Showing 219001 words to 222000 words out of 322641 words
Chapter 74 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
nufi kofar
Saidai suna kaiwa inda tsakaninsu da motar baya wuce taqi ashirin sukayi mugun ganin da basu ta6a irinshi ba
Motar da akace masu mujaheed na ciki ta tashi da wuta๐ฅ a gaban idanunsu.."โ๏ธ
Ummin fasihu ๐ง๐ปโโ๏ธ?
8/2/21, 9:42 PM - Buhainat๐: *๐๐ปโโ๏ธDEEN ๐๐ปโโ๏ธ?*
*068*
*THE UNVEIL 2*
_๐ni yau ido rufe zanma yi typing saboda kunyar wasu nakeji ๐๐_
Toshe baki zee tayi idanunta awaje tana kallon Aysha da kuka yafara cin qarfinta
"a..agaban idanunsu motar taita ci da wuta... Abbanmu ahakan yaso qarasawa ga motar amma Hussaininshi da tsirarun mutanen da wutar tajawo hankalinsu suka hanashi ta hanyar rirriqeshi.
And..and before his very eyes, beloved son dinshi ya qone qurmus dashi da mot..."
Kasa idawa tayi saboda kukan dayaci qarfinta.
Kamar hadin baki da zee da batool suka rarrafa wajenta suka rungumeta suka hada kai waje guda suna kuka kamar ransu zai fita
Sun dauki tsawon lokaci ahakan anrasa wanda zai rarrashi wani
Can Aysha ta dago da jajjayen idanunta tana kallon su zee da har lokacin kukan sukeyi
"ba acikin hayyacinshi ba aka maido Abbanmu gida, daga nan akayi asibiti dashi.
Itama ummie najin abinda yafaru ta yanke jiki ta fadi, kan kace me jini ya 6allemata
Itama kamar abba sai aka kwasheta sai asibiti.
Kamar hadin baki shima mussadiq jikinshi ya rikice yashiga convulsing, numfashi ma Dakyar yake fizgoshi daga huhunshi.
Iya tashin hankali wannan ahalin sun shigeshi a lokacin.
Nima don Allah yayi zanzo duniyar shiyasa cikin ikon allah aka shawo kan bleeding din da ummie keyi
Lokaci guda happy family dinmu ya tashi daga happy family zuwa akasinshi
Abba tunda ya kwanta gadon asibiti be qara tashi ba
Saida yayi wata daya a kwance sannan watarana yatafi cikin barcinshi.
Yatafi yabi danshi yabar matarshi abar qaunarshi da cikin dake jikinta dakuma danshi da har lokacin beda cikkaken lafiya.
Haka ummie tayi takabarshi, ga ciki ga ciwo don tun lokacin da ta yanke jiki ta fadi lokacin da aka dawomata da labarin mutuwar mujaheed ta hadu da ciwon hawan jini.
Haka tayi takabarshi tagama ta cigaba da zama gidanmu tareda mussadiq da shima izuwa lokacin ya warware sosai Saidai kwata2 ya chanza daga mussadiq din da aka sani.
Mussadiq mai qiriniya mai surutu yakoma so silent.
Yana iya yini batareda ya furta ko kalma daya ba, ga wata rashin yarda da ya bijiro daita lokaci guda.
Baya yarda wani ya ra6eshi ko kadan Duk yadda kau kake dashi.
Ko baqi ummie tayi walau family dinmu ko wasu daban baya yarda yabar jikin ummie duk inda zata yana maqale daita.
Idan baqin zasu shekara suna mashi magana ko kallo bazasu isheshi ba
Idan kuma sukace zasu daukeshi da tsiya sai ya fasa ihu kamar wanda ake yankawa Hakan yasa duk masu qulafucin daukarshi suka haqura Saidai gani daga nesa wato ajikin ummie
Da farko ummie tayi tunanin yarinta ne kuma qila harda abinda yagani ranar da abin yafaru tunda tana kyautata zaton kome yafaru a ranar mussadiq yagani tunda da alamu ma kamar shi kuftowa yayi Saidai a lokacin ko an tambayeshi bazai iya bada amsa ba don qarami ne sosai magana ma bata gama nuna a bakinshi ba
Hakan yasa take yimashi addu'o'i sosai da rubutun sha duk na dangana wanda zai kuma taimaka mashi wajen manta abinda ya faru din
Saidai abin yafara bata tsoro ne ganin harya fara girma bai bar wannan sabon halin nashi ba
A lokacin baya zuwa ya lafe jikin ummie Saidai duk tsiyarka daga nesa nesa zaku gaisa dashi ya maida fuskar ya
dinke tsaf idan zaka shekara yimashi magana bazai amsa ba
A lokacin an haifeni sai ya kasance bayan ni da ummie babu wanda yake kuma yarda dashi.
Anyi maganin anyi gwajin both physically and mentally amma result din ya nuna babu abinda ke damunshi, he's normal Saidai a kowacce rana abin nashi qara gaba gaba yakeyi
Har takai ni kaina yafara hanani kula mutane, ko zuwa yayi ya ganni da yara muna wasa saiya fizgoni daga cikinsu ya hanasu zuwa wajena kuma gashi a lokacin mugun tsoronshi yara sukeyi saboda rashin warginshi shiyasa wani lokacin da sun ganshi sai su gudu ko susha Jinin jikinsu, lokacin fa bazai wuce shekaru goma sha biyu ba Saidai rashin warginshi yasa ko manya saisu kasa tsawatar mashi saboda kwarjinin dayake masu
Wannan abin ba qaramin cima ummie tuwo a qwarya yake ba don da dama can haka yake da da sauqi amma sanin cewa daga baya ya bijiro da wannan halin yasa abin ke damunta sosai
Ko shiryamu tayi muje gidajen danginmu baya zuwa Saidai yaita yawo dani mudawo gida, idan tagane Hakan saita tisa shi gaba da fada shikuma data fara sai yaita kuka kamar ranshi zai fita
Tasha zaunar dashi ta tambayeshi meyasa yake abinda yakeyi ko wasu sukeson yimashi wani abu ne? Sai ya girgiza kai kawai yace
'ummie banason kowa sai ke da ukhtie'
Haka rayuwa taita tafiya tun ummie nasa abin a rai harta fawwalawa allah komai ta cigaba da Binshi da addu'a
Mussadiq ko a makaranta be ta6a yin aboki ba nima ya hanani yin qawa ko daya, kasancewar shi kadai ne yaya na kuma abin koyi na tunda mostly sai kiga a kowanne gida qarami yafi saurin koyi da wa ko yayanshi bisa ga yadda zasuyi koyi da iyaye saboda kusanci dake tsakaninsu, sai ya kasance nima bana Sakin jiki da mutane ko a family dinmu ne don ko ummie ta tilasta mana zuwa gidajen su bama shige masu, daga gaisuwa shikenan, gwara ni fuskata kodayaushe asake take kuma idan akayi min magana zan amsa asake shikau yaya a kodayaushe fuskarnan tashi na dinke tsaf ko magana akayi mashi cikin cin magani zai amsa.
sai ya kasance bamuda wata qawa sai Umminmu
Haka zamu zauna mu ukunmu muyita nishadi wanda mostly dama a lokacin ake ganin Dariyar yaya mussadiq
Familynmu kau tun suna surutu wai ummie takasa controlling dinmu tasanya mana aqidar qin jininmu a zuciyarmu har suka gaji suka qyaleta suma suka yanke mu'amala daita suka bar aiko yaransu gidanmu wanda Hakan ba qaramin dadi yayi wa yaya ba
Saidai dukda Hakan ummie bata fasa turamu zuminci gidajen su ba dukda ba wani kulamu suke ba idan munje ita acewarta ta fita haqqin zuminci
Kawu Hussaini da iyalanshi ne kawai wanda basu juya mana baya Ba, kuma 'yayanshi na zuwa gidanmu shima kanshi yana zagayowa akai akai yana duba lafiyar mu kuma ko sau daya be ta6a nuna 6acin ranshi akan halayen mussadiq ba, yana matuqar haquri akan Hakan don shi mutum ne mai matuqar haquri da kawaici.
Ahaka har yaya mussadiq yagama karatunshi ya mallaki hankalin kanshi to a lokacin Kawu hussain ya damqa mashi gadonmu dake hannunshi tun rasuwar Abbanmu
Kasancewar fannin kasuwanci yaya mussadiq ya karanta saiya zuba kudadden a business yafara jujjuyasu
A lokacin kawunnan mu da danginmu maza sunyo caa wajen bama mussadiq shawarar yadda zaiyi da kudin Saidai duk ya watsa masu qasa a idanu ta hanyar yin watsi da dukkanin shawarwarunsu yayi amfani da nashi
Cikin ikon allah sai gashi allah yasama abin albarka kasuwancinshi yafara girma
Nan kuma danginmu suka tuso ummie gaba da maganar aure, wai ya kamata mussadiq yayi aure tunda ya isa kuma ko a dangine yana iya za6ar wacce yakeso tunda akwai yanmata kala kala a dangin.
Firr mussadiq yaqi yarda yana cewa shi yanzu ba aure ke agabanshi ba kuma Koda auren zaiyi sai wacce yakeso basai an kawo mashi tallar yanmatan dangi ba
Wannan abin ba qaramin rikici yakawo a danginmu ba, nan kowa ya dora laifin akan Umminmu wai ita keson rabamu da dangin mahaifinmu, sosai abin ya damu Umminmu a lokacin takuma so fahimtar dasu akan bazata iya yiwa mussadiq dole ba akan ya auri wata ba amma sukaqi sauraronta saima suka dauki gaba da ita da muma gabadaya
Ashe tun farkon rikicin yaya mussadiq ke tattara dukkanin harkokinshi yana maido su nan dubai
Kwatsam watarana yazo ma ummie da maganar komawarmu dubai
Da farko ummie qin yarda tayi tana cewa babu abinda zai fiddata daga saudiya Hakan kamar tabbatar da magangganun dangin Abbanmu ne na tanason rabamu da danginmu ne
Dakyar mussadiq yashawo kan ummie inda Saida yabi gidajen dangin namu da daddaya yana fadamasu kasuwancinshi zai kaimu can ba wani abu ba kuma zamu ware lokaci muna zuwa saudiya ziyara
Abin mammaki sai aka rasa wanda zai qalubalanceshi akan hakan, hayaniya da cecekucen da ummie tayi tunanin zasuyi sai taji tsit basuce komai ba
Hakan yasa muka tattaro namu ya namu muka dawo nan dubai da zama
Cikin ikon allah cikin qanqanin lokaci business din yaya ya ha6aka yayi albarka, budi yaita shigo mashi takoina, kowa na kwadayin samun share a company dinshi kasancewarshi jajirtacce a aikinshi ga riqon Gaskiya don yaya mussadiq ba duk rintsi baya cutar mutum kuma baya bari a cuceshi shiyasa bada kowa yake aiki ba saiya yarda dakai dakuma qwarewarka a aiki dakuma yanayin riqon amanarka
Har lokacin dabi'arshi ta rashin yarda na nan, baya barin wani space komin qarantarshi wanda xa'a iya yaudararshi, yana yin komai nashi cikin taku shiyasa Koda yafara bude wurare irinsu parks, malls da makarantu be sanya sunanshi ko sunan daya daga cikinmu ba saiya za6i yasanya wani sunan daban wanda duk qwaqwar mai qwaqwa bazai san mai su ba sai idan dama can ya sanshi.
Gwara gwara gidajen marayun dayake dasu wanda ya bude su da sunan Abbanmu da dan uwanshi mujaheed wanda yatara marayu aciki yana kula dasu da saran ladar Hakan allah yakaima su Abba har cikin qabarinsu.
Danginmu na kawo mana ziyara jifa jifa muma muna zuwa qaranci sau biyu a shekara mostly qaramar sallah da babbar sallah.
Tunda muka dawo nan qasar ban ta6a yin qawa ba sai akanki, bansan meyasa ba tun aganin farko naji kin kwanta min arai, naji kamar akwai wani connection tsakanina dake.
Dan zaman da mukayi dake farko farkon abotarmu kuma yasa kika ida shiga zuciyata naji komai naki na burgeni, a lokacin na bawa Umminmu labarin ki kuma na hadaku a waya inda itama nan take kika kwanta mata takuma bani go ahead akan abotarmu
A lokacin yayana bayanan yana switzerland business trip kamar yadda yasaba tafiye tafiyenshi na business
Tun yana can nake bashi labarin ki, dafarko ya nuna 6acin ranshi akan Hakan yana cewa ba ya hanani yin abokai ba? Amma saiya haqura lokacin da ummie tayimashi magana tace itama tasanki ke mutuniyar kirki ce, babu yadda ya iya saiya kyaleni kawai amma yayi min gargadi akan na dinga kulawa
Jiya kwanan shi biyu da dawowa kuma tunda yadawo nake addabarshi akan yazo ya ganki Saidai yace he's busy amma idan yasamu lokaci zaizo
Shine fa kwatsam jiya muna zaune dake a library yayi min text akan gashi nan yazo ganin bestie din tawa dana addabeshi da batunta shiyasa kikaga na Kamo hannunki cikin jindadin wannan bazatar dayayi mana, ashe halinshi zai saida nan saniba"
Ajiyar zuciya duk sukayi kowannensu idanu jajur a dalilin kukan dasuka sha na labarin mujaheed.
"wataqila ba laifinshi bane shima... Tabbas mun ta6a haduwa dashi sau biyu kafin ranar
Ranar farko yayi min kama da wani dana sani a Nigeria shiyasa naje na sameshi, am so desperate that banyi saurin gane bashi bane ba sai daga baya, daga bayan ma bayan yatafi.
Haduwarmu ta biyu kuma a wani supermarket ne, nida batool munje siyayya sai bamu samu abinda mukaje nema ba kuma munga abin a magazine dinsu shiyasa ma mukazo shopping din
Sai naje wajen cashier nayi complaining akan Hakan saiya bani haquri yakuma kira akace ya turoni na amsa sama wajen Manager
To wajen zuwa office din Managern na 6ace
Naita shige shigen hanyoyi amma nakasa gane hanya kuma narasa hanyar dazanibi nadawo inda nafito.
To anan muka sake clashing dashi inda nan take yayi concluding Binshi nake, I was shocked and scared jin yana tuhumata da bibiyarshi, Dakyar nasamu su cashier sukazo suka ceceni a wajenshi
To kinga after all these, ganina kwatsam a matsayin qawarki dolene ya tabbatar mashi da zarginshi, I know shiyasa yayi concluding akan tabbas ni yar leqen asirinshi ce bayan bemasan ita kanta kalmar spy din ba qaramin kadamun hanji yake ba idan aka ambaceta"
Dariya duk sukayi
"that's yaya mussadiq for you, komai saiya dora mashi ayar tambaya. Jiya ran ummie ya 6aci sosai dajin abinda ya aikata shiyasa nan take tasashi Sakinku" inji Aysha
"Allah sarki, ai bayada laifi, duniyar ce ta zama abin tsoro, mutane ba abin yarda bane... Nikau sai naga kamar mussadiq baya rasa sanin wani abu gameda sace mujaheed, as in why lokaci daya zai chanza yabar yarda da mutane bayan da ba Haka yake ba?" inji batool
"abinda yake daurewa kowa kai kenan, tabbas qila yaga wani abin wanda ya firgitashi amma kuma yakamata ya manta tunda lokacin da abin yafaru yanada qarancin shekaru tunda lokacin shekarun su uku uku da yan kai"
"nikuma nafi zargin cikin familynku, anya babu wanda mussadiq ke zargi acikinsu duba da yadda be yarda dasu ba kwata2?" inji zee
"hmm I donโt think so ummie saboda kamar yadda nafada dazu lokacin da abin yafaru yanada qarancin shekaru bazai iya recalling komai ba kuma da ace zai iya da nasan zai fadane right away, kawai ni nafi tunanin razanar abinda yafaru aranar ne taqi sakinshi haryanzu, a lokacin brain dinshi is so fragile wajen daukar irin wannan shock din shiyasa abin yayi affecting dinshi sosai ya zauna ajikinshi har girmanshi batareda shi kanshi yasan meyake damunshi, wataqila Hakan yasa mashi tsoron mutane da rashin yarda dasu har zuwa wannan lokacin don so da dama idan ummie ta tsareshi da Tambayar meyasa yake saurin zargin mutane kuma baya saurin yarda da mutum sai yace shima besaniba kawai yana ji ajikinshi kowa ma na iya zama maqiyinshi shiyasa yakasa yarda da kowa"
Duk Kada kai sukayi cikin alhini, tabbas akwai lauje cikin nadi a wannan al'amarin, dagaske ne mussadiq besan komai ba kawai Hakan nan ne yake jin baya iya yarda da mutum ko yanada dalilin yin Hakan? Allah kadai yasan Gaskiya dashi mussadiq din
Ajiyar zuciya batool ta sauke
"to allah ya bashi mafita akan abinda ke damunshi, allah yajiqansu Abba"
Da ameen duk suka amsa Saidai deep down batool da zee sunsan wannan addu'ar ta Abba ce kadai don mujaheed nanan da ranshi
Cigaba da firarsu sukayi wanda duk ta deen ce, Aysha nabasu labarin yarintarshi wanda itama ummie ke bata su don sosai Aysha ke kaunar deen dukda bata zo ta tardashi ba, da kingata zaune da ummie to labarin deen suke har wani dadi takeji idan ummie na fadin abubbuwan data biyo nashi musanmman a hallaya sai tajita cikin shauqi na musanmman.
Sai gab da magrib drivern gidansu Aysha yazo
Saida suka rakata wajen ummu batool sukayi bankwana inda tabata kyautar turarruka takuma bata saqon gaisuwa ga umminsu sannan tacewa batool ta dauki rubber dambun naman datayimata dazu a kitchen idan sun sauka tabata, godiya sosai Aysha tayimata sannan suka fito
Atare su ukun suka sauko qasa suna tafe suna fira cikin raha
Wucewa batool tayi don yin yadda ummu batool tace sukuma suka nufi kofa.
Wayar Aysha ce tayi ringing daidai sun kusa isa bakin kofar
Dubawa tayi saikuma ta dago ta kalli zee
Harara zee ta gallamata cikin wasa ta kauda kai don ko ba'a fadaba tasan wannan umar dinne
Dan murmushi Aysha tayi sai kuma tayi saurin yin gaba don amsa kiran kafin ta tsinke
Dayake sauri take kuma hankalinta na kan waya bata lura da bude kofar da aka rigata yiba tasa kai sai quuuum! Taji taci karo da abu
Yar qara tasaki taja baya tana sosa goshinta cikin yanayin jin zafi
"ya sallam! Are you ok?" Taji muryar zee dake qarasowa na fada a bayanta
Daga kai tayi taga mai ya qumeta sai taganshi shima tsaye yana murza goshinshi cikin yanayin jin zafi
Sanye yake da farar spotless shirt da baqin wando sai lapcoat dinshi rataye a kafada
Dagowa yayi shima ya kalleta sai suka hada ido
Ganin yadda ya 6ata fuska yana kallonta yasata Dan buda idanu tace
"oh! Sorry"
Bece komai ba Sai duqawa dayayi yana tsintar Wayar data fadi qasa
Binshi da kallo tayi sai taga ashe Wayar hannunta ne ta fadi
Kafin tayi wani abu harya miqe ya miqomata
"oh, thanks.. So much" tafada tana amsar Wayar
Kada kai yayi
"always be careful kuma ki dinga kallon gabanki don next time bazaki sa'ar karo da abu mai taushi kamar goshina ba, sai abu mai mugun tauri kamar garuu"
Dariya zee da batool data fito yanzu sukayi yayinda Aysha ta 6ata fuska
"wayace maka goshin naka da taushi? Dafarko nayi tunanin da dutsin marmara(rock) naci karo"
Wani kallo yayimata yace
"koba dutsin marmara ba" ya cigaba da tafiyarshi
"gayamashi dai ukhtie, kedai idan kika koma gida ki tabbatar ummie takaiki kinga mai duba qashin kai, kar ace wani wuri ya tsage baki sani ba" inji batool
Dariya Aysha da zee sukasa yayinda aymaan ya dakata Daga tafiyarshi ya juyo ya kalleta sai kuma ya cije lip ya girgiza kai
"kinci sa'a agajiye nake yanzu amma ki kiyayi haduwarmu"
Dariya suka sake sawa shikuma ya cigaba da tafiyarshi ya nufi stairs
"ammm... Akhie?"
Jin Hakan yasashi dakatawa daga hawan stairs din dazai fara saiya juyo
Fuska dauke da murmushi tadan qara matsowa gabanshi
"erm.. Dama akan abinda yafaru jiyane... Am sorry on my behalf, my brother's and my mum. Am sorry about that and that won't happen again insha allah"
Sai a lokacin yama shaidata, kamar wanda yagani tareda wannan marar mutuncin jiya
Kallon zee yayi sai itama tadan tako tana cewa
"Aysha... Sunanta Aysha, qanwar mussadiq, tazo bayar da haquri ne on his behalf"
Sake maida kallonshi yayi akan Aysha da tadan sha jinin jikinta Ganin yadda yanayin fuskarshi ta chanza
Dan ta6e baki yayi yace
"oh? Thanks then" saiya juya ya cigaba da tafiyarshi harya haye sama
Bataji dadin Hakan ba don sai taga kamar shi be haqura ba
Zee ce tadan yi Dariya tace
"Dayake yanzu yadawo kuma ya kwaso gajiya, don't worry Hakan yake idan yana gajiye" inji zee duk don Aysha taji Dama dama
"saikace wani ya aikeshi ba" inji batool tana qarasowa itama
Murmushi Aysha tayi tace
"ai dole, aikin hospital akwai wahala"
Da Hakan