Showing 126001 words to 129000 words out of 322641 words
Chapter 43 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
๐"
"๐ฆ kinci bashi yarinya ๐ "
"babu komai na biya idan muka hadu๐ ina alarrama yaya Auwal?"
"waya bashi muqamin alarramancin ๐"
"ai basai anbashi ba, alarrama ne ๐ alarrama ango ba๐คฃ๐คฃ"
"kutt! Ni tsarar wasanki ce ๐ฌ"
"๐๐๐"
"zaki gane bakida wayau ne ๐ "
"๐๐tuba nake uwata ta kaina"
"zamu Hade ne zaki fadamin yaushe muka fara wasan jika da kaka dake ๐ "
"haba Aunty ta ta kaina, ai babu mai jin kanmu insha allah๐ฅฐ"
"๐๐ayi kema azo a aurar dake don naga wani tashen balaga kikeji kwanan nan"
"can't wait ๐๐๐"
"๐ณmarar kunya?"
"๐๐๐๐"
"๐Allah ya shirya"
"Amin summa amin Aunty ta ๐"
Kira taga ya shigo wayarta
*Dโค๏ธ* taga ansa Hakan yasata dan murmusawa
Daidai nan message din Aunty Feenah yasake Shigowa
"ai yanzu tunda hankali ya kwanta dole ki nunama kowa kin qoshi"
Murmushi tayi sannan tayi saurin typing
"eh babu komai๐, Saida safe"
"tun yanzu?"
"shine yakira๐"
"yar isss lamiya๐"
Dariya tayi ta kashe datarta lokacin har kiran ya tsinke amman nan take wani kiran ya shigo
Murmushi tayi Saida takusan tsinkewa sannan ta daga, saita tsinci kanta da kashe murya wajen yin sallama
Wata nannauyar Ajiyar zuciya Deen ya sauke daga dayan bangaren sannan ya amsa sallamarta sannan ya dora da
"nayi tunanin har kinyi barci wlh"
Murmushi tayi
"kamar kaza?"
"who knows"
Murmushi tayi ta janyo pillow qirjinta ta rungume tace
"ina kaka ta?"
"tayi barci nasan takai kaduna yanzu"
Yar Dariya tayi tace
"bakada kirki, a gaban aminiyar tata kake fadin haka?"
"oh haka ne fa ashe ku aminan juna ne"
"sosai ma" inji zee
Murmushi taji yayi sannan yace
"banida lfy, ko ki kira kiji ya nake" ga yanayin dayayi magana tasan kumbura fuska yayi
Dan wara idanu tayi tace
"bakada lfy? Meke damunka?"
"kewa"
Dan daga gira tayi sannan tace
"kewa? Kewar wa?"
"Kewar wa? Banda ke"
Murmushi tayi
"duka yaushe muka rabu"
"duka yaushe ma zakice? Tunfa 3"
"3 din, duka awa nawa?"
"O'O! Kenan ni bakiyi missing dina ba" yafada a marairaice
Yar siririyar Dariya tayi tace
"nayi amma kadan"
"babu komai, what matters shine kinyi, zan taimaka miki nazo school gobe dawuri don ki ganni kiji sanyi a ranki" yafada cikin sigar tsokana
"wasa ma kenan, dani dakai wa zai ga wani yaji sanyi?"
"dani dake"
Sai sukayi Dariya atare
Hira suka shiga yi mai cikeda nishadi da raha
Sai gashi wasa wasa har sukafi mintuna talatin sai anan kudin Deen suka kare
Bugamashi zee tayi ita kuma don Saida firar ta dauko sugar katinshi ya qare
Sai gashi sune har 12 dare suna fira kwata2 sunma mance a wace duniyar suke kawai basa tunawa da kowa da komai sai kansu
Tun zee na iya qoqarin bude idanunta idan suna rurrufewa alamun barci har barcin ya saceta batareda ta farga ba
Jin saukar numfashinta yasashi sanin tayi barci Saidai kuma yaqi kashe wayar saima ya danna recording yana daukar saukar numfashi a zuciyarshi kuma yana hasasota tana barcin, yasan barci zai mata mugun kyau, zaiso ganinta idanunta Lumshe bata komai sai sauke numfashi ahankali, yasan sosai fuskarta zata qara Fiddo cuteness dinta
Katse kiran yayi ba don ya gaji ba sai don tunawa dayayi kudinta ne ke qonewa a banza
Koda ya katse kiran kasa barcin yayi sai juye juye yakeyi
Firarsu yake sake yin bitarshi a zuciyarshi yana jin wani shauqin sonta na qara fizgar zuciyarshi
Ahaka har shima barcin ya daukeshi batareda ya shirya ba.
โค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธโค๏ธ
Soyayya sukeyi tsaftattaciya wanda ya kunshi kulawa da tarairaya a kowanne bangare
Zee bata bar soyayyar ta zama boring ba ta hanyar yin dunkum, itama tana nuna mashi kulawa da soyayya tsantsa dukda ba wai rawar kai takeyi ba, komai tana yinshi ne stylishly da kuma class.
A school tun ana zargin soyayya suke har suka tabbatar da Hakan don a relationship dinsu babu batun wani 6oyo ko kunya, don wani lokacin ma zee ce ke dan jin kunya amma shi baya kunyar nuna mata kulawa a koma inane.
Duk inda kaga daya to dayan na wajen except idan daya yashiga class yabar dayan
Idan suna tafiya Deen ne ke Rataya jakkar zee ita kuma ta rungume littatafanshi
Da farko daya fara amsa jakkarta hanawa take don cewa take tayaya zai daukar mata jakka kamar wata mijin Hajiya
Amma nacinshi dakuma cewan dayake dama ai mijin hajiyan zai zama yasata dinga bashi itakuma saita amshi littatafanshi ta rungume
A fannin waya kau ba dama
Bata ta6a tunanin Deen ya iya waya ba sai a dan wannan lokacin don sa6anin da da idan sunyi gudun tsiya suyi wayar five minutes to yanzu wayar awanni suke kuma su rabu bawai don firar ta ishesu ba
Deen ke fara bugowa sai sun cinye katinshi sannan ita ta bugo su ida wayar.
A fannin text messages kau zee har tasan lokutan shigowar text dinshi a wayarta
Idan ta farka da asuba da text dinshi take fara tozali, idan ranar akwai school kafin ta fito sai yayimata na fatan isowa lfy, idan kuma suka rabu daga school saiya daidaici sun isa gida zai mata na fatan sauka lfy, da daddare ma haka
Itama tana yimashi Saidai ba kamar nashi ba barkatai, tana yimashi daya kowacce safiya, sai ranar juma'a kuma tayimashi na barka da juma'a bayan an taso daga sallar juma'a
Zee bata yarda da yin dunkum ba a soyayya kamar yadda Mafi yawan yanmata keyi
Idan be kira ba ita tana kiranshi, idan suna fira tana co-operating itama batayi mashi shiru Daga eh sai A'a sai hmm
Tana Sakin jiki suyi labari na raha Saidai kuma tana matuqar kama kanta sosai wajen ganin bata bar wata 6araka tashigo a soyayyarsu ba
Akwana a tashi saigashi bikin Feenah sai qara matsowa yake, kowanne bangare an shiga hidima ka'in da na'in
Amarya sai shan gyara take ciki da bai taqara fitowa tass fess kamar ka wanke hannu kafin ka ta6ata
Mummy da zee sai biki saura kwana hudu suka wuce Ruma
Anan zee taita santin kyaun da Feenah tayi tana tsokanarta da itama wacce tayi mata gyaran zatamata itakuma saita hau masifar ta rainata ta maidata kakarta
Bikin ba'ayi wani bidi'a ba sai dinner daza'ayi ranar daurin aure da daddare
Washegarin ranar da suka isa zee da qawayen Feenah data shige cikinsu tsamo tsamo dukda duk sun girme mata suka wuce saloon
Idan ka ganta cikinsu sai kayi zaton tsararraki ne don kusan babu mai girman jiki sosai cikinsu gashi ta iya mu'amalla da mutane musanmman yan gayu irinta shiyasa suma suka jiki sosai daita don tun a ganin farko yanayinta da gayunta yayi musu
Daga saloon suka wuce shopping bags da shoes dazasuyi amfani dashi da yan abubbuwan da ba'a rasaba.
Daga nan suka dawo gida
Ranar daren biki kuma masu qunshi sukazo gidan inda aka yini ana yin qunshi, ita amarya dama mai qunshinta ta musanmman ce don ita kadai dama zatayi mawa
Haka aka xauna a garejin gidan kasancewar yanada girma sosai aka baje anama amarya da qawayen amarya qunshi sai fira ake ana shewa na irin wayyayun mata
Qawayen Feenah kau sai tsiya suke mata ganin yadda Auwal ya addabeta da kira, bini bini sai ya kira Hakan yasa wata qawarta ta amshe wayar daya sake bugowa cikin barkwanci tace allah idan yasake damunsu saisu fasa bashi amaryar su riqe abinsu
Dariya yayi yana cewa tuba yake kanshi abisa wuya, idan suka hanashi ita ai Hakan daidai yake da hanashi numfashin shaqa, ya tuba bazai qara ba sannan yace to don Allah abata yaqara jin muryarta yayi alqawarin daga wannan bazai qara takura musu ba
Dariya dik sukayi sannan qawar tata ta karama Feenah da duk ke jinsu wayar a kunne kasancewar hannunta duk qunshi ne
Suka danyi magana wanda babu wanda yaji abinda suke cewa Saidai dariyar datake ahankali sannan sukayi sallama ya katse kiran
Zee daga inda take zaune ana zana mata na qafa jaa take kallon dramarsu cikin burgewa
Sai yanzu taqara gano hikimar Feenah na amincewa da Auwal don ko yanzu ka santa dashi to saika lura da tsananin so da kulawar dayake nunamata kuma tana ji ajikinta insha allah zata soshi don yana kyautata mata kuma zuciya kowacce iri ce tana tsananin qauna da ganin girman mai kyautata mata
Hakan yasa ta tuna da Deen dinta, basu dade da gama waya ba yana complaining shi ta tafi tabar shi cikin kewarta tana mashi Dariya akan cewa ba gobe zaizo ba (dayake ta gayacceshi daurin aure, Aunty Feenah da kanta tabada katin I.v din abashi don tsakani da allah mutumin yayi mata kuma muddin kaji Feenah ta yabi abu to karka bincika abin yayi ๐ฏ)
Dakyar tasamu sukayi sallama bayan ta fadamashi qunshi za'ayi mata
Basu suka gama qunshin ba gabadaya sai can da marece liss kowanne sai santin nashi qunshin yake don ba qarya masu qunshin qwararru ne
*WASHEGARI*
Rana bata qarya... ๐
Yau su Hajiya Feenah za'a amarce
Gida ya cika maqil ya cinkushe takoina, duk wanda zaka gani is very busy musanmman su mummy da matan kawunnan zee.
Su Umma ana bedroom dinta an qame bisa gado tasha dakakkiyar shaddarta dataji aiki ajiki ga daurin dan kwalin da zee ta dotsana mata mai kyau, anci gayu ansha lalle tsohuwa ta fada kwata, kukau bikin auta guda? ๐
A bangaren Amarya kau tana dakinta dake cike da qawayenta da yanuwa yanmata
Kowa sai shiri yake don an kusan daura auren
Amarya ana gefen gado taci kwalliyarta itama cikin ankon bikinta, fuskar nan tasha makeup ga wani dauri mai shegen kyau da aka murzamata sai hasketa masu daukarta hotuna keyi da flasher.
Zee ce tashigo dakin cikin hijab iya gwiwa sai daurin gaba datayi da zane aciki wanda ana iya hango zanen ta qasan hijab
Fuskarta da hannayenta duk a jiqe suke da alama daga wanka tafito
"wai ke ina kika shiga Tundazu kinbar waya anata kira?" inji wata cousin dinta
Qarasowa tayi tana yamutsa fuska
"wanka najeyi part din Aunty Raliya I can't use toilet din dakinnan"
Harararta yarinyar tayi tana cewa
"sannu tsafttatu, nidai dalla amshi abinki an wani cika mana kunne da kira"
Itama Harararta tayi sannan ta amsa tana cewa
"waye?"
"saiki duba ai da kanki" inji yarinyar tana kauda kai ta maida gasu Feenah dake can suna dimi bama susan abinda suke ba
*Dโค๏ธ* tagani
Murmushi tayi sannan ta juya tafita daga dakin saboda hayaniya ta zagaya can bayan gidan inda babu hayaniya sosai tayi dialing number
Ringing biyu aka daga amma sai akayi shiru
"Baiby.." tafada cikin sigar tsokana
"babu wani nan, don't baby me mun 6ata"
Dan wara idanu tayi murmushi a fuskarta
"6atawa? Meyasa?"
"kinsan kira nawa nayimiki?"
"yakai dari?" ta Tambaya cikin sigar jan fada
"Haka ma zakice?"
Dariya kawai tayi
"mun sake 6atawa, hang the phone banason yin wayar dake kuma"
Dariya tasake yi tace
"kai kayi hanging din mana"
"ai ke kika kira ke ya kamata Kiyi hanging up"
"then we die here"
Dariya sukayi gabadaya
"gist me, kun taho?"
"yanzu muka gama Gaisawa da suruki na"
"suruki kuma?"
"yes, ashe zai iya ganeni? Rabonmu da juna tun hospital kafin a sallameni amma tsaf ya ganeni, muka gaisa amma naji kunya ๐"
"wow! Nufinka har kun qaraso?" tafada cikin doki
"yes? Gashi nanma ana shirin daura aure" injishi
"wow! Ashe dai kakar tabari"
"zauna nan... Bari in katse gashinan za'a fara"
"na bari... Tare zaka biyo su daddy ku dawo nan?"
"tambaya ma kike? Me zan tsaya yi acan?"
"tsayawa Wurin anguna"
"meye kuma anguna? Dama shi ya kawoni? I came to see my missing princess"
Zatayi magana ya sake katseta da
"gashi nan za'a fara, bye.. See you"
Kittt.. Ya katse kiran
Ajiyar zuciya tayi tana rollling manyan idanunta sannan tayi hanyar cikin gidan da sauri don shiryawa
Koda tashigo dakin saita tararda anama Feenah wani daurin dan kwalin don harta chanza kaya zuwa wani royal blue materials
Bata tsaya wani kalle kalle ba tawuce bude wardrobe din Feenah taciro kayanta dake cikin leda tafice daga dakin again
Part din Aunty Raliya taqara komawa don achan ne kadai babu mutane ta bude falon da makullin hannunta tashiga ta rufo
Saida tafara gabatar da sallar xuhr don dama da alwalarta tafito wanka dazu
Sannan itama tafara shiri shap2 don kar Deen yazo bata gama ba
Angon bikin ne tasa Atamfa mai shegen kyau taji dinkin doguwar riga wanda yayi mata dass ajiki
Sannan ta zauna ta tsara makeup dinta daya dace sosai da fuskarta sannan tafara daurin dan kwali
Tana cikin daurin taji hayaniya daga waje sai kuma 6uda dake tashi a can cikin gidan
Murmushi zee tayi ta cigaba da daurinta acikin zuciyarta tana masu addu'ar zama lafiya.
Saida tagama ta tashi ta feffeshe jikinta da turare mai sanyin qamshi sannan ta yafa yalolon gyalenta stylishly a kafada
Linke kayan data cire tayi ta zuba a leda ta ajiye dakin yara sannan tafito da sauri don hayaniyar gidan sai qara sama sama take.
Rufe mata gidan tayi sannan tafito tana tafiyarta kamar yadda tasaba tana duba wayarta dake vibrating
"Hajiya Zainab!"
Taji an kira sunanta abaya
Juyowa tayi sai taga wani cousin dinta ne ke kiranta
Kauda kai tayi kawai bata amsa ba tana qoqarin sake dialing number Deen don shi yakira
"haba Aunty zee, meya kawo fada babu gaba? Magana fa nake maki"
"don kana min magana sai akace dole saina saurareka?" tafada tana qoqarin dialing number still tana cigaba da tafiya
Saurin shan gabanta yayi yana cewa
"tuba nake ranki ya dade, haba sisi nifa yayanki ne be kamata kina yarfani ba"
Wani kallon ta makamashi na wasa tace
"kaine yayan wa?"
"yayanki, idan kina gardama muje mu tambayi mummy"
"A'a daddy zamu tambaya ba mummy ba" tafada tana qara dialing number Deen don ba'a daga wancan kiran ba
"eh muje a tambayeshi daddyn, zakiji abinda zaice. Yarinya bar ganinki haka kin wani zabge to har naman sunanki Saida naci wlh da wayau na aka haifeki"
Sauke wayar tayi daga kunnenta ganin ba'a daga ba again sannan ta kalli cousin din nata tace
"inyee, congratulations tunda kaci naman sunana sai kaje ka rattaba Hakan cikin littafin tarihinka Saidai ko me zakayi bazai chanza ni yayarka bace, haka kowama kecewa" tafada tana mashi gwalo
"marassa hankali ba, don sun ganni da dan jiki? Su kalli fuskata dakyau zasu ga bata yau bace wlh, wadannan tamoji tamojin kadai ya ishesu amsa"
Dariya tayi tace
"ai alarrama anbar duba fuska yanzu, tsawo ake dubawa mallam don haka kazo mu taimaka mu sanmma tsawo" tafada tana mashi Dariya
"Kutt.. Amma fa kin qoshi saura ki dora da juice, wato ni kike ma shairin tsawo ko?" yafada cikin jin haushi
Juyawa tayi tafara tafiya tana cewa
"niba sharri nayimaka ba, Gaski... "
Maganarta ce ta maqale lokacin dasuka hada idanu dashi daga can jikin gini ya jingina da bango ya harde hannayenshi a qirji ya zubamata idanu... โ๏ธ
Kuyi hqr jiya kunjini shiru, jiya bananan ne shiyasa ban samu zaman typing ba ๐
Ummin fasihu
8/2/21, 9:37 PM - Buhainat๐: *๐๐ปโโ๏ธDEEN ๐๐ปโโ๏ธ?*
*043*
*THE PROPOSAL*
Jitayi numfashinta yakusan daukewa saboda yadda ya tafi da imaninta
Sanye yake cikin farar shadda riga da wando irin na samarin nan wanda zakaga rigar da kadan ta wuce gwiwa, anyiwa wuyan rigar siririn aiki da dark blue din zare a wuya dakuma tsakankanin qirji sai kuma saman aljihu
Kanshi sanye da hular dara kalar aikin kayan sai takalmi farare sai usual agogonshi data sanshi dashi daure a hannunshi
Karo na farko data fara ganinshi da manyan kaya kenan sai taji dama su yake sawa don sosai yafito acikinsu yayi wani irin breathtaking kyau
"waye shi din?" taji muryar cousin din nata kamar daga sama
Hakan yasa tayi saurin dawowa daga duniyar kallon Deen ta kalleshi sai kuma tasake kallon inda Deen yake
"muje.. He's a friend" tafada tana wucewa
Dan Jimm cousin din yayi sannan yabi bayanta suka nufi Deen din da haryanzu be Janye idanunshi ba daga kanta
Qarasawa tayi gabanshi cikin murmushi, sai yaji kaso mai yawa cikin 6acin ran dayake ciki yabi iska
"hey.. " tafada tana dan daga mashi yatsu
Dagowa yayi daga jinginen dayake yana murmushi
" hyy"
"ashe kana nan, inata kiranka no response" tafada hankalinta Kwance
"oops na manta ban fiddata daga silent bane, nasata a silent ne dazamu shiga masjid" yafada yana kallon cousin din zee da shima shi yake kallo kowa da irin expression dinshi a fuska
Ganin wanda yake kallo yasa ta juya ga cousin dinta
"Umar meet Deen.. Kamaldeen, a friend"
Murmushi Umar yayi mashi dryly yana miqa mashi hannu
Miqa mashi nashi Deen yayi shima suka shiga yin musabaha
"Deen, this is Umar.. My cousin"
Dan murmushi yayi na gefen baki sannan yace
"ashe shine? The guy.. Nice to meet you" yafada yana yiwa Umar murmushi
Shima dan murmushin yayi yace
"you're welcome" Sai suka sauke hannunsu gabadaya
Umar ne yajuya ya kalli zee datayi kamar wanda ruwa ya cinye don sarai tasan inda maganar Deen ta dosa
"ok sisi, bari natafi, see you" inji Umar
Dan murmushi zee tayi mashi tana cewa
"yeah, see you"
Besake kallon Deen ba yayi gaba ya barsu anan
Binshi da kallo Deen yayi yana jin zuciyarshi na mashi zafi sannan yajuyo ya kalli zee
Cikin basarwa zee tace
"you're welcome to Ruma, so ya kaga garin?"
"Amazing" yafada simply still yana kallonta
Murmushi tayi tace
"to muje ciki ku gaisa dasu mummy ko?"
"is that necessary?" yafada still babu irin wannan walwalar tashi attatare dashi
"yeah, ba kace kun gaisa da daddy ba? Bazata ji dadi ba idan taji kazo bakaje kuka gaisa ba"
Kada kai yayi sai yace
"muje to"
Tare suka jera suka nufi cikin gidan Saidai babu mai magana acikinsu
Zee ta lura fushi yake but he's trying wajen 6oye Hakan
Ita Dariya ma yabata, ita wlh tama manta da wani batun cousin dinta data ta6a yimashi don dama qarya ce kawai don tabashi haushi lokacin yasa tafadi Hakan ashe shi be manta ba
Da ta tuna Da ko introduction din ba zatayi ba Amma kuma a qasan zuciyarta dadi taji ganin yadda yake kishinta, tana son mutum mai kishin abinshi wanda beson wani abu ya ra6eshi ko yaya ne Hakan na daya daga signs of qauna.
Wani wuri inda babu jama'a sosai suka tsaya
"bari nayiwa mummyn magana"
Kada mata kai kawai yayi ta juya ta wuce yabita da kallo
Hannu yasa ya cire hular kanshi yadan yamutsa lallausan gashinshi sannan ya maida hular ya sake harde hannayenshi a qirji
Ganinta da wani ya 6ata mashi mood sosai, kafin lokacin murna yake da doqin Ganinta amma kuma ganinta da wani