajen tana riqota

juyowa tayi atsorace ta kalli Aysha din saikuma taqara kallon Deen ta kalli Mussadiq

"Aysha.. idanuna gane gane sukemin, gani nayi yayanki yakoma biyu" tafada cikin rawar murya tana qoqarin tashi

qoqarin maidata zaune Aysha tashiga yi tana cewa
"ki kwantar da hankalinki ummie..."

"yayanki biyu fa nake gani, ko idanuna sunfara lallacewa ne? kalla kigani ga wani can ga wani nan" tafada tana qara binsu da kallo kamar ta66a6iya

"eh ummie su biyu ne, nima nagani"

wani irin wara idanu ummie tayi

"kema kingani? kinga su biyun"

kada kai Aysha tayi tana qoqarin danne hawayenta
"eh ummie, aidama su biyu ne, dama su biyu kika haifa"

shiru ummie tayi tana kallonta saikuma tace
"eh subiyu na haifa amma ai yanzu daya ke akwai, wancan ya... ya..." saikuma takasa idawa sai juyawa datayi tana kallon Deen dake kallonta har lokacin zuciyarta na wata iriyar bugawa

kusada ita Mussadiq yazo ya duqa
"beyi komai ba ummie, beyi komai ba... gashi nan yadawo gareki"


kallon Mussadiq tayi shock all over her face

kada mata kai yayi
"yes ummie, Mujaheed dinmu beyi komai ba, gashinan yadawo, gashinan agabanki, yadawo garemu"

girgiza kai ummie tashigayi unbelievable jikinta na rawa sosai

"No" tafada unbelievable

"yes ummie Mujaheed is alive"...✍�



*I can't go futher, kuyi manage please banajin wellπŸ€’*



Ummin FasihuπŸ§šπŸ»β€β™€οΈ?
8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *πŸ™πŸ»β€β™‚οΈDEENπŸ™πŸ»β€β™‚οΈ?*










*086*











girgiza kai ummie tashigayi cikin rashin yarda, tayaya za'ace Mujaheed na raye bayan an tabbatar agaban idanun mutane ya qone cikin mota

"he was kidnapped ummie not killed, dama nasan Dan uwana bazai mutu hakanan ba, nasha ji ajikina akwai wani sashe na jikina a wani wuri, nasha jina incomplete, ashe shine kuma gashi cikin yarda allah yadawo, yadawo garemu ummie dawowa ta har abada" duk wannan maganar da Mussadiq keyi idanunshi nakan Deen dake kallon ummie still

itama ummie idanunta na kanshi tana Jin wani irin feeling mai qarfi na yawo a ilahirin jikinta

tashi Mussadiq yayi yaqarasa wajen Deen dake makure waje guda har lokacin yariqo hannunshi ya tadoshi tsaye sannan yanufo ummie

duk da kallo mutanen falon sukabisu dashi harsuka qarasa wajenta

jan Deen Mussadiq yayi qasa ya kasance sun duqa agaban mahaifiyar tasu

"Mujaheed ga ummie, ummie ga Mujaheed, rabonku da juna shekaru ashirin da uku kenan amma na tabbata koda bayan shekaru dubu ne kuka hadu bazaku kasa gane juna ba"

hawaye sosai kezuba a idanun ummie data kafe Deen dasu

shima Deen hawayen yakeyi involuntary yana bin fuskarta da kallo


hannu ummie tadaga ahankali tadora afuskarshi kamar mai tsoro, ahankali tashiga tatta6a fuskar

"Mujaheed?" tafada tana cigaba da tatta6a fuskarshi

"ummie.." Deen shima yafada ahankali

"Mujaheed"

"ummie na"

"Mujaheed na!" tafada daqarfi tana jawoshi ajikinta lokaci daya cikin fashewa dawani matsanancin kuka

wani irin warmness yaji lokacin data sakashi ajikinta, warmness din dabazai iya misaltawa ba

yasha samun warmness ajikin Kaka idan ta rungumeshi amma wannan na daban ne don sai jiyayi kamar yanarke su cigaba daxama ahakan saboda wani unexplainable sense of comfort dayakeji a jikinta

dama wannan ake kira da mother embrace?

kuka sosai ummie keyi tana magana at the same time cikin larabci, tariqeshi gagam kamar zata sakashi ajikinta

shima dai jiyake kamar yashige cikin jikin natan ne don shima gagam ya rungumeta

bayajin Abinda take cewa amma ga duk kalma daya dazatayi saiya amsa da kalmar 'ummie na'

kuka suke sosai su biyun kowanne uncontrollable

ahakan wani irin tari ya sarqe ummie tashigayi babu kakkautawa

Jin hakan yasa Deen raba jikinsu yadago yana kallonta sai yaga she's coughing blood, tana tari jini nafita abakinta

arude ya riqota ahannunshi jikinshi na rawa sosai

"ummie! no..No, ummie No!" yafada cikin ihun kuka yana dan jijjigata

da gudu kingin yan dakin suka qaraso wajensu cikin tashin hankali

"ummie kar kiyimin haka please! please stop am scared!" yafada cikin kuka sosai yana mannata ajikinshi not minding yadda jinin ya 6atamashi kaya

har lokacin tarin ummie keyi amma a mugun galabaice

Mussadiq kau tuni yatashi arude yakoma gefe yafara qoqarin lalubo number family Dr dinsu

aymaan ne yaqaraso gaban Deen yana qoqarin amsar ummie ahannunshi amma Deen ya matsa baya yana qara qanqameta

"No! go away!... ummie na" yafada cikin fitar hayyaci yana qara qanqame ummie din

"calm down ok? she's gonna be ok, kabari nadubata" inji aymaan ahankali

"No!" Deen yaqara fada cikin kuka sosai gani yake kamar sake rabasu za'ayi

"idan baka bari nadubata ba zamu iya rasata, ka duba kagani she's in a very critical situation, tama suma zamu iya rasata"

sai a lokacin Deen yafara dawowa hankalinshi saidai be saketan ba sai maida numfashin dayakeyi

"kabari a dubata before it's late, kun dade ba atare ba nasan yanzu bazakaso kuyi rabuwar har abada ba" inji aymaan again cikin persuading voice

maganar aymaan tashigeshi hakan yasa yafara nutsuwa

qara matsowa aymaan yayi kusada ita yana neman kama ummie din

"kawota na kaita saman kujera"

maimakon yabashi din saiya qara qanqameta yafara qoqarin tashi daita

"easy" inji aymaan yana dan tarosu ganin zasu fadi

da taimakonshi Deen yakaita kan dagowar kujerar ya kwantar saidai yaqi matsawa ko inch daga kusada ita saima bake wajen dayayi


"alright, kadan matsa nadubata" yafada gently

ahankali Deen ya matsa din amma hannunshi na riqe da nata gamm kamar wanda za'a kwacemawa

babu 6ata lokaci aymaan yafara dubata

ruwa da tissue yafara buqata

dagudu Aysha dake tsaye tareda batool sunci kuka sun godewa allah taruga ta dauko tabashi


amsa yayi yafara bata ba ummie taimakon gaggawa cikin qwarewa

Mussadiq daketa safa da marwa shima tsayawa yayi yana kallon aymaan don har lokacin Dr din daya kirawo be isoba


cikin qwarewa aymaan yashiga ceto rayuwar ummie








🀍🀍🀍🀍🀍🀍🀍🀍🀍🀍




zaune take takafe waje da kallo ta glass window dake kusada ita

kofin shayi ke hannunta wanda tuni yahuce ma don tunda aka bata kur6a biyu tayimashi takuma fita babinshi


idanunta na kafe akan window daya kasance glass ne don ana iya hango waje tarr ta wajen

kallo daya zakayi mata kasan bata awannan duniyar tamu kwata2


bude kofar dakin akayi ahankali aka shigo

Inda ta barta nan tazo ta sake taddata

girgiza kai Kawai tayi sannan tanufeta

zee batama san da shigowarta ba saida taji an dafata

saurin dagowa tayi daga duniyar tunanin data lula

ganin ummy ce yasa tadanyi murmushi tana kai kofin shayin da har yayi sanyi baki

murmushin itama ummy tayi mata taja kujera ta kawo kusada ita ta zauna

"daughter" takirata ahankali

dagowa zee tasake yi ta kalleta

"haryanzu baki shanye shayin ba?"

qara kai kofin zee tayi abaki ta kur6a dukda rashin dadin dayake mata gashi yayi sanyi

"gashinan ina sha ummy"

murmushi ummy tayi

"ai yama huce ko? mugani kinasonshi ahakan ko ahada wani mai zafin?"

saurin bata zee tayi cikin marairaice fuska tace
"ni nama qoshi ummy kalla kigani nasha dayawa"

kallon shayin da ba'asha ko kwata ba tayi tayi murmushi tace
"to shikenan yanzu tashi ki chanza daddy na qasa yana jiranki kutafi yawo"

nan take fuskarta tayi brightening

"dagaske?" tafada cikin zumudi

"dagaske, maza yi sauri kar yaita jira"

da sauri ta tashi cikin jindadi

dama tagaji da wannan zaman loneliness din tasan koyaya suka fita koda kaso kadan ne zai rage daga cikin damuwarta


wucewa bathroom din dakin tayi ummy tabita da ido cikeda tausayawa saikuma tadan girgiza kai sannan ta tashi tafita riqeda kofin shayin zee din




***







Ahankali tafara bude idanunta dasuka yimata nauyi

da farko biji biji tafara gani sai ahankali ahankali ganinta yafara dawowa

akan fuskarshi tafara sauke idanunta yana kallonta itama affectionately

lumshe idanu tayi akanshi tasake budewa and he's still there

hakan ya tabbatar mata ba mafarki bane kamar yadda tayi tunani

"ummie na" yafada ahankali yana qara damqe hannunta dake cikin nashi

idanunta ne suka fara qyallin hawayen dasuka fara taruwa a kwarin idanunta

girgiza mata kai yayi yana kai hannunta dake hannunshi saitin bakinshi ya sumbata yace
"don't ummie, you're sick, please no more tears.. am here"

ahankali takai hannun nata tashafi gefen fuskarshi daidai nan hawayen suka gangaro

dora nashi hannun yayi saman nata dake bisa kumatunshi yasa dayan hannun yana share mata hawayen



"ina katafi kabarmu?" tafada in tears

"bazan qara barinku ba" ya amsa mata

riqo fuskarshi tayi
"karka qara nisantarmu kaji? karmu sake haka dakai"

"har abada ummie.. har abada"


rungumeshi tayi cikin shauqin qaunar d'an nata mafi soyuwa a zuciyarta

shima rungumeta yayi yanajin kamar su dawwama ahakan

ahankali Aysha ma ta matso tayi joining dinsu ganin hakan yasa shima Mussadiq qarasawa suka rungume juna dukkansu in a big family hug

kowa na dakin murmushi ne afuskarshi na farinciki da taya murna na wannan family reunion din



saida komai ya lafa sannan su aymaan suka nemi tafiya

anan ummie taso riqesu wai ba yanzu ba su tsaya suci abinci inyaso idan sun tashi tafiya saisu tafi tare don sotake suje suyima su Abbu godiya don they own them much


cikin girmamawa sukayi turning request dinta down Inda suka nuna gwara dai su tafin kuma ai batada lafiya tafiya bazata yiwuba agareta yanzu

ba don taso ba tabari suka tafi Inda tasa aka kaisu bayan goma ta arziqi data hadosu dashi wanda saida tayimasu tilas sannan suka amsa


bayan tafiyar su aymaan ummie tasa aka kirawo dukkan ma'aikatan gidan Inda anan tayi musu introducing Deen amatsayin d'ayan d'anta kuma twin din Mussadiq

sosai ma'aikatan sukayi mashi maraba cikin girmamawa a qasan zuciyarsu kuma suna mammaki to ina yashiga tuntuni don sudai basu ta6a ganinshi ba ko sanin dashi

anan ummie tabada order ashirya abinci Inda nan take tasa akayo hiring kuku wadda ta iya abincin Africans

agefe kuma kaya sosai tasa aka fitar domin yin sadaka ga mabuqata amatsayin nuna godiya ga allah daya bayyana mata d'anta

da farko taso sanarda yan saudiya saidai Mussadiq ya hana yace ai zasuje subari Kawai sai sunje


shidai Deen dan kallo yazama shida habeeb da aka barsu tare suna kallon irin rawar kafar da akeyimasu kowa burinshi ya faranta mashi.

Daga baya wani haddaden part aka kaisu don suyi wanka su shirya Inda part din ma abin kallo ne don ya qayattu iya qayatuwa


har lokacin Deen bebar Jin komai kamar a mafarki ba, Kawai gani yakeyi soon za'a tasheshi ya farka yaga komai mafarki ne


koda suka gama shiryawa sukayi Acikin wasu tsaddadun kaya wanda tuni akayi musu order su

saida suka shirya tsaf sannan suka dawo main falo din Inda anan akayi leading dinsu zuwa dining area wanda izuwa lokacin shake yake kalolin abinci daban daban

akusada ita ummie tasashi zama tashiga serving dinshi da kanta, kallo daya zaka mata kasan tana cikin tsananin farinciki

shikau Deen maidata t.v Kawai yayi dama gashi akwai asirin kallo ya iya kafe abu da kallo babu ko gajiya


duk Abinda tanuna mashi akan yanaso zai kada mata kai Kawai idanunshi akanta, kwata2 baya qaunar Abinda zai janye mashi hankali daga kallon wannan kamillaliyar fuskar tata

itama ta lura da kallon dayake mata saidai bata damuba don tasan ba laifinshi bane koda yayi fiyeda hakan don itama tana iya kwana tana kallonshi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login