Showing 138001 words to 141000 words out of 322641 words
Chapter 47 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
ta kuma sauke idanunta qasa tana wasa da yatsunta ta Wani yi kalar tausayi
Ganin Hakan yasa daddy riqo hannunta datake wasa dashi din yace
"tell me, wani abu ke damun ki?"
Shiru tayi kuma bata dagoba
Qara squeezing hannunta yayi
"tell me" yafada a tausashe
Hadiye wasu yawu ahankali sannan tace
"daddy, dama...maganar Deen ne.... Please daddy.."
"I thought mun riga munyi closing wannan chapter dake" daddy ya katseta da fadin Hakan
"daddy, wlh Deen beda matsala ko kadan, he's very nice and innocent, gashi yanada ilimi both boko da Arabic and he loves me so much more than I did to him"
"so? Don duk yanada wadannan abubbuwan Hakan na nufin zai iya riqeki? Anacin ilimi ne? Ko ana saka kyawawan hali? Meye aikinshi? Nawa yake samu a wata? Sune abubbuwan daya kamata ki gayamin"
"daddy he's still under-graduate wannan shine last year dinshi a school kuma yace min yana practicing carpentry work irin na funitures yana dan samu anan kuma ai kafin lokacin yagama school nasan ma yasamu aiki"
"carpentry? Nufin ki kafinta zaki aura? Diyar dan faranshi a matsayin matar kafinta?"
"daddy I told you zai samu aiki kafin lokacin" tafada kamar tayi kuka
"yaushe? A wannan Nigeria din kikeda yaqinin samun aikinshi da wuri? Masu kwallin degree har masters nawa ne ke kan titi Suna yawo kullum don neman aiki? Wasunsu sunfi shekaru biyar suna buga bugar neman aikin haryanzu basu samuba, ahaka zakiyita jiranshi har saiya samu aikin wanda allah kadai yasan lokacin?"
"Daddy, kana da companies dayawa, yanzu haka akwai dayawa dakake ginawa, kullum cikin daukan ma'aikata kake, a ganina samun aiki bazai yima wanda nakawo wajenka a matsayin wanda nakeso wuya ba don ko wasu nakawo Koda bansansu ba kawai nayi niyyar taimakonsu nakawosu wurinka gani nake zaka iya sama masu aiki a cikin kanfanoninka bare wannan"
Murmushin manya daddy yayi
"yanzu na gano komai, kuma na tabbatar da abinda nake zargi.
Wato dama don kudinki yake sonki, don yasan ke diyar wani ce wanda idan ya ra6a yasan zai kwashi arziqi, tunda harya fara sanya maki tunanin ni zan samomashi aiki"
"haba daddy" zee tafada hawaye na kawomata
"wlh daddy, kaji na rantse? Bamu ta6a wannan maganar dashi ba hasalima bayada kwadayi ko kadan wlh, abin hannun mutum be cika damunshi ba"
"haka zai nunamaki ai amma a zuciyarshi akwai wata manufa ta daban, auran jari yakeson yi dake yadda shima zai ra6i arziqi, nawa akayi? Nasha ganin irin case dinnan a wurare da dama, sai yaro yazo ya hurema diyarka kunne ya kasance ta aminta dashi dari bisa dari, ta nace sai an aura mata shi sai angama sannan tazama itace abin wulaqantawa na farko a Wurin shi sannan kuma yafara planning yadda zai handame komai nata yadawo qarqashinshi, that's it, that's their aim"
Hawaye sosai zee keyi tunda yafara maganar
"haba daddy, why zaka siffantashi da wadannan munnanan aiyukan? Don baka sanshi bane, da kasanshi da bazaka ta6a fadin haka akanshi ba" tafada cikin kuka
"kema ai iya abinda yakeso kisani gameda halinshi yabari kika sani, dama bari zaiyi kisan qudurinshi? Koko cemaki akayi hali a fuska ake ganewa, Zainab you're too young, bakisan komai ba a rayuwarnan.
Ni nasan duniya kuma nasan mutanen cikinta, huldata ta yau da kullum yasa nasan mabanbantan halayen yan Adam
Ba kowanne murmushi ke amsa suna murmushi ba, wani murmushin na mugunta ne, don mutum yayi looking innocent ba hakan na nufin he's innocent din har cikin zuciyarshi ba
Kin riga kin makance a soyayya, ya riga ya burkita tunaninki, bazaki iya gane komai ba yanzu don bakya a hayyacinki
amma ni ina a hayyacina kuma bazan ta6a folding hannayena ina kallonki ki fada halaka ba, never!
Don Haka ma mubar wannan maganar don rayyuka ne kawai zasu 6aci don abune da bazai ta6a yiwuwa ba"
Kuka sosai zee keyi, tama rasa abinda zatace
Bata ta6a sanin haka akeji ba idan akaqi fahimtarka, bata ta6a sanin haka akeji ba idan aka soki masoyinka ba aka laqamashi abinda kasan bazai ta6a iyawa ba
Wai Deen daddy ke cewa saboda kudi yake sonta, yaudararta kawai yakeyi saboda kudinta, how? Mutumin da abin duniya basa gabanshi? Be damu da abin hannun mutum ba? Tayaya?
Shigowar mummy da sallamar ta yasa duk suka dago suka kallo kofar
Mummy tadanyi Jimm ganin expression din fuskokinsu, zee idanu jajur ga hawaye a fuskarta shikuma daddy alamun 6acin rai a fuskarshi
Qarasowa tayi cikin dakin Hakan yasa zee miqewa tsaye
"Saida safenku" tafada idanunta a qasa sannan ta juya ta fice dakin
Binta da kallo duk sukayi harta fita
Maida kallonta mummy tayi akan daddy Saidai ko damar yin magana be bata ba shima ya tashi ya nufi bedroom dinshi rai 6ace.
Da gudu ta nufi gadonta ta fada akai ta cigaba da kukan datake
Tarasa meyasa daddy bazai tsaya ya fahimceta, tarasa meyasa daddy yayi ma abin mummunar fahimta.
A ranar barci rabi da rabi tayi sai can gab da asuba wani barci mai dadi ya dauketa Hakan yasa Saida mummy tasha wahala kafin tasamu ta tashi sallar asuba.
Koda tagama komawarta barci tayi bata farkaba sai wajajen 8:30am shima don mummy ce ta sake tadata.
Wanka tashiga tayi sharp sharp tafito ta shirya ta tsara makeup dinta sannan tafito cikin shirin school ta sauko qasa
A falo ta tarar da mummy, gaidata tayi ta amsa sannan ta nuna mata dining area tace taje tayi break
Babu musu tawuce don tasan dole tayi inba haka ba ranta ne kawai zai 6aci a banza
Tadan ci babu laifi sannan ta taso tazo tayiwa mummy sallama sannan tafice.
*UMYU*
Qarfe 9 da yan mintuna suka isa makarantar
Tana jin anyi parking ta bude lumssasun idanunta ta dan kalli waje sannan ta miqe zaune daga jinginen datake da kujerar motar ta tsaida waqar datake ji ta bluetooth din kunnenta
Jitayi an bude mata kofa Hakan yasata daukar jakkarta tafara yunqurin fitowa.
Dago kan da zatayi sai taga ashe Deen ne ma ya bude kofar, yana tsaye riqe da murfin motar yana kallonta
Dan wara idanunta tayi alamun dama kaine
Shikuma yayi mata murmushi tareda ja da baya yana bata hanya don saukowa
Ahankali ta sauko tana kallon smiling face dinshi tana jin damuwarta na yayewa a hankali.
Saida ta ida fitowa sannan ya maida kofar ya rufe sannan ya juyo wajen ta yana mata murmushi yace
"Good morning"
Murmushi kawai tayi mashi sannan tace
"ya weekend?"
"Bad.. That's the most boring weekend I've ever had"
Dan wara idanu tayi
"dagaske? Meyasa kace haka?"
"zan gayamiki, but first mutafi tukkuna"
Hannu ya miqamata yana dan russunawa
"may I?"
Tasan abinda yake nufi Hakan yasa tabashi jakkarta itama ta miqamashi hannu ya doro mata littatafanshi akai
Murmushi sukayima juna sannan suka nufi cikin school din.
Basu yada zango a koina ba sai library don dama yau sunyi zasu dan ta6a karatu
Kwana biyu soyayya ta hanasu karatu, da sun zauna sai su bige da firar soyayya before you know it lokaci ya tafi hakan yasa suka yanke shawarar fidda ma kansu timetable din karatu inda zasuyi scheduling komai yadda ya kamata.
Usual seat dinsu suka zauna kowa na ajiye abin hannunshi bisa desk
"Tundazu nake jiran zuwanki"
"to? Amma ai am not late ko?"
"you're not late amma son ganinki ne yasa naga kamar kinyi late din"
Murmushi zee tayi batace komai ba
"how's your weekend?"
"cool.. Kaifa?"
"not that cool" yafada yana yatsine fuska
"why not?"
"I was missing you, most especially muryarki, wai me yasamu wayarki?"
"kajita kashe jiya?"
"yes, tunda mukayi wayar nan da safe naketa neman wayarki amma shiru, what's wrong?"
"matsala tadan samu shiyasa, muna cikin waya ta dauke sai screen din yabar kawo haske sai kawai na badata aka gyaromin" tafada tana daukar jakkarta dake gabanshi ta fara zuge zip din
"ayyah, I thought as much. But are you sure you're ok?"
Dagowa tayi daga bude jakkar datake
"Me ka gani?"
Daga kafadu yayi
"kawai naga kamar you're not ok ne, kinmin wani iri"
Murmushi kawai tayi ta cigaba da leqa jakkarta
"then idanunka sun fara ciwo" tafada cikin tsokana
Murmushi shima yayi yace
"babu mammaki"
Ciro handout da wani littafin tayi tana cewa
"yanzu dai mufara, karka shagalar damu da surutunka"
Harararta yayi yafara Ciro Littafi shima
"ni dake wa yafi surutu?"
"ni dakai"
Dariya sukayi atare sannan duk suka bude Littatafan suka fara duddubawa
Sun dan jima ahakan kafin lokacin shiga lecture din zee yayi ta wuce ta barshi anan shima yana duba nashi Littatafan kafin shima lokacin shiga class din nashi yayi shima ya tashi.
Babu laifi zuwanta school a yau ya ragemata damuwarta sosai kuma ta cigaba da iya qoqarinta wajen 6oye damuwarta don ganin Deen be fahimci komai ba dukda dai yini yayi yana mata mitar shidai sai yaga kamar she's not ok
Abin na bata mammaki don sosai take qoqarin pretending komai is ok amma sai yace tayi wani iri kamar something is wrong, idan yace Hakan saita tsokaneshi akan qila idanun ke buqatar doctor sai suyi Dariya Hakan kuma bazai hana yasake yimata maganar ba idan yasake kallon fuskarta.
Sai wajajen 3pm bala yazo daukar zee
Har motar Deen ya rakota kamar yadda suka saba tun bayan fara soyayyarsu
Shi ya bude mata kofar tashiga sannan ya rufo mata yana cemata sai sunyi waya
Kada mashi kai kawai tayi tana murmushi
Dage tinted glass din motar tayi takoma ta jingina da kujera tana kallonshi
Jin an tada motar yasa Deen dake waje fara daga mata hannu dukda baya hangenta
Bïñ hannun tayi da kallo tana kallon band din data dauramashi ranar valentine
Saita maido kallonta kan nata itama
Ahankali ta danna dan botton din fuskar abin yakawo wuta
_*DEEZEEN 💞*_
tasake dannawa
_*TOGETHER FOREVER ❤️*_
Murmushi tadanyi ta dago tana kallon Deen jin motar tafara tafiya
Har a lokacin daga mata hannu yakeyi har Saida suka fita daga school din
Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya maida hannayenshi cikin aljihu yana cigaba da bin inda suka bi suka fita da kallo kafin daga baya yajuya yakoma inda yafito.
Tun daga ranar da sukayi magana da daddy tashiga wasan 6uya dashi
Idan tasan yana wuri bata yarda tafito wurin haka ma idan ya ritsata gaisuwa ce kawai a tsakaninsu babu irin wannan wasan nasu
Da farko tayi tunanin itace ta dauke mashi wuta sai daga baya taga ashe shima Hakan take a wajenshi don maimakon ya damu kamar yadda yasaba yi duk lokacin da take fushi akan abu sai taga tayi biris daita kamar ma besan tana yi ba wanda Hakan na nuna alamun babu gudu babu ja da baya a Maganarshi.
Hakan yaqara sakata cikin damuwa, don tasan muddin aka rabata da Deen to rayuwarta ta tagayyara don Deen shine farincikinta, idan babu shi zata qarasa rayuwarta ne babu ko digon farinciki.
Ta rasa yadda zata 6illowa daddy ya fahimceta yakuma fahimci Deen don taga alamun ma kwata2 Deen be yimashi ba don ko Maganarshi bayason ana tadawa a gidan.
Rannan data rasa yadda zatayi saita yanke shawarar samun mummy da maganar
Batasan ra'ayin mummy akan wannan case din ba amma sai taga kamar mummy na son za6inta duba da yadda bata nuna rashin amincewa ba akan Hakan kamar yadda daddy yayi.
Ranar Saida tagama sallar asr sannan ta tashi bayan tagama bitar abubbuwan dazata gayawa mummy din
Direct dakinta ta nufa don bataji fitowarta ba Tun bayan shigarta sallah
Ahankali tafara knocking acikin zuciyarta kau tana addu'ar samun nasara
Tasan idan har mummy ta goyi bayanta to abin zaizo da mugun sauqi don zatasan yadda zatayi convincing din daddy kamar yadda tasaba a abbubuwa da dama.
Saida tayi knocking uku sannan aka bata izinin shigowa
Ahankali ta murda handle din ta tura kofar tashiga da sallama a bakinta
Mummy dake ninke sallayarta ta dago ta kalleta ta amsa sallamarta sannan ta cigaba da ninkinta ta ajiye a ma'ajiyarta.
Qarasowa zee tayi jiki a sanyaye kamar ta allah sannan ta zauna bisa sofa dake dakin
Zama itama mummyn tayi a gefen gadonta tana kallonta, kallo daya zakayimata kasan tana cikin damuwa
"yes? Meya faru ne?" inji mummy a tausashe
Hakan yasa taji zuciyarta na raunana
Shiru tadanyi tana jujjuya abinda zatace sannan ta dago ta kalli mummyn
"mummy... Dama akan.. Maganar Deen ne.." saikuma tayi shiru
Itama mummy shiru tayi tana kallon ta kawai
"mummy, daddy kwata2 yaqi fahimta ta, wai saboda kudi Deen kesona kuma wlh ba Haka bane hasalima shi bema damu da abin mutum ba, idan ma ka bashi baya son amsa.
Deen na sona sosai mummy, bazai ta6a yaudarata ba kamar yadda daddy ke cewa saboda bema san yadda ake yaudarar ba
Babu ruwanshi, he's so innocent, shine silar gyaruwan wasu daga halayena marassa kyau, shi yafara saitani a hanya mai kyau batareda nasan saitanin yake ba.
He's always there for me, yana taimakona a karatu sosai mummy, sosai.
Shi yafara sona tsakaninshi da allah tun kafin ma yasan sona yake.
A school babu mai sona harta wadanda nakema daukar qawaye, duk kowa qina yake sai shi kadai dukda abubbuwan danayi mashi marassa kyau"
Saita fara bata labarin farkon haduwarta dashi dakuma haduwarsu ta biyu da abinda yafaru
Ta cigaba da bata labarin yadda ta maida shi errand boy dinta har zuwa lokacin da case din assignment dinta ya hadasu da kwanciyar asibiti data jamashi
Ta gangaro zuwa yadda suka shirya dakuma yadda yafara nunamata kuskuren da takeyi har ta gangarowa zuwa ranar da abinnan yafaru tsakaninta da master.
Labarin take badawa tana kukan da batama san tanayi ba
Ta cigaba da cewa
"mummy har waya na siyamashi lokacin da za'a sallameshi ganin bayada waya tashi ta fadi a wancan ranar amma yaqi amsa Saida nayi fushi sosai sannan ya amsa kuma bama amfani yake daita ba don tun daga ranar ban qara ganinshi da ita ba
Be ta6a roqona yar biyar ba, kuma bayaso nabashi, ko tashi mukayi daga makaranta Saidai yayi min karyar akwai abubbuwan dazai tsaya yi a makarantar duk don kar nace yazo mu rage mashi hanya.
Mummy tayaya za'ace saboda kudina yake sona? Wlh ni nasani soyayyar Gaskiya yakemin mummy, idan narasa shi bazan ta6a samun wanda zai soni ko rabin son da yakemin.
Please mummy kisa baki, kema ai kinsan halinshi, he's very nice and obedient.
Aunty Feenah ma tasan shi da ita da yaya Auwal suma duk sunce yanada kyawawan halaye don su sukama gayyaceshi a bikin su kima tambayesu kiji, wlh babu ruwanshi, bazai ta6a yaudarata ba mummy"
Tunda tafara maganar mummy ke kallonta
Lallai Zainab, ba qaramin kamu soyayyar Deen tayimata ba, ji yadda tabi ta rikice
Ita dama tun a hospital tafara zargin Hakan amma sanin halin zee na high taste dinta akan namiji shiyasa bata ta6a kawoma ranta soyayyar ce dagaske
Ajiyar zuciya mummy ta sauke sannan ahankali tace
"Zainab, nima nasani, Deen bazai yaudareki ba Amma abinda nakeso kisani shine, baka kwallafawa ranka abu kace dole dole sai abin don Mafi yawancin abubbuwan da mukeso baya zama alhairi agaremu shiyasa allah ke musanya mana da wani abin, idan mukayi hqr sai kiga munci ribar haqurin.
Zanyi mashi magana kamar yadda kika buqata amma kuma inason kisa a zuciyarki koma menene idan har Kamal mijinki ne to saikin aureshi idan kuma ba mijinki bane ko duniyar nan zaki gayyato suyima daddyn magana Hakan bazai faru ba
Abinda nakeso ki dinga yi shine addu'a, ki dinga addu'ar allah ya za6amiki abinda yafi alhairi bawai ki nace Lallai lallai sai shi ba, idan shine yafi alhairi allah ya za6amiki shi idan kuma bashi bane to allah ya musanya miki da wanda ya fishi, kinji ko?
Kada kai tayi ahankali acikin zuciyarta tana cewa insha allah shine ma wanda yafi alhairin
Cigaba da yimata nasiha mummy tayi mai kwantar da hankali wanda Hakan ya rage mata kaso Mafi yawa na damuwar ta kafin daga baya ta sallameta akan zata sameshi tayi mashi maganar, kawai tayi addu'ar allah yasa ya gane don ita tana maraba dashi a matsayin suruki don hallayarshi ta dade tana burgeta.
Da wannan zee taqara samun qwarin gwiwa, tashiga addu'ar allah yasa qarshen case dinnan kenan, allah yasa ya fahimta.
***
Suna Kwance suna dan fira irin na kafin barcin nan cikin nishadi
Mummy nata son yimashi maganar su Deen Amma tarasa ta ina zata fara don a kwana biyun nan ta fuskanci idan akwai maganar wanda ke 6ata mashi rai to na Deen ne
"jiya ma munyi waya da Ummu batool ai tace tana gaisheka wai ta nemi number ka bata shiga" inji mummy
"ita ta nemi number ta Ko ni na nemi number ta? Tunfa shekaranjiya nake neman number ta bata shiga" inji daddy
"nima haka nace mata don nima na nemeta ban samu ba wai ashe layi ta chanza, jiya ma da sabuwar number ta kira"
"ayyah to duk ya suke? Yasu batool?"
"Duk suna lfy lau ai har gaisawa mukayi da batool shi yayan nata ne bayanan yana wajen aiki"
"ai wadannan yaran naso naga lokacin da zasu dinga zuwa nigeria frequently musanmman babban, rabonshi da nigeria ai za'ayi shekara biyar ko?"
"ko fi ma, ai kasan halin aikinsu they're always busy gwara gwara batool ita ana dan zuwa daita dukda itama wani sa'in school na hanata zuwa"
"ai babu komai, insha allah lokaci zan fidda mu kwasa dukanmu muyimusu zuwan bazata"
Yar Dariya mummy tayi tace
"dakau mun kyauta, ai yakamata a dinga tunawa da zuminci ko yaya ne bawai business ba kowanne lokaci"
"to? Dani ake kenan?"
Yar Dariya taqara tace
"ni bance ba Saidai idan tsarguwa kayi"
"har tsarguwar ma nayi tunda nasan dani ake"
Dariya sukayi sakeyi atare
Shiru yadan biyo baya
"diyarka fa nacan, kodayaushe very moody, abinci ma saina tilasta mata takeci, na rasa gane kanta"
Nan take mood din daddy ya chanza
"ai dole kiga Hakan tunda tana can kullum wancan yaron na zigeta"
"Yana zigeta kamar ya?"
"hmm, ai duk motsinsu yanzu akan kunne na yake don tun ranar da mukayi maganar qarshe akanshi daita nasamu balarabe nayi mashi Tambayoyi akansu yace min shidai ada lafiya lau take huldarta ita daya amma daga baya ya dinga ganin yaron na liqemata wai har budemata mota yake idan zata shiga ma Hakan wai harda riqe mata jakka.
Bayan naji daga gareshi na sallameshi na kuma samu wani akan ya dinga samin ido akansu a school din and the same amsa dasamu dana bala harda ma qari