Showing 171001 words to 174000 words out of 322641 words
Chapter 58 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
tambayeni? Tafiki iko da gidan, me zakiyi?"
Kumbura fuska tayi kamar zatayi kuka
Dariya Abbu dake sauraronsu Tundazu yayi yace
"Allah ya shirya ku, nidai karku koyawa yayata wannan halin naku, tana yar saliharta itama ta koma burkakka"
Dariya duk sukayi itakuma zee ta sauke kai tana dan murmusawa
Matsowa Aymaan yayi kusada Abbu cikin rada yace
"Abbu wai wacece?"
Murmushi Abbu yayi yace
"ai dole ka tambaya, kaida bakasan kusan mafi yawa cikin danginka ba.
To Zainab ce ta gidan daddy, daddyn Nigeria"
Wara idanu Aymaan yayi saikuma ya qara kallon zee da bashi take kallo ba
"you mean diyar Daddyn Nigeria?"
Kada mashi kai Abbu yayi in affirmation
"wannan yar yarinyar? Yaushe ta girma haka?" inji Aymaan cikin mammaki
Dagowa zee tayi jin abinda yace sai suka hada ido
Hararar da batasan tayi ba ta gallamashi don sosai taji haushin kiranta da yar yarinya dayayi
Ganin Hakan yasashi kauda kai yana Sosa qeya bakinshi dauke da murmushi
Dariya duk aka dauka falon ummy tace
"ba dole kayi mammaki ba? Yaushe rabonka da Nigeria? Almost 6years ba dole ta chanza maka ba?"
Qara satar kallonta yayi yaga bama gefen shi take kallo ba
"hmm ai zanje kwanan nan" yafada yana wucewa dining
"kamar duka kenan" inji ummy
"Allah kau ummy, bari aiki ya dan lafa, zan baku mammaki" yafada yana jan kujera daya ya zauna
"hmm allah yasa" inji ummy
"Amin dai ummy" batool ta amsa
Dagowa Aymaan yayi ya watsamata mugun kallo
"ba na hanaki sakamin baki a magana ba?"
Turo baki tayi ta koma bayan ummy
"bazaki zo Kiyi serving dina ba?" yasake fada yana huro hanci
Qara turo baki tayi sannan tazo ta wuce kitchen
Binta da kallo yayi sannan yayi kwafa ya juyo sai caraff suka hada idanu da zee, da sauri ta kauda kanta tana dan ta6e baki
"Daga zuwa sai cin abinci baka freshening up" inji ummy da tayi gaba jaye da hannun zee
"zanyi idan nagama, darabanil ju'i" yafada yana shafa cikinshi fuska a marairaice
"acici" inji ummy tana jan hannun zee suka nufi wajen Abbu
"muje mu raka Abbu kinji 'yata"
"to ni natafi, ma'asallama" inji Abbu
Fatan tsari Aymaan yayi mashi sannan suka fice gaba daya, Abbu a gaba ummy da zee abaya
Binsu da kallo yayi har suka fice sannan yadan daga kafadu
Batool ce tafito da kayan break wanda dama an fidda mashi nashi an ajiye incase idan yadawo
Zuwa tayi tana jerawa still fuskarta a kumbure
"tazo nan hutu ne?" inji Aymaan
"wa?"
"baquwar" ya amsa yana kallonta
Daga kafadu tayi tace
"kusan haka amma zata dan jima kadan"
Daga girarenshi yayi yace
"masha allah, kice mun qara yawa amma naga kamar bata magana, meyasa?"
"bari tadawo na tambayar maka ita"
Yiyayi kamar zai maketa tayi saurin ja baya da serving spoon a hannunta tana Dariya
Kwafa yayi kawai yajawo abincinshi yayi basmallah yafara ci
Acan waje kau har mota su ummy suka raka Abbu
Sallama sukayi da zee tana mashi fatan dawowa lafiya sannan ta juyo ta dawo ciki tabar ummy can tareda Abbu suna magana
Da sallama tasake Shigowa falon
Dago kai Aymaan da yanzu saura shikadai a falon yayi yana kallonta ya amsa
Kallonshi itama sukayi suka hada ido saita kauda kai
Stairs tanufa batareda ta yarda ta qara kallon gefenshi ba dukda yadda takejin idanunshi akanta
Binta da kallo yayi harta haye saman sannan yasake daga girarenshi biyu ya kada kai ya cigaba da cin abincinshi
A daki zee ta tararda batool Kwance tana waya cikin harshen larabci
Zama tayi gefen gadon tana sauraron batool din absentmindedly
Idanunta ne suka sauka akan Ring din yatsarta dake sheqi sanadin hasken rana dayayi reflecting akanshi ta window din bayanta
Qurama zoben idanu tayi tunanuka kala kala na kai kawo a kwalwarta
Yanzu Deen na ina? Me yakeyi? Yana tunawa da ita kau? Koko ya riga ya shafe babinta a tarihinshi? Yana cikin farinciki koko akasin haka?
Yana kewarta? Koko bayayi?
Ta yarda ta biyo Ummu batool nan ne don aganinta zata iya mancewa dashi with time, amma daga jiya zuwa yau tafara tantamar yiwuwar Hakan
Don duk motsin da zatayi saiya fadomata arai, duk blinking idanun da zatayi sai yayi mata gizo a idanu
Anya zata iya mantawa dashi? Anya?
She doubt it, tana tantama sosai akan haka, don Deen acikin zuciyarta yake, yariga yabi Jinin jikinta, mantawa dashi daidai yake da musanya zuciyarta da wata wanda babu Deen aciki kokuma musanya jininta da wani wanda babu shi a gudanuwarshi
Jitayi an dafa kafadarta Hakan yasa ta dawo daga duniyar tunanin data lula
Batool ce zaune kusada ita tana mata murmushi
Kamo hannunta batool tayi tana kallon zoben yatsarta itama
"shi yabaki?" inji batool tana kallon Ring din
Dago idanunta zee tayi ta kalleta batareda tace komai ba
Itama batool ta dago tana kallonta sai tadanyi murmushi
"yanada kyau sosai" tafada tana dan Kada kai
Nan ma batace komai ba
"sister, wani lokacin you have to let go abinda kake matuqar so sosai, ba wai don son ranka ba sai don Hakan shi zai fiyemaka alhairi.
Wani sa'in abubbuwa masu kyau basu cika zama masu amfani ba, misali wannan zoben dake hannunki
Kina Ajiyarshi ne bayan kinsan bazai amfaneki da komai ba Saima ya jefaki a wani hali idan kika kalleshi, why not ki cireshi tunda kema sanin kanki ne be cancanci zama a yatsarkiba yanzu"
Dan murmushi zee dake kallonta Tundazu tayi saikuma ta maida kallonta akan zoben
"a tunaninki cireshin zai sauya wani abin ne?"
Saita girgiza kai
"babu abinda zai chanza, babu.
Rashin shi ne ma zai jawo wani abin"
Kallon zoben tasakeyi
"idan na kalli Ring din sai natuna da ranar, ranar dayake gabana, zube a gwiyagunshi begging me to marry him.
The love, affection, seriousness dana gani a qwayar idanunshi a ranar yana sani tantamar abinda nagani a takardar da yabani, yana sani tunanin anya shi ya rubuta takardar, da hannunshi?
But sadly shine, shine, dalili kuma shine ban sani ba, abinda yafi komai tsayamin arai kenan.
Meyasa zai tafi batareda gayamin atleast dalili qwara daya ba? Meyasa?
Atleast yafada min Koda kuwa zuciyata ce zata buga, Koda qarya zaiyi min yayimin amma bawai yatafi hakannan ba, leaving me like a lost cat in the jungle"
Batasan hawaye takeyi ba Saida batool ta jawo ta ajikinta tana share mata su
"it ok zee, nasan yadda kikeji.."
"baki saniba batool, kuma bazaki ta6a sani ba sai idan kin tsinci kanki a wannan halin, nikuma bana maki fatan haka"
Qara rungumeta sidely batool tayi sannan tace
"ki gayamin, ki gayamin tarihin soyayyarku"
Girgiza kai zee tayi
"A'a, nima da nasan abinda zanyi inmanta da tuni nayi Hakan"
"unfortunately baki sani ba, amma kuma idan kikayi sharing dinshi da wani zakiji sauqi.
Tunda abin yafaru kin ta6a zaunar da wani kinyi pouring out abinda ke a zuciyar ki?"
Ahankali zee ta girgiza kanta
"you see? Fadama wani damuwarka ma yana rage damuwa.
Problem shared is Problem solved.
Idan kin fadamin zaki samu abu daya zuwa biyu
Nafarko zuciyarki zata rage nauyi saboda kinyi pouring out abinda ke cinkushe a cikinta wanda ke hanaki saqat
Na biyu kuma, who knows wataqila ina iya hango maki wani abu a soyayyar taku ko kuma na sama muku solution, bawai don am perfect ba saidon kowa da irin nashi baiwar da hangen"
Murmushi mai ciwo zee tayi tace
"zan fadamiki saboda dalili na farko da kika fada, wato don naji sauqin abinda nakeji a zuciyata
Amma batun samun solution ba be tasoba, sai idan akwai Problem ake samun solution, anan babu wani Problem idan ma akwai to bansaniba, tayaya za'a samu solution din?"
Ajiyar zuciya batool tayi tace
"to shikenan, ki fadamin din, am all ears"
Itama zee Ajiyar zuciya ta sauke sannan ahankali ta maida kallonta akan zoben hannunta
"Sunanshi DEEN... KAMALDEEN MUHAMMAD...."
****
Ummy ce tashigo falon bayan taga tafiyar Abbu
A dining din ta iske Aymaan yanata aika abincinshi hankali kwance
Qarasowa wajenshi tayi taja kujera itama ta zauna
"Likita bokan turai" inji ummy cikin tsokana
Murmushi yayi sannan ya dauki glass cup din gabanshi yayi sipping ruwa
"Umminmu! Ashe jiya zaki dawo da nasani da banje aiki ba"
Harara ta gallamashi
"kamar duka kenan"
Dariya yayi
"Allah ummy jiya munshiga busy sosai, surgery hudu nayi da daddaren nan"
Girgiza kai Ummy tayi
"Allah sarki, ai mata na shan wuya, haihuwa yaqin mata, allah yasa kowacce tagamata lfy"
Sipping ruwa yasake yi sannan ya amsa da amin
"kaga qanwarka ko?" inji ummy tana kallonshi
"baquwa?"
Harararshi tasakeyi
"sunanta kenan?"
"I don’t know her name ai"
"shame on you, ace bakasan sunan cousin dinka ba"
Sosa kai yayi yana dan 6ata fuska
"kai ummy"
"to ai Gaskiya ce, to sunanta Zainab"
"oh kinga kina fadi na tuna, ai na santa lokacin danaje Nigeria last ai naganta lokacin yar qarama ce nasan bazata wuce 15 ba kuma she's a talkative tana magana sosai gashi batajin magana amma yanzu ta chanza sosai, naga ko magana batayi, ko haka girman yazo mata?"
Murmushi ummy tayi
"eh to, kasan ana qara girma ana qara nutsuwa, tabbas ta nutsu Saidai wannan nutsuwar haka bata lafiya bace don kamar yadda kace magana ma wuya take mata gata always moody"
Ajiye spoon din hannunshi yayi
"to meya faru? Meya maidata haka to?"
Ajiyar zuciya ummy tasakeyi tace
"she's heartbroken"
"heartbroken?" inji Aymaan yana kafe maman tashi da hazal eyes dinshi
"yes, wanda takeso ne ya yaudareta, kwanan nan ba kaji muna maganar introduction daza'ayi a Nigeria ba?"
"yes, naji kuna discussing dinshi da Abbu"
"to itace, yaron asalinshi dan talakawa ne don koko da qosai suke saidawa for living
Sun hadu da Zainab dinne a school and they both fell in love
Amma da maganar tazo wajen daddy saiyaqi yarda saboda yaron ba Dan masu hali bane plus yana gudun ace ba sonta ba yake kawai yaudararta yake yana sonta saboda kudin da mahaifinta kedashi
Daddy yayi iya qoqarinshi don ya rabasu amma a banza don she's deeply in love with the guy don a sanadin haka ta kamu da hawan jini saboda damuwa.
Ganin babu sarki sai allah yasa kawai ya yarda yakuma cema yaron ya turo magabatanshi suzo ayi introduction idan dagaske yake.
Lafiya lau aka fidda ranar introduction din har ya bugomin nan munata murna
Saidai ranar da aka fidda don yin introduction din babu yaron babu magabatan nashi babu alamunsu.
An jira anjira shiru gashi wayar yaron bata shiga
Ganin Hakan yasa daddy aika drivernshi don ganowa ko lfy?
Wai dayaje saiya iske gida garqame da kwado
Aranar dai Saidai aka watse ba'ayi introduction din ba
Washegari shiru, babu su babu alamar su
Hankalin Zainab ya tashi don tana sonshi Sosai fiyeda tunaninka
Ganin ta tashi hankalinta yasa daddy shiryawa washegari yaje yagano da kanshi and the same story ya tarar still gidan kulle
Zainab dai taqi yarda ta nuna tanaso taje tagani da kanta
Koda sukaje din saita tarar da abinda suka tarar suma, suna ahaka wani abokin yaron yazo wajen da shar6e6iyar envelope wai gashi inji yaron da sukaje nema
And could you believe what she saw inside?
Letter ne ya rubuta yana magangganu marassa kan gado wai he's gone wai tayi haquri wai he's gone forever"
"what? But why?" inji Aymaan
Watsa hannuwa ummy tayi
"oho, beyi stating dalili qwara daya ba nayin Hakan, kawai wai he's gone.
Anan take tayi collapsing a wajen daga nan aka kwasheta sai hospital
Saida tayi kwana uku kafin ta farfado, blood pressure dinta yayi high ga difficulty in breathing.
Dakyar aka shawo kanta a kwana na uku ta farfado kuma daga ranar takoma haka, babu uhm babu uhm uhm, yanzu ma fa wai da dan sauqi ne ma tunda idan akayi magana tana amsawa da kau bata magana Saidai tayi smiling painfully.
Ganin Hakan yasa kawai na yanke shawarar tahowa daita nan don am very sure zatafi saurin healing nan bisa ga can, don ko babu komai ta chanza environment. Shiyasa kaga na taho daita har lokacin da zata warware kamar babu abinda yafaru"
Sosai jikin Aymaan yayi sanyi, nan take yaji abincin gabanshi ya fita ranshi
"so sad" yafada ahankali
"very sad indeed wlh, donma kamar yadda nafada maka ta dan warware da lokacin danaje Nigeriar ne da sai kayimata qwalla"
Wani zafi Aymaan yaji ya ziyarci zuciyarshi nan take yaji ya tsani koma waye wannan mayaudarin
"amma wannan ya cika butulu wanda besan alhairi ba, ko babu komai ko don soyayyar Gaskiya data nunamashi be kamata ya badamata qasa a idoba"
"hmm ai kai kasan da Hakan shi besaniba"
Shiru yayi ya cigaba da huci, yana jin ranshi na 6aci sosai
"shiyasa nazo daita nan don tasamu sallama, Aymaan wannan aikin tareda ku zamuyishi, help her, help her forget her past, mu Hade qarfi wajen ganin mun mantar daita past dinta, tayi moving on kamar babu abinda yafaru"
Dagowa Aymaan yayi ya kalli ummy
"yes ummy, we'll do everything, everything wajen ganin mun mantar da ita past dinta, I assure you, insha allah zata yi farinciki fiyeda da"
Murmushi ummy tayi cikin jindadi
"barakallahu fika Aymaan, allah yayi muku albarka gabadaya, idan kukayimin haka kun biyani wlh"
Wani qayattacen murmushi Aymaan yayi yace
"karki damu ummy, wataqila dama basu daceba, wataqila ba alhairi bane agareta shiyasa allah ya kawar dashi, insha allah zata samu wanda ya dace daita, insha allah zatace gwara da akayi hakan, shikuma zaiyi nadama har qarshen rayuwarshi"
Murmushi jindadi ummy tasakeyi
"Alhamdullilah! Allah yasa Hakan Aymaan, allah ya tabbatar mana da alhairinsa"
Da amin Aymaan ya amsa yana daukar ruwan gabanshi yakai baki
"bari naje sama ok? Kayi sauri ka qarasa abincin karya huce" tafada cikin yanayin farinciki
Kadamata kai yayi kawai yasake jawo abincin gabanshi
Ganin Hakan yasa ummy wucewa tana jin wani madaukakin farinciki a ranta, tabbas da alamu haqanta zai cimma ruwa, taga alamun abinda takeso zai faru, idan kau Hakan yafaru sai tafi kowa murna a duniya.
Aymaan kau tana wucewa ya ture abincin gabanshi ya koma ya jingina da kujerar bayanshi ya harde hannayenshi a qirji
Fuskarta tayi mashi gizo a idanu, yes! She's in pain, yaga Hakan a fuskarta, to amma wane asarrare ne marar hankali da zai rasa wanda zaiyi hurting sai damsel irin wannan
Wani kayattacen murmushi ya su6uce mashi
Lallai, to koma waye yayi sakaci, sakacin dazai qare rayuwarshi yana cizon yatsa, har qarshen rayuwarshi, he'll make sure he did that.... ✍️
_wasa farin girki🤸🏻♀️_
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:39 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*056*
*KADDARAR SO ❤️*
Kuka sosai Batool keyi lokacin da zee takai aya a labarin soyayyarsu da Deen datake bata
Jawota tayi jikinta suka rungume juna suna cigaba da kukan atare.
Sun dan jima ahakan sannan sukayi breaking hug din
"Am sorry" inji batool tana kallon zee idanunta jiqe da hawaye
Girgiza kai zee tayi tace
"Don't be"
"labarinku is so touching, rabuwarku is so disheartening" inji batool
Kada kai kawai zee ta iya yi tana share hawayenta da bayan hannu
"Inaji ajikina ba laifinshi bane zee, inajin koma menene ba da son ranshi ba ya barki"
Dan murmushi zee kawai tayi tace
"nima Hakan nake tunani don na yarda da soyayyarshi agareni amma koma menene yakamata ya gayamin, who knows muna iya working together musama ma kanmu mafita, koma menene be kamata ya karya alqawurranshi da yayi min ba"
Kada kai batool tayi tace
"Kiyi hqr zee, nasan duk inda yake shima yana can yana kewarki kamar yadda kike kewarshi"
Girgiza kai zee tasake yi
"I don’t miss him, I miss who I thought he is"
"kibar fadin haka zee, insha allah watarana qaddarar data rabaku zata qara hadaku and at that time zai fayyacemiki komai"
"babu qaddarar dazata sake hadamu batool, mun riga mun gama da juna a duniyar nan, shi yana Nigeria ni ina nan, bazan koma Nigeria ba kamar yadda shima bazai ta6a zuwa nanba, tell me, tayaya qaddarar zata hadamu"
"zee kenan, qaddara ta wuce tunaninki musanmman qaddarar so, you dont know what allah have in stock for you dahar ya rabaku, wataqila ba alhairi bane agareki ko kuma akwai wata manufa akan Hakan"
Daga kafadu kawai zee tayi tace
"mubar maganar haka, atleast na danji sauqin zuciyata danayi sharing damuwata, nagode"
Murmushi batool tayi
"never mind, amma idan bazaki damu ba zan dan nemi alfarma awajenki"
Komawa Zee tayi ta jingina da frame din gadon tace
"Inaji"
"please idan kinada picture din gayen ki gwada min inason ganinshi"
Shiru zee tayi
"please.." inji batool pleadingly
Dan murmushi tayi sannan ta nuna mata wayarta dake kan mirror
Da sauri batool ta tashi ta dauko wayar ta miqa mata
Girgiza mata kai tayi tayimata nuni da ta bude
Swiping wayar kawai tayi ta bude don dama ita bata sakawa waya security
"ki shiga gallery"
Yin yadda tace tayi
"shiga folder mai suna DEEN"
dubawa tayi saita ga folder saita danna ya bude
Hotuna tagani masu yawa duk sun bubbude
Na farkon ta danna nan take smiling face din Deen ya mammaye screen din wayar
Dan Wara idanu batool tayi tana gasping
"woooow!" tafada ahankali tana qarema fuskarshi kallo
Itadai zee mayar da idanunta tayi ta rufe kawai tana sauraronta
Wuce hoton na farko tayi na biyun ya bayyana nanma Saida tayi gasping
Haka taita bin hotunan daya bayan daya wanda duk hotunan fuskarnan dauke take da wannan murmushin nashi mai tafiya da zuciyar mutane kuma ga dukkan Alamu ma babu hoton da aka dauka da saninshi, wani Wurin yana magana ne, wani Wurin idanunshi nakan littafin dake hannunshi, babu wanda yafi burgeta sai wanda akayi mashi yana dauke da sultan suna Dariya.
Saida tagama going through duka sannan ta dago ta kalli zee da haryanzu idanunta ke a lumshe
"wow sis, Gaskiya guy dinnan ya hadu, dole rashinshi yasa ki shiga hali" inji batool cikin santi
Bude idanunta zee tayi ta gallamata wata muguwar harara sannan ta maida idanunta ta rufe
Dariya batool tayi tace
"Allah kau karki ji wasa sis, wannan na sameshi ai tusashi gaba zanyi ina kallo inajin dadi, ko laifi yayi min dana kalli fuskarshi zan huce, wayyo allah amma ya hadu dama ana samun ire iren hot guys dinnan a Nigeria?"
Banza zee tayi ta kyaleta kawai
"wayyo, aikau Ahmed nafasa sonka, Nigeria zani! Wayyo hot Nigerian guys inanan tafe"
Dan murmushi ya su6uce ma zee, sosai shirmen batool ke bata Dariya, haka taita sauraronta tayita zuba ita kadai ko gajiya batayi.
*AYMAAN*
Aymaan kau da maganar zee ya yini ya kwana ya kuma tashi
Sosai