Showing 288001 words to 291000 words out of 322641 words

Chapter 97 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6134

Kuma idan basu isheka ba kayi magana su qaromaka don suna iya baka ko nawa ne don ka kyalemasu diyarsu"

tana kaiwa nan tajuya tashige daki tarufo tana hawaye

kasa ko kwakwarar motsi Deen yayi awajen

sosai zuciyarshi taqara dagulewa yarasa abinda kemashi dadi

yana nan tsaye aka fara kiraye kirayen magrib

cikin mutuwar jiki yajuya yanufi kitchen dinsu ya ajiye siyayyar dayayi sannan yafito yawuce wajen bokitan ruwansu batareda yako kalli gefen kudadden dake kan tabarma har lokacin

ciccika butocinsu yayi daruwa yayi alwalla sannan yadawo kofar dakin kaka

turawa yayi yaji gamm hakan yasashi sanin rufewa rtayi daga ciki


cikin kwantar da murya yace
"kaka don allah kiyi hqr kitaso kiyi alwalla lokacin sallah yayi"

banza tayi dashi ta kyale

"kinji kaka?"

nanma shiru

jiyayi an kabbara sallah hakan yasashi cewa
"kaka zantafi masallaci don allah kifito kiyi alwallar ga ruwan can nazuba"

banza tayi nan ma ta kyaleshi hakan yasashi juyawa Kawai yatafi zuciyarshi a quntacce


koda yadawo daga sallar sai yaga alamun tafito tayi alwalla din don butarta ma babu ruwa hakan yasashi sake nufar kofarta saidai har lokacin a kulle take


haka yatsaya yayta bubbuga yana bata haquri akan tabude amma tayi banza dashi har lokacin isha'i tayi

dole ya haqura yaje ya chanzo alwalla yasake fita sallah

koda yadawo ma,bata budeba haka yasha bubbugarshi yagaji ya haqura yaje ya kwashe kudadden dasu daddy suka bari zuciyarshi na quna yashiga dakinshi

daidai nan yaji wayarshi dake gefen katifa na ringing

saida yafara adana kudadden sannan yazo ya dauki wayar yaduba lokacin harta tsinke

ganin sunan zee yayi Kuma har 3missed calls

sauke ajiyar zuciya yayi sannan yakashe wayar gabadaya ya ajiyeta


ranar sosai kaka tayi fushi dashi don qin bude dakinta tayi tana jinshi yana didimarshi shikadai a tsakar gidan taqi fitowa

shi yayi tatar qullin koko ranar ya daka barkonon duk tana jinshi taqi fitowa dukda yadda takejin kamar tafito ta tayashi din don tasan dole aikin yayimashi yawa


aranar dai haka kowannensu ya kwanta rai babu dadi




Washegari tunda yadawo daga sallar asuba yashiga kiciniyar dora koko


saida yafara hura wuta ya dora ruwa sannan yaje yafara surfen waken qosai

kaka na daki tana jinshi amma bata fito ba don har lokacin tana cikeda baqincikin abinda su daddy sukazo sukayimata jiya

tana jinshi harya gama yazo bakin dakinta ya kwankwasa

shiru tayi batace komai ba saiya sake kwankwasawa yace
"ina kwana kaka"

nan ma shiru

yasan tana jinshi hakan yasashi cewa
"kaka zantafi kai markade"

nan ma shiru

hakan yasashi tashi zai juya yaji muryarta qasa qasa tana cewa
"kasa rigar sanyinka"

kallon kofar yayi yadanyi murmushi sannan yace
"to kaka"

komawa yayi daki yasanyo rigar sanyin dukda bawani iska akeyiba yadawo yasake mata sallama sannan yatafi


be dade ba sosai yadawo da markaden lokacin har gari yafara haske

ganin kaka agaban murhu tana hura wutar kosai yasashi jindadi sosai


zuwa yayi ya ajiye markaden yazo zai tayata hura wutar saita tashi tabar mashi murhun fuska atamke tawuce tadauki markaden

be damuba ya cigaba da hura wutar itakuma tashiga hada kullin kosan


haka sukaita aiki ba uhm ba uhm uhm kamar kurame

da taimakon Deen suka sheqa kokon lokacin har yan saye sunfara shigowa


ahaka suka shiga sallaman customers dinsu inda kaka ke gaban kaskon qosai shikuma Deen ke sallaman masu saye


zuwa 10 saura sungama tsaff sun gyara gidan, har lokacin kaka taqi sakarmashi fuska

ahaka suma sukayi kalaci sukayi wanka

ganin Deen beda niyyar shiryawa yatafi school yasata kallonshi fuska adaure tace
"Makarantar fa?"

"kaka yau bazani ba"

"dalili?"

turo baki yayi
"nidai bazan iya fita kina fushi daniba"

harara ta gallamashi

"zakaje ka shirya ka wuce koko?"

qara narkewa yayi yace
"kaka wlh konaje bazan iya komai ba, don allah kiyi hqr kibar fushi dani"

"ni fushi nace inayi dakai? Kawai kaje kaitayi tunda nidai baka ganina da mutunci kaje kayi duk abinda kakeso, babu ruwana"

"haba kaka, wlh bakiji yadda nakejiba idan kina fadin haka, duk duniya wa nakedashi bayan ke? ke kadai zaki sani nayi ki hanani nabari don allah kibar fadin haka" yafada kamar zaiyi kuka

"Kuma shine nace ka rabu daita kaqiya? duk abinda nake gudanmana kenan ai, don yimin yarinyarnan tayimin don alamu sun nuna tanada hankali amma ai ba anan take ba, yanayinmu dasu ba daya bane kuma bazai ta6a zama daya ba, mu dasu mabanbantan mutanene masu mabanbantan rayuwa wanda hadawarmu abune mai matuqar wuya"

"kiyi hqr kaka, wlh nima bansan abin yakai haka ba amma insha allah zan kiyaye"

kauda kai Kawai tayi batace komai ba

"kinji don allah kaka?" yafada cikin marairaicewa

"to indai kanason mu shirya dakai kafita harkar wannan yarinyar, iyayenta ba mutanen arziqi bane ka kyalemasu diyarsu suyita kaya allah zai baka wacce tafita, kadai jini ko?"

"to kaka"

"bawai to a iya fatar baki Kawai, a aikace nakeso don ko a Makaranta ban yarda ku haduba"

"to kaka, insha allah hakan za'ayi" inji Deen in,affirmation dukda yasan wannan abun abune mai matuqar wahala


"kudaddensu fa ya kayi dasu?" inji kaka


"na adana, zan maidamasu kayansu"

"dadai yafi" inji kaka tana ta6e baki


"yanzu katashi kashirya kawuce Makarantar don bawai bari zanyi kayi qalula ba"

murmushi Kawai Deen yayi yatashi yashige dakinshi tabishi da kallo cikeda qauna da tausayawa



Ranar dayaje school be ganta ba Kuma yasan hakan be rasa nasaba da daddy don yasan tsaff ya hanata zuwa kodon karsu hadu


haka ya yini a school din ranar cikin rashin kuzari, babu abinda yake mararin ji kamar muryarta, idan yatuna da sautin kukanta najiya saiyaji ranshi yaqara dagulewa


gashi ya manta wayarshi agida da babu abinda zai hanashi kiranta

yasan yayima kaka alqawarin fita harkarta amma shi kanshi yasan abune marar yiwuwa

bazai iya rabuwa da zee ba, bazai iya datse soyayyarsu ba don rabuwa daita daidai yake da rabuwa da farincikinshi gabadaya


haka yawuni a school din ranar batareda ya iya ta6uka komai ba har lokacin tafiya gida yayi yakoma gida rai duk badadi


koda yadawo gida da doqinshi yafada dakinshi don daukar wayarshi yakirata saidai yaga wayam be ganta ba

neman duniyar nan yayimata be ga ko abu mai kama daita ba


yana cikin haka ne kaka tashigo ta taddashi yana bincike bincikenshi hakan yasata hade rai tace

"wai meye haka kawani burkita daki kamar dakin mahaukata?"

yana dan yarfe gumin dayayi na neman dayake yace
"kaka wayata nake nema wlh, naduba koina,ban ganta ba"


"wayar allurace dazata 6ace harka burkita daki haka don nemanta? to tana wajena"

dagowa yayi ya kalleta yaga tawani qara hade rai tana kallonshi

"tana wajenki?"

"eh" tabashi amsa kai tsaye

"to.. amfani kike daita?"

"A'a Kawai daga yanzu nahanaka riqeta tunda ba dole bane riqe wayar" tafada tana cika tana batsewa


"amma.. meyasa" yafada ahankali

"shine nace saboda ba dole bace, aidai duk cikin masu kiranka nice mai muhinmmanci ko? to zan haqura koma menene saimun hadu sai nafadamaka amma yanzu dai bakai ba waya"


shiru Deen yayi rai babu dadi

"menene kawani sunkuyar dakai kamar wanda akayiwa rasuwa?"

ahankali ya girgiza kai
"A'a babu komai"

"to maza muje kaci abinci yau abinda kafiso nayimaka" tafada tana mashi murmushi don lightening dinshi

"to" yafada Kawai yayi hanyar waje rai babu dadi


a tabarmar dake waje ya zauna ya jinginar da kanshi yanajin zuciyarshi na d'aci

ahaka kaka takawo mashi abincin ta tusashi gaba tana bashi abaki tana mashi fira duk don farantamashi


shidai amsan abincin Kawai yake yana tauna yana hadiyewa badon dadi ba don gabadaya bemada appetite

sosai zuciyarshi ta dagule, yasan saboda zee kaka tadauke wayar wanda hakan ke nufin bazai qarajin muryarta ba

saidai wani bangaren zuciyarshi ta tausheshi kan yayi hqr idan tahanashi waya daita ai bazata hanashi haduwa daita a school ba

hakan yasashi jin dan sauki sauki yadan saki ranshi yana jin kamar yajawo gobe don doqin ganin zee



Washegari tunda wuri yaje school din

dukda bayada lecture ko daya haka yabuga safkon zuwa duk don yaganta saidai shiru

haka yaita gararanba cikin school din amma babu zee babu alamunta


shine har bayan la'asar school din amma ko mai kama daita be ganiba class dinsu kuwa yaje sau babu adadi amma babu ita, dole daga baya yaja qafaffunshi yabar school din rai adagule



wasa wasa saida sukayi sati batareda sun haduba ko sunyi waya

izuwa lokacin yagane tabar zuwa school ne don kullum haka zaije yaci zamanshi a school amma babu ita babu alamunta

ga kaka har lokacin taqi bashi wayarshi yakuma nema adakinta beganiba don ba qaramin 6oyo tayimata ba


cikin satin nan guda duk ya chanza kamar bashi ba, kallo daya zakamashi kasan yana cikin tsananin damuwa

kaka ma na lure da yanayinshi dukda qoqarin 6oyemata dayakeyi saidai babu yadda ta iya don ita aganinta hakan yafi gwara yarabu daita tun wuri kafin komai ya lallace, haka yasa taita iyakar qoqarinta wajen ganin tana yayemashi damuwa ta hanyar yimashi abubbuwan datasan yanaso saidai ko kadan hakan be taimakama yanayinshi ba don zuciyarshi tariga tayi nisa, batajin kira.



Ana haka watarana Deen yadawo daga school ya tadda gidan a kulle

ganin hakan yasashi wucewa gidan maqocinsu Mallam Nasiru don mafi yawanci idan zata fita nan take barin makulli

yaro yasa yashiga ya tambayomashi ko an bar makulli

can saiga matar Mallam Nasirun tafito dakanta tabashi makullin tace ai haihuwa kaka taje amsa qasan layinsu batama dade da tafiya ba


amsar makullin yayi yaimata godiya sannan yawuce yabude gida yashiga


direct dakinshi yashiga ya ajiye littatafanshi sannan yafada kan yar katifarshi


shiru yayi ya qurawa ceiling idanu can kamar wanda aka tsikara yamiqe zaune yana zare zaren idanu sai kuma yamiqe dasauri yafita yanufi dakin kaka.


bincike yafarayi adakin yana duba every possible place da kaka zata 6oyemashi waya


haka yaita bincike yana yi yana kallon kofa harwani hada zufa yakeyi, can dakyar yaganota can qasan kwallarta ta daddaneta da kaya

ajiyar zuciya ya sauke yana fiddota

qara kallon kofar yayi sannan yasamu wuri ya zauna gefen gadonta yana kunna wayar don akashe take


cikin sa'a kau takama dukda battery dinta yayi low sosai


shiga yayi call log yaga number ta ce asama don dama itace tayi kiran qarshe


qurawa number ido yayi nawani lokaci sannan yakai hannu da niyyar dannamata kira saidai kafin yayi hakan kiranta yashigo


tsayawa yayi yana kallon kiran yakasa dagawa harta katse

can saiga wani kiran

lumshe idanu yayi yanajin sanyi a zuciyarshi, dama yasani duk inda take tana cikin damuwa kamar shi kuma tana missing dinshi itama

akira na uku ya daga yakara a kunne

shiru yaji ba'ace komai ba hakan yasashi cewa
"Zainab.."


nan ma shiru

"hello Zainab?"


nanma shiru


"Zainab is this you? please say something" yafada cikin damuwa


"Deen..." yaji tafada cikin rawar murya saikuma sheshekar kukanta yabiyo baya


"Zainab are you crying? please kibari kinji kar zuciyata tabuga, am ok kinji?" yafada yanajin kamar shima yayi kukan


"Deen ina kashiga? nakusan mutuwa saboda fargaba, meya samu wayarka?" yaji tasake fada cikin kuka


"am ok zee, babu abinda yasameta Kawai babu charge ne" yafada cikin son kwantar mata da hankali

"no Deen you are not ok, gayamin meya faru? me daddy yayimaka?" tafada cikin kuka


"babu komai Zainab, babu abinda yayimin. I love you and I'll never back off, no.matter w..."



fittt... yaji anfige wayar hakan yasashi juyowa arazane


wara idanu yayi cikin faduwar gaba ganin kaka tsaye agabanshi da wayar hannunta

zaiyi magana yaga takara wayar a kunne yaci ta cigaba dacewa

"eh yana jinki, Mallama mekuma kike nema da jikana? mekuma yasaki nemanshi?"

shiru tayi saikuma tace
"eh nice, kaka ce nagodema allah dayasa kika gane hakan, meye kuma kike nemanshi bayan abinda kukaimashi eh?" tafada amasifance

"to ahir dinki wlh, karki qara kiran yarona wlh don shima yariga yagama dake, dama ai qarfin haline irin nashi banda haka ai ke ba kalar matar dazai aura bace"

"kaka.." inji Deen daya sandare atsaye tunda tafara


"menene? menene kake hanani magana? kabari nayimata wonin

kina jina? wlh kifita harkar jikana kina jina ko? muba,kowan kowa,bane,bamuda wadanda zasu tsayamana idan kika jefamu a chakwakiya. muna zaman zamanmu ne cikin rufin asiri da wadatar zuciya, muna zamanmu cikin farinciki don allah karki tarwatsa mana shi.don allah ki kyalemin yaro kije kema allah yahadaki da daidai ku masu kudi muma haka
mungode daduk dawainiyar dakukayi mana da qaunar dakuka gwadamana amma don allah karki sake nemanmu, ba don muba don allah"

daga haka ta katse wayar kitt tayi jifa daita kan gadonta

juyowa tayi afusace tana kallon Deen dake kallonta shima kamar wanda ruwa ya cinye ga idanunshi sunyi jajir

nunashi tayi da yatsa

"wato bakajin magana ta ko? ban isa nasaka kayi ba ko kuma ban isa na hanakaba ko? to shikenan ga wayar nan kadau abinka amma kasani kasake ka qara kiranta ko takiraka ka daga ban yafe ba kuma ban yafe ba idan kaje kuka hadu bare harka bude baki kayimata magana, kai ko ita tazo wajenka tayimaka magana ka amsa ban yafeba, shashasha Kawai!"

daga haka ta juya ta hankada labule tafice daga dakin afusace


binta da kallo yayi harta fice sannan yazame yazauna bisa gadonta ya dafe kanshi dake mugun saramashi da hannu bibbiyu....✍?





Ummin fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:45 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?*










*092*










Aranar Deen kasa walwala yayi kwata2, tunaninshi bewuce wane hali zee zata shiga ba bayan wayar dasukayi, haka Kawai yakejin duk inda take ba lfy.


haka ya qarashe wunin cikin tsananin damuwa

a bangaren kaka kau shareshi tayi dukda lura da halin dayake ciki datayi saidai batajin tana iya barin wannan al'amarin yacigaba da tafiya ahakan don tunfarkon kawo zancen zee taji abin be kwanta mata ba don bata qaunar abinda zai tarwatsa dan farincikinsu har yakai ga tonuwar babban sirrinta na shekara da shekaru



a daren ranar kasa barcin kirki yayi, washegari kuma tunda wuri yafice school ko yadanji sauqin abinda yakeji dukda yanzu school din yabar yimashi dadi saboda rashin zee acikinta

sosai yakejin kewarta kamar sunyi shekaru basu hadu ba

ranar haka ya yini a school din batareda yama fahimci lectures din daya dauka ba




bedawo gida ba sai bayan asr inda yauma kamar rannan ya tadda wata galleliyar mota a kofar gidansu


tsayawa yayi yana kallon motar abubbuwa da dama na kai kawo a zuciyarshi


can sai yanufi hanyar shiga gidan zuciyarshi fall saqe saqe


da sallama yashiga yana bin mutanen tsakar gidan da kallo kamar yaddasuma suka dago suna kallonshi


kaka ce zaune kan tabarma tana facing daddy da wannan mutumin dasuka zo tare rannan


amsa sallama duk sukayi suna kallonshi hakan yasashi qarasawa yana karantar yanayin fuskokinsu

gani yayi su daddy suna mashi kallon dayasha banban dana rannan don har murmushi yaga kamar daddyn namashi itakau kaka fuskarta babu yabo babu fallasa


qarasawa yayi gabansu ya russuna ya gaidasu cikin girmamawa suma suka amsa cikin kulawa

ganin zai tashi yasa daddy cewa
"A'a d'ana zauna ai dama maganar takace"

babu musu ya zauna yana satar kallon kaka dataqi kallonshi tundazu

wanda ke tare da daddy yace
"nasan kana mammakin meya dawo damu yau don nasan kaji labarin abinda yakawomu rannan ko?"


shiru Deen yayi kanshi aqasa hakan yasashi cigaba dacewa
"munzo bada hqr ne akan abinda yafaru rannan, agaskiya muma mun gane abinda mukayi samm be kyautu ba, munyi nazari munga sam bamu kyauta ba shiyasa mukazo baku hqr don muma ba ason ranmu mukayi hakan ba.
kunsan dai yadda duniyar ta lallace yanzu, masu gaskiya yan qalillan ne, yanzu a duniya saika rasa wanda zaka yarda dashi don gur6atattun suke 6ata nagarin shiyasa duk ake tsoron tsoro

abinda yasa daddy be yarda da zancenku ba kenan don yawanci mutane basuda gaskiya saisu nuna suna sonka don allah while a zuciyarsu ba haka bane. ba,komai alhaji ke gudu ba sai yaudara shiyasa Tunfarko beyi na'am da zancenku ba don Zainab itace diyarshi daya tilo bazaiso abinda zai cutar daita ba shiyasa Tunfarko yaqi amincewa amma yanzu yagano gaskiya, ya bincika yaga dagaske bazaka yaudareta ba shiyasa yajawoni muka sake dawowa don mubaku hqr akan abinda yafaru wancan karon, kuyi hqr sharrin zuciya ne kuma insha allah tunda yanzu ansamu fahimtar juna hakan bazai sake faruwa ba, don allah d'ana katayamu ba Baaba haquri"


tunda suka fara magana kan Deen naqasa yana sauraronsu bece komai ba harsuka kai aya

daddy ya dora da
"hakane son dik abinda yafada hakane, insha allah,yanzu komai ya daidaita tunda ansamu fahimtar juna, idanuna yaso yarufe nayi abinda zaijawo tarin danasani nan gaba amma alhamdulillah tunda yanzu komai ya daidaita nakuma fuskanci soyayyar gaskiya kukewa juna, fatanmu anan dai allah yasa kun huce yakuma sa hakan yafi alhairi"

nan ma kasa cewa komai Deen yayi don besan me zaice ba, ba zato yaji muryar kaka nacewa
"amin amin, shikenan komai yawuce allah ya kyauta gaba"

dagowa Deen yayi ya kalli kaka with surprise saiyaga har lokacin taqi kallon 6arinshi hakan yasashi sunkuyar dakai yanajin wani sanyi na ratsa qasan zuciyarshi, kenan kaka ta yarda daddy ma ya yarda, this is unbelievable!


cikin jindadi suma su daddy suka shiga amsawa da amin

nan suka sanardasu Deen halinda zee keciki cewar yanzu haka tana kwance asibiti

sosai hankalin Deen yatashi dajin wannan labarin har hakan ya bayyana a fuskarshi

nan suka nemi alfarmar Deen yabisu asibitin qila zuwan nashi ya taimakama yanayinta


Deen yayi tunanin kaka zata hana sai gani yayi ta amince da hakan hakan yasa yashiga farinciki sosai saidai saida suka maidamasu kudaddensu wanda suka kawo rannan wanda dafarko su daddy sunso qin amsa amma ganin sun nace yasa suka amsa badon sunso ba

babu 6ata lokaci Deen ya kimtsa suka wuce taredasu daddy asibitin da aka kwantar daita


anan sukaje asibitin har komai yakoma daidai har takai ga tasamu sauqi an sallameta har daga baya daddy ya bijiro da maganar Introduction (all in book 1)



Sosai batun Introduction din yaba deen mammaki don beyi expecting hakan ba a lokacin

a tunaninshi sai sungama school sannan za'a fara maganar amma sadda zee tayimashi bayanin wai so ake atsaida maganar ne kawai bawai auren za'ayi ba yasa hankalinshi yadan kwanta don soyake ya kasance kafin lokacin koyaya ne yasamu abinda zai iya riqe kanshi da zee


lokacin da zancen Introduction din ya iso ga kaka duk saita rasa kwanciyar hankali

dukda bata nunawa Deen komai ba amma deep down abin na cinta


nan take ta gano manufar su daddy akan wannan Introduction din dasuka qirqira wanda bata raba dayan biyu suna sane sukayi hakan

dama wannan zuwan nasu da amincewarsu lokaci daya bawai shiganta yayi ba, tasan duk yadda za'ayi akwai maqalqashiya gameda hakan

jin batun Introduction din ya tabbatar da zarginta yakuma darsa fargabar tonuwar sirrinta data dade tana rufewa


sosai kaka tashiga damuwa komai ya kwance mata, kullum da tunani take kwana take tashi

bata fatan sirrinta ya fallasa a wannan lokacin, bata fatan abinda zai maidamata hannun agogo baya



duk halin datake ciki bata bari Deen yasani ba don batason kwata2 yasan da damuwarta yayinda a gefe guda tashiga nemama kanta mafita akan wannan hargitsatsen al'amarin dake shirin tunkarota



A bangaren Deen kau besan kaka nayi ba, shi duniya cema tadawo mashi sabuwa inda suke shan soyayyarsu da zee kamar zasu hadiyewa juna, kodayaushe suna maqale awaya don har lokacin batayi resuming school ba don bata,ida warwarewa ba

lokacin Introduction sai qara matsowa yake inda Deen kejin kamar yajawo ranar don doqi

dukda bawai auren za'a daura ba bakuma saka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login