Showing 207001 words to 210000 words out of 322641 words
Chapter 70 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
don baya yabasu
Sallamar Aysha ce yasashi Dagowa daga danne dannen dayake a waya ya juyo garesu
Kallo daya zakayimashi kasan shima balarabe ne don the same skin colour gareshi da Aysha Saidai baida kyau sosai, farinne kawai saikuma kyan fatarshi wanda da alamu harda hutun dayake ciki yabata gudunmawar glowing
Dama da murtukaken fuskarshi ya juyo amma ganin zee yasa yadanyi jimm yana kallonta cikin yanayin rashin fahimta sannan ya kalli Aysha cikin son qarin bayani
Cikin fara'a Aysha tafara gabatar da zee da itama ta Hade rai cikin larabci sannan ta juyo ta kalli zee tace
"Ummie meet Umar, my love"
Jitayi kamar ta kwadeta don haushi ganin yadda take wani rawar kafa wajen introducing din amma saita daure ta dago kai ta kalli wanda aka kira Umar na 2secs sannan ta kauda kai tana dan ta6e baki tayimashi sallama
Kamar bazai amsaba shima saiya amsa sama sama sannan ya maida hankalinshi kan Aysha kamar dama jira yake yafara yimata magana da larabci cikin fada fada
Tsayawa zee tayi tana kallon ikon allah don yamaqi tsayawa yaba Aysha din dake son yin magana damar yin maganar data fara saiya katseta yanayi yana watsa hannuwa kamar wani ubanta Hakan ba qaramin 6ata ran zee yayi ba dukda batasan me suke magana akai ba Amma ko don ita datake baquwa acikinsu kuma baquwar budurwar shi yaci ace yaji kunyar masifeta a gabanta Hakan yasata taka mashi burki a fusace
"Hey mr man! Meye haka? Zaka tusa mutane gaba kana masu ihu?" tafada cikin harshen turanci rai a 6ace
Dakatawa yayi ya tsaya yana kallonta kamar a mammakince sai shima a harshen turanci yace
"Me kika ce?"
"cewa nayi meyasa zaka tisa mutane a gaba da ihu? Waye diyarka anan, Is this also in your manners of speech"
Riqo hannunta zee taji anyi ta juyo taga Aysha ce idanunta fall hawaye
Haushi yaqara kamata ta fizge hannunta daga riqonta tana cewa
"dalla kyaleni, waye diyarshi? Waya haifa anan dazai tisamu agaba da ihu?!"
"who are you?" yafada yana jin zuciyarshi na qara 6aci
"kai ka cancanci wannan Tambayar, waye kai daxaka tisamu gaba da haushi!"
"Ummie!" inji Aysha da dan qarfi hawayenta na gangarowa
Matsawa baya tayi ganin tana niyyar riqomata hannu cikin 6acin rai tana cewa
"dalla karki ta6ani, kai waye dazaka tisata gaba kana mata masifa kamar ubanta? Haihuwarta kayi? Ko baiwarka ce? Zaka kwaso jiki kazo har school kasameta kacimata mutunci, did you even have conscience?"
Afusace yajuya kan Aysha yafara magana cikin larabci
Katseshi zee tayi da
"look, ba ita tayimaka ba ni nayi maka, ni zaka kalla kayiwa magana da yaren dazan gane ba ita ba!"
Juyowar yayi ya kalleta cikin turanci shima yace
"kinsan ko meke tsakaninmu zaki shiga tsakaninmu? Kinsan ko wanene ni?"
"waye kai banda wanda besan darajar mace ba, wanda be darajja soyayyar da akemishi, babu abinda ke tsakaninka daita sai mugunta kuma baka cancanci soyayyarta ba!"
"Zainab!" inji Aysha saikuma ta fashe da kuka
Cikin tsananin 6acin rai Umar yake nuna kanshi da yatsa
"ni.. Ni kike cewa haka?"
"eh kai, sai me?"
Juyawa yayi ya kalli Aysha dake kuka har lokacin yace
"infact, it's over!"
Ya juya Afusace zai bar wajen
"Umar!" Aysha tafada da qarfi tana yunqurin Binshi
Riqo hannunta zee tayi tana cewa
"let him go Aysha, so what?"
Fizge hannunta Aysha tayi daga riqonta itama a fusace tana cewa
"leave me alone!"
Sannan tajuya ta nufi Umar dahar yashiga mota ya rufo kofar
Kwankwasa glass din gefen shi Aysha take tana cewa ya bude mata cikin kuka amma ko kallonta beyi ba ya tada motar yaja da qarfi ba don zee ta fizgo Aysha ba da saiya bigeta
"Umar!!" tasake kiran sunanshi tana kallon motarshi data nufi gate aguje
Binshi tasoyi sai taji takasa yin gaba saboda an riqeta
Juyowa tayi taga zee ce riqe da ita Hakan yasa ta fizge jikinta daga riqonta
"take your hands off me!"
Qara matsowa zee tayi tana qoqarin yimata magana saita daga mata hannu
"stay away From me!"
Saita juya ta nufi hanyar fita daga school din itama
Binta da kallo zee tayi tana jin zuciyarta na suya
And on her very eyes her only link to Deen's problem is gone... ✍️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:41 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*065*
*THE GIRL*
Iya dagulewa ran zee ya dagule, tsayawa tayi tana kallon hanyar da Aysha tabi ta fita cikin dacin rai
Juyowa tayi taga har few mutane sundan taru suna kallon abinda yafaru
Janye idanunta tayi daga kansu ta wuce cikin school din feeling very bitter
Har aka tashi daga school din ranar ran zee na a dagule gashi bata qara ganin ko wulgin Aysha ba a school din
Drivern da Aymaan ya samomata yazo wanda shi ke maidota gida don mostly Aymaan dama ke kawota school din
Shiga motar tayi suka bar school din cike da dacin rai.
****
"wow, this is crazy! Kodai asiri yayi mata?" inji batool tana kallon zee da haryanzu fuskarta ke a dagule
"ba asiri bane, kawai tsantsar soyayya ce, tana sonshi ne over"
"kutt... Wallahi ba'ayi namijin dazai juyani tun ina gidanmu ba, wannan ai idan tashiga gidanshi tashiga uku, tun yanzu yana mata iko kamar ubanta ina ga tashiga gidan nashi yasan ya mallaketa?"
"abinda nake gwadamata kenan taqi fahimta, you have to see yadda yakeyi mata, ko babu komai ai kasancewata a wajen yakamata ya ragamata amma kinga yadda yake mata? Not minding who and who is watching?"
"irinsu ne zakiga ko bayan auren ne basajin komai su duzgata agaban mutane, sai kiga mutunci ya zube hatta abokanshi ma sunsan batada wata daraja awajen shi"
Ajiyar zuciya zee kawai tayi batace komai ba
Tunani take ace misali Deen ne Hakan, Deen ne keyimata Hakan, zata iya jurewa, kai da kamar wuya, duk son datake mashi bazata iya jurar wulaqanci daga wajenshi ba Saidai son ya kasheta
"yanzu meye mafita? Gashi kince ta tafi cikin fushi, idan tayi deciding ta rabu dake fa? Ya kenan?"
Shiru zee tayi bata amsa ba sai kafe waje daya datayi da idanu
"kema da kin kyaleta kawai, gashi yanzu Hakan na neman ta6a friendship dinku wanda wargazewar abotarku daidai yake da wargazewar shirinmu, gashi dama bamu samu abinda mukeso ba har yanzu"
"ni ba damuwa ta wargazewar abotar mu ba, damuwata halin dazata tsinci kanta aciki, yanzu da nan gaba
Batool, yes nafara abota da Aysha saboda wani dalili nawa na kaina amma yanzu ina jinta a raina fiyeda yadda ya kamata na jita
Bana regretting abinda nayi don shine daidai
Koda abotar tamu zata watse bazan damuba kamar yadda zan damu idan Aysha tayi ending up da Umar a matsayin miji
Kwata2 they dont make a match
Aisha is very cool, kamar Deen.
Batada hayaniya, very jovial and timid.
While Umar masiffafene na gidan gaba gashi he doesn't have regard to her feelings, yanzu yana mata Haka yana mata masifa kamar zai rufeta da duka wa keda tabbacin idan sukayi aure bazai dinga dukanta ba? Kwata2 Aysha ba match din Umar bane"
Ajiyar zuciya batool tayi tace
"to ya zakiyi? Idan allah ya qaddara shine mijinta fa? Ya zakiyi? Ya zatayi?"
"insha allah bashi bane ba ma, insha allah mijinta na nan tafe, very nice and kind person wanda zai sata farinciki akoda yaushe, insha allah..."
Har dare Aysha na maqale a ran zee, tunani takeyi ko a wanne hali take ciki yanzu
Qila ma tana can tanata kiran wayar shi baya dagawa kokuma tana mashi text upon text kamar yadda tace tana mashi idan suka 6ata
Wayarta tajawo tashiga number Aysha din tashiga rubuta mata short text message
_*wani lokacin abinda zuciya keso baya zama alhairi ga mutum.. Wani sa'in you have to let go what your heart crave for saboda ba alhairi bane a gareta*_
_*No guy is worth your tears and when you find one that is, he won’t make you cry*_
_*ki roqi allah yayimiki za6i na alhairi, karki roqeshi akan lallai sai za6inki zai mallaka miki*_
Turamata tayi sannan ta tura wayarta qarqashin pillow ta kwanta ta lumshe idanunta trying to catch some sleep
Ta jima tana saqa da warwara sannan barcin yayi nasarar dauketa.
Washegari haka zee taje school da yaqinin ganin Aysha suyi magana Saidai har suka tashi daga school din bataga ko mai kama daita ba, takira number ta ma bata shiga, haka ta haqura tana jin ranta babu dadi
Wasa wasa Saida sukayi kwana uku basu hadu da juna ba tun zee na damuwa tana kiran wayarta da bata shiga always harta haqura ta qyaleta kawai
A cikon kwana biyar da yin abin watarana zee na zaune cikin class tana duba wani Littafi taji an dafata a kafada
Ga mammakinta tana Dagowa sai idanunta sukaci karo da Aysha
Tsayawa tayi tana Binta da kallon mammaki don bata ta6a expecting itace ba
Harara Aysha ta gallamata sannan tace
"Wurin zaman ma baza'a bani ba?"
Dan murmushi zee tayi saita matsamata cikin tsokana tana cewa
"Wata sabon gani, yan yaji an dawo"
Hararar wasa Aysha tayimata tana zama tace
"kuda kukaqi zuwa biko"
Dariya zee tayi tace
"biko na nawa, a school dinnan babu inda ban shiga ba da sunan nemanki, shikenan daga samun dan misunderstanding kinyi cutting off dani ko wayarki bana samu"
Murmushi Aysha tayi tace
"ba Haka bane, dubeni kiga, bakiga na chanza ba?"
Sai a lokacin zee ta tsaya ta kalleta dakyau sai taga tadan rame tayi pale
"ya sallam, meya sameki? Naga kamar kin rame"
Murmushi Aysha tayi tace
"ba kama bane, na rame. Yanzu haka ma da sauqi. Tun ranar da muka rabu nake rashin lfy"
Wara idanu zee tayi saikuma tayi alamun fuskar tausayi
"meya sameki? Kuma shine ko Kiyi informing dina?"
Murmushi Aysha tadan sakeyi sannan tace
"ni tun washegarin ranar ban qara sanin inda wayata ba take sai jiya, tayaya zanyi informing dinki to?"
"to meya sameki?"
Murmushi kawai Aysha tayi
Dan Wara idanu zee tayi tace
"badai saboda abinda yafaru ba?"
Dan murmushi tasakeyi tace
"it doesn't worth it, right?"
"tell me its not because of it" inji zee tana kallonta
Wani murmushin taqara yi sannan tace
"sadly, it is"
Shiru zee tayi tana kallonta not knowing what to say
"Zainab, in gayamaki wani abu?"
Kada mata kai tayi still looking at her
"tunda nake ban ta6a yarda da wata ba ko inji mutum ya mugun kwantamin kamar ke ba, saina dinga jin kamar na dade da sanin ki, sai na dinga jin kamar akwai wani bond daya hadamu tare da daddewa tunma kafin haduwarmu"
Shiru zee tayi still looking at her batareda tace komai ba
"shiyasa naji bana iya rabuwa dake dukda abinda kika yimin yakai na rabu dake din don da wata ce I won't have anything to do with her anymore, a dalilin abinda kikayi nayi rashin lafiyar kwana uku"
Zee dai har lokacin bata ce komai ba kuma bata daina kallonta ba
"Zainab kowa da irin jarabtar da allah yayimishi, ni tawa kenan.
Kowa sai yace Umar baya sona while ni nasan yana sona
Everyone was against soyayyarmu, yayana, ummie na dukda dai bata nunawa fili but itama batason relationship dinmu and now you.
Hakan yaci ace na haqura ko?
Amma nakasa, I love Umar fiyeda tunanin kowa, nima bansan yaya akayi ba kawai I know I can't live without him kuma na gasgata Hakan a kwanan nan
Can you believe don Umar yace it's over na kwanta rashin lafiya harda qarin ruwa?
Wannan yaci ya nuna muku ba laifina bane, it's my heart's"
"Aysha, nasani. It's hard to forget someone you love musanmman first love
Nima I was once in your shoe, infact am still there
Amma mine is totally different From yours
Nawa yana sona, a zuciya akuma aikace
Yana gudun 6acin raina, yana son farincikina, baya iya fushi dani, baya iya hurting feelings dina amma naki fa? Ke kanki kinsan wannan abinda kukeyi ba soyayya bace, ke kanki kinsan ke kadai ke sonshi shi baya sonki"
"yana sona ummie, nina sani, kawai baya gwadawa ne"
"to meye amfanin soyayyar da ba'a gwadawa? Haka zakuyi ta yafiya Aysha, bazaki ta6a sanin dadin soyayya ba idan kuka cigaba da tafiya a Hakan, kuma juma'a mai kyau tun daga laraba ake ganeta, your marriage life depends on your love foundation"
Kada kai Aysha tayi sannan tace
"ki tayani da addu'a, naga message dinki na rannan and I decided zanyi yadda kikace, zan dinga addu'a allah ya za6amin mafi alhairi ko Umar ne ko bashi ba sa6anin da danake addu'ar allah ya mallakamin shi"
"Good, idan ma bashi bane ki roqi allah ya sassauta ko ya ciremaki sonshi gabadaya daga zuciyarki, komai mai yuwuwane a wajen allah, sai kiga abin yazama tarihi"
Kada kai Aysha tayi tana murmushi
"thanks, zanyi Hakan insha allah, nima bada son raina nake wasu abubbuwan ba Amma insha allah zan dage da addu'a, kema ki tayani"
Itama zee saita kadamata kai
"insha allah, ukhtie"
Murmushi sukayi atare
Buga tagumi Aysha tayi da hannu daya
"bani labari"
"labari? Labarin me?" inji zee
"labarin soyayyarki, daji zaiyi dadi naji kince he loves you so much beson ganin 6acin ranki"
Dan murmushi mai ciwo zee tayi ta maida hankalinta kan littafin gabanta
Dauke littafin Aysha tayi tace
"saifa kin gayamin, I love hearing love stories musanmman wanda akwai kulawa sosai aciki, tell me, waye very Lucky guy daya samu mallake zuciyarki"
Dariya zee tayi tace
"hmm is he really Lucky?"
"sosai ma, keta daban ce nasan shima nasan na daban ne, special people always spiced up"
Dariya zee tayi afili a zuciyarta kuma tana cewa
'yeah, he's special kamar yadda kowa na ahalinshi yake including you'
"inaji" inji Aysha tana qara buga tagumi
"to ni ta ina zan fara?"
"ki fara kota ina ne" tabata Amsa
"ok, bari nafara ta ranar damuka fara haduwa"
Gyara zama Aysha tayi cikin son jin labari fuskarta beaming with smile
"Ranar wata juma'a ce...."
Nan tashiga bata labarin soyayyarsu da Deen.
Komai ta gayamata babu abinda ta rage mata har takawo daidai ranar introduction dinsu saita tsaida labarin iya nan
"wow! So so romantic! Mutumin harya shiga raina, very cool guy dama ana samun irinsu a duniya?"
"why not? Gaki? Komai naku na hallaya iri daya, you're also cool kamar shi, inajin shi kika biyo" inji zee
Dariya Aysha tayi tace
"ta yaya xa'ayi na biyoshi? Mutumin dabamu hada komai dashi ba? Honestly speaking soyayyarku ta burgeni, dama mune Hakan"
Murmushi kawai zee tayi mata
"yanzu ankusa engaging din naku?"
Girgiza kai zee tayi ahankali
"ba'ayi ba? Wait ma, meyasa yanzu kike Dubai shikuma yana Nigeria?"
"Destiny" tafada ahankali tana kallon Aysha
Jikin Aysha ya danyi sanyi ganin yanayin datayi maganar
"bangane ba, where is he?"
"I don’t know either" tafada tana jin komai na dawomata sabo
"I don’t get you" inji Aysha cikin rashin fahimta
"he's.. Gone" tafada cikin murya mai sanyi
"on our introduction day... Ya tafi.. Wai maybe forever wai maybe not, Hakan ya rubuta a takardar daya bar min"
"Zainab are you crying?" inji Aysha ahankali
"nasaba, I do that everyday" tafada tana tsane fuskarta
"ina yatafi? Meyasa ya tafi?"
"I don’t know" tafada tana kallonta trying to control her emotion
"tell me, gayamin komai"
Shiru zee tadanyi sannan tace
"Ranar na wayi gari da matsanancin farinciki, I can't believe ranar family din Deen zasu zo suga nawa kuma mainly akan maganarmu, wannan tunanin nasani shiga shauqi marar misaltuwa
Ranar nayi wanka na zauna ina cancada kwalliyata ina humming best waqa ta ina tunanin izuwa lokacin suna can suna tattaunawa akanmu, kwatsam sai aka bubbugo kofata mummy tashigo rai a jagule..."
Nan tashiga bata kingin labarin da bata bata ba daga qin zuwan mutanen Deen har zirga zirgar da akayi tayi gidansu ana taddawa rufe, har zuwan ta da kanta, har bata wasiqarshi daya ajiye mata da akayi har collapsing datayi lokacin data gama karanta ta har farkawarta bayan kwanaki biyar, har rayuwar quncin data cigaba dayi daga lokacin har zuwan qanwar daddynta Nigeria da shawarar tahowa daita nan datayi har kawo yanzu (Saidai ta 6oyemata gano asalin Deen dasukayi dakuma dalilinta na zuwa school dinnan datayi)
Sosai labarin zee ya ta6a Aysha sai gashi itama tana hawayen
"why? Meyasa ya tafi?" tafada cikin hawaye
"I don’t know" itama zee ta bata amsa cikin hawaye
"yanzu dama kina cikin wannan yanayin? Bakiyi kama da mai wata matsala ba"
"yes, ba lallai bane nayi kama dame matsala ba physically amma idan kika ga zuciyata you'll cry for me, its still broken"
"sorry" Aysha tafada cikin tausayawa
Kada kai zee tayi batace komai ba sai tsane hawayenta data cigaba dayi
"kowa da irin qaddararshi, wataqila kema ba alhairi ne ba agunki"
"wataqila.." inji zee itama
"kinada pics dinshi? Inason ganinshi"
Gabanta yafadi, wai meyasa duk wanda taba labarin shi sai yace yana son ganinshi? Lallai akau ganinshi agareta bamai yiwuwa bane, not now.
"banida, duk na gogesu, babu abinda zanyi dasu kuma, hotonshi na cikin zuciyata ya isheni"
Kada kai tayi tace
"hakane, amma karki dora mashi laifi ummie, karki tsaneshi, allah kadai yasan dalilin tafiyarshi, don’t judge him please"
Murmushi kawai zee tayi sai tace
"I won't, dafarko naso yin Hakan amma daga baya da nasan wasu abubbuwa gameda shi sai nafara tunanin qila it's not his fault din"
"Me kika sani gameda shi?" inji Aysha
Murmushi zee tayi tace lakaci hancin Aysha cikin wasa
"zan gayamaki.. But not now, muje mu nemo wani abu dazamu sama cikinmu, am hungry" tafada tana shafa cikinta
Murmushi Aysha tayi tana tashi tsaye
"muje, nima kina fadin haka naji nima cikina yayi min warning alarm"
Dariya sukayi atare suka fita daga class din suna tafe suna fira cikin annushuwa
Daga ranar suka sake qullewa kamar da kai harma fiyeda da don sau da dama Aysha na bugowa ta hada zee da umminsu su gaisa, ranar farko da zee ta gaisa da Umminsu Saida taci kuka kamar zata shide
Ba mahaifiyarta bace amma taji wani iri sosai a zuciyarta kamar itace din bata ta6a jin muryar mahaifiyarta ba shekara da shekaru, muryar Ummin sak muryar Deen, very cool.
Aysha tasha tambayarta yaushe zatazo gidansu amma Saidai tayita yimata kwana kwana kullum da excuse din dazata bata harta haqura ta qyaleta
A bangaren soyayyar Aysha da Umar kau bata qara sanin yaya suke ciki ba don Aysha tabar waya dashi a gabanta, takuma bar bata labarinshi amma tasan confirm suna tare.
Watarana zee na zaune library da Aysha suna fira littatafai a gabanta da alamu ma karatu sukeyi suka zarce firar.
Wayar Aysha tayi beeping
Dauka tayi ta duba sai gani