Showing 237001 words to 240000 words out of 332344 words

Chapter 80 - KIRAN RABO Book 3 Complete Hausa Novels By Nanah Halima.doc

30 Nov 2025

14894

bayan sallar magrib Didi ta kira wayarsa, a lokacin yana tsaye da key Win mota zai je ya Wauko Nayla. Ya Wauki wayar ya saka a kunne ta ce,  Omar ya ake ciki? Ina fatan maganar ta wuce ko?. Ya ja tsaki cikin Sacin rai ya ce,  bata wuce ba, tarwatsa zaman nayi domin abinda ya nema bazai samu ba. Saboda abinda ki ka ce ne ya saka na amince dpo ya shiga maganar, wai an kira shi ana faWa masa abinda za a yi ni yake kallo yake cewa sai na bashi ha?uri zai ha?ura? Ni Omar ni ne zan bashi ha?uri?.

Didi cike da takaici ta ce,  to meye a cikin bada ha?urin? Ba dai in ka bada ha?urin maganar ta wuce ba?.

 Na fi ?arfin na bada ha?uri. Mutum biyu kaWai na taSa bawa ha?uri a duniya, daga ke sai Jidda. Bana sauke kai ?asa in na kalli sama, shima yana so ya kafa tarihi a kaina shiyasa yake so na bashi ha?uri, dan ya san ba Wabi ar Omar bace.

 Yanzu fisabinillahi meye dan ka bashi ha?uri? Kalma uku ce fa kacal Omar, a cikin kalma ukun nan da zaka furta akwai kwanciyar hankalinka, dana matarka, dana Wan cikinta. Rai uku ne a ?ar?arshin kalmar ka yi ha?uri, kenan ka zaSi a rasa rayuka har uku akan kalmar ha?uri?. Yanzu da baka bada ha?urin ba in suka cutar da ita fa?.

Ya yi shiru bai ce komai ba, Didi ta cigaba da yi masa nasiha cikin kalamai masu daWi da kwantar da hankali, ta hana shi magana tana isar da sa?on da take so ta isar, tana sake faWa masa illar ?in bada ha?urin Nayla za a cuta. Da yake ta san Nayla ce rauninsa tunda take faWar haka sai ya sauke ajiyar zuciya ya ce,  FaWuwa ce a gare ni na bada ha?uri.

 Ba faWuwa ba ce, kowa yaji ka bada ha?uri zai tabbatar da cewa Omar Win baya bana yanzu bane, Omar Win yanzu ya san abinda yake yi. Mai hankali da wanda ya san ya kamata shine yake kwantar da rigima. Kasan adadin mutanen da zai haWa kai dasu a cutar da Nayla? Yanzu ba ta kai suke yi ba, Nayla zasu cutar saboda itace rauninka Omar, duk yadda da zasu bi dan cutar da ita zasu bi. Don girman Allah ka bada ha?uri a wuce wajan.

Omar ya sauke numfashi ya ce,  Didi in na bada ha?uri na faWi, na ja baya, kuma naji tsoro. Ban dace da wannan abubuwan ba, zubina ba na masu bada ha?uri bane. Didi taji kamar ta ziro hannu ta wayar ta zabga masa mari. Didi ta ce,  yanzu zaka koma gidan jiya kenan? Zaka butulcewa ni imar da Allah ya yi maka ko?. Ai shikenan Omar Allah ya taimaka, ina jin sai ka ga gawata, kaga gawar Nayla, kaga ta Marmerh duk an kashe mu saboda bashin da kake Wauka sannan zuciyarka zata yi sanyi. Kar ka bada ha?uri, ka je ka yi abinda ka ke so ta faWa tana yanke wayar. Ajjiye wayar yayi ya Wauki abinda zai Wauka ya fita daga gidan.

Bai je Waukar Nayla ba sai ?arfe tara na dare, yana ajjiye motar ya ganta a ?ofar gida ita da Jidda da mijin Jidda, da Jawad da Salma da alama rakiya suka yo musu. Wani takaici ya mamaye masa zuciya, daman ransa a Sace yake ga wani Sacin ran ya tarar. Ganin Jawad yana kallon Omar yana dariya sai ya daure ya fito daga motar ya ?arasa inda suke. Da Wan murmushi a fuskarsa suka gaisa da Jawad, suka gaisa da mijin Jidda. Salma da Jidda suka gaishe shi ya amsa fuskarsa ba sakewa sosai.

Nayla ta bishi da kallo suka haWa ido sai ta ce,  bara na Wauko wayata a cikin gidan. Ko kulata bai yi ba ya Wauke kai. Yana gani sai shagwaSa take yiwa Jawad yana biye mata, harda ri?e mata hannu ita kuma ta yi masa side hug Salma tana tsokanarta. Yana cikin mota yana kallon komai zuciyarsa kamar zata buga saboda haushi. A haka su Jawad suka tafi ita da Jidda da mijin Jidda suka koma ciki.

Ba jimawa Nayla ta fito ita da Jidda ta shiga motar Jidda tana yi mata sallama suka wuce gida.

Yadda fuskarsa take a Waure haka itama ta ta fuskar ta ke, Allah ya sani yana bata haushi sosai. Ace har yanzu ya kasa sakewa da danginta? Har gwara Jawad yana iya yi masa murmushi amma ko Salma fuska ba yabo ba fallasa yake amsa gaisuwarta. Tana ganin yadda mijin Twiny yake, wasa da dariya ake yi dashi kamar Wan gida amma nata miji kamar fuskar shanu.

 Kafin ki shiga gidan Wazu me nace miki?. Juyowa tayi ta kalle shi taga kamar ba shine ya yi maganar ba. Ta muguWa baki ta ce,  kace na zauna a gidan.
 Amma da nazo a ina na same ki?.
 Yaya J ne fa& ..
 Ki amsa min kawai, a ina na same ki?.
 A waje.
 Yayi kyau. Daga nan bai sake cewa komai ba suka cigaba da tafiya itama bata ce komai ba.

Haka suka ?arasa gidan suna share juna, ta wuce Waki tayi wanka ta shirya ta fito zuwa Wakinsa ta shiga. A zaune ta same shi yana waya, ta ?arasa ta zauna a akan gadon tana danna wayarta.

 Abinci fa? Ya tambaya ba tare da ya kalle ta ba. Nayla ta mi?e ta ce,  me zan dafa maka?.
 Dake nake. Sai ta koma ta zauna ta ce,  naci abinci, sai dai na dafa maka. Bai ce mata komai ba ya cigaba da abinda yake yi itama haka. Gajiya tayi ta tashi ta kashe hasken Wakin tayi addu a ta kwanta. Bai jima ba ya tashi ya kwanta shima, duk a zatonsa tayi bacci ya jawota jikinsa yana shafa ?ansan cikinta yana ji wajan yayi tauri sosai. Ya lumshe ido ya yiwa wajan kiss yana jin ?aunar abinda bai zama mutum ba a zuciyarsa.

Nayla tana jinsa tayi shiru kamar tayi bacci, ya yi pecking goshinta yana sake gyara mata kwanciya a jikinsa.

Washe gari da ta tashi har breakfast ya yi, bayan tayi wanka ta zauna a kusa dashi ta ce,  YaMar. Ya kalle ta sannan ta ce,  zan je gidan Daddy. Ya Wauke kai daga kallon ta bai ce komai ba. Nayla haushinsa ya mamaye mata zuciya, ta mi?e ta bar falon. Ya bita da kallo bai motsa ba ya cigaba da abinda yake yi.

Bata jima ba ta fito ta haWa tea ta wuce dashi Waki bata ce masa komai ba. A haka suka yini shida ita kowa yana jin haushin Wan uwansa. Da daddare da ya shigo ta gama dafa noodles tana zaune tana ci. Yana zama ta tashi ta kawo masa ya bita da kallo ba tare da ya karSa ba. Ta ajjiye masa a gabansa cigaba da cin abincinta. Tana gamawa bata ce masa komai ba ta wuce Waki, ya yi murmushi yana shafa kansa.

Sai da ya gama abinda zai yi sannan ya shiga Wakinta, a banWaki yaji motsinta sannan ta bar ?ofar a buWe. A hankali ya ?arasa sai ya tarar tana amai, duk noodles Win da taci ta dawo. A ruWe ya ?arasa ya ri?ota ya ce,  Jidda baki da lafiya? Me ya same ki?. Ya ri?ota suka dawo Wakin ya zaunar da ita akan gado, ya fita ya kawo mata ruwa tasha ya zauna a gefenta tare da ri?e hannunta ya ce,  yanzu har fushin da ki ke yi dani ya kai baki da lafiya baza ki faWa min ba Jidda?.

Nayla ta kalle shi ta ce,  Nifa lafiyata ?alau, wannan aman kuma ina yi wani lokacin.
 Me yake kawo shi?.
 Unborn ta faWa ba tare da ta kalle shi ba.

 Amma ya kamata ki faWa min, bai kamata fushin ki ya shafi rashin lafiyarki ba. Ta kalle shi kafin tayi magana ya ce,  kin dawo da abinda ki ka ci, me zaki ci yanzu?. Ta girgiza kai ta ce,  bana jin yunwa.
 A a, ki faWa min abinda zaki ci.
 Bana jin yunwaaa! Ta ja ?arshen kalmar hawaye yana sakko mata.

Omar ya dafe kai ya ce,  Jidda meye na kukan kuma? Ya kike so nayi miki? Kina so ki haukata ni ne?. Nayla ta goge ido bata ce komai ba. Ya zamo daga kan gadon ya zauna a ?asa kusa da ?afarta yana kallon fuskarta tana ?ifta idanu ya ce,  Jiddaaa!. Ta Wago ta kalle shi ya ri?e hannayenta ya ce,  laifi nayi miki?.

 Kai na yiwa laifi, kaine tun a gidan Twiny ka ke ta hararata kawai dan ka ganni a ?ofar gida. Kuma tun daga Kaduna Yaya J da Salma suka zo yi mana sallama zasu tafi Malaysia, dan na fito na rako su ?ofar gida sai ya zama laifi?.

Omar ya zuba mata ido yana kallon yadda take maganar da fusata da alama bata ji daWin abun ba, ya sauke numfashi ya ce,  Duk abinda nake yi saboda ke nake yi Jidda, duk saboda lafiyarki nake yin hakan.

 Amma ka san Yaya J ma bazai bari wani abun ya same ni ba, in ma sake ?o?arin kashe ni Win ake yi zai tsaya dan ganin ya kare ni kamar yadda zaka kare ni. Har yanzu ka kasa sakewa da ?an gidanmu, kayi ta Waure fuska in ka gansu. Wai a haka ma kana sakarwa Yaya J fuska shiyasa fuskarka ta tsaya a haka. Amma Salma da Jidda kamar baka sansu ba, ka haWe rai in ka gansu kamar waWanda ba jinina ba.

Omar ya yi shiru yana jinta dan yaga alama abinda yake ranta kenan shiyasa zai bari ta gama. Nayla ta ce,  bana jin daWin hakan ko kaWan, ba haka naga ana yi da mijin Twiny ba, shi sakewa ake yi dashi kamar Wan gidanmu haka yake. Kai kam Yaya J kawai ka ke sakarwa fuska, Yaya Ahmad kuwa ko number wayarsa bana tunanin kana da ita. Yanzu in aka nuna kama Jalil da Jalila ?annena baza ka gane su ba, saboda baka sansu ba. Sati biyu Jalila tazo tayi a gidan Twiny, ni da nace mata meyasa bata zo gidan nan ba cewa tayi tsoronka take ji, kuma tsoron gidan nan take ji kar a shigo a kashe ta. Ni bana jin daWin attitude Win nan naka gabaWaya, lokacin da Twiny ta haihu ni mijinta ya kira ya faWawa, yanzu ni in na haihu ko Jidda baza ka gane a fuska ba balle har ka samu number ta ka kira ta. Balle kuma a kai ga kiran su Mama ko Hajja ta faWa tana kuka sosai.
KRB3P090
Nana haleema.

Rauni ya mamaye zuciyar Omar musamman maganar ?anwarta da tace tana tsoron zuwa gidan, ya yi shiru yana jin yadda take kuka kana ta ce, "wanda suke Kano sune a kusa dani, amma kai da na Kaduna ka ke Wan sakewa kaWan."

Omar ya yi shiru yana kallon ta zuciyarsa sam babu daWi, ta ja numfashi ta goge idanunta tana kallon gefe Waya. Calmly Omar ya ce, "ki yi ha?uri." Ta kalli idanunsa jin yadda kai tsaye ya bata ha?uri, duk dai bai Wauki bata ha?uri a bakin komai ba, har mamaki take yi in ta Sata mata rai ya gama fushin kai tsaye zai ce mata ki yi ha?uri. Tana mamakin hakan dan bata Wauka zai iya aikata hakan ba, dan Twiny ta faWa mata mijinta duk bala'i baya buWe baki yace tayi ha?uri, sai dai zai yi abubuwan da zata fahimci ha?uri yake bata. Tayi mamakin bada ha?urin nasa cikin sauri haka, dan ta san sai ya gama fushin sannan yake bada ha?uri. Omar ya girgiza kai ya ce, "nasan a zuciyarki kina regretting aurena, kina ji ina ma baki aure ni ba, da baki aure ni ba da ?anwarki bata ce tana tsoron gidan nan ba. Ki yi ha?uri Jidda!."

Zata yi magana ya katse ta ya ce, "yadda na baki dama ki ka faWi abinda yake ranki ki jira na gama." Ta sunkuyar da kai ?asa ya ce, "Mijin Yayarki da ni ko a sunayen mu muna da banbanci, halinsa daban da halina Jidda. Bani da saurin sabo kin fi kowa sani, ke kan ki sai a hankali muka saba har muka zo yanzu. Bazan iya canja kaina ba Jidda, bazan iya canja yadda Allah ya yi ni ba, amma ni nasan ina ?o?arin ganin na sake da kowa naki."

Ya sauke numfashi ya ce, "Zan koma yadda ki ke so Jidda, zan yi ?o?arin ganin na koma zaSinki saboda kar damuwar halayena su yi miki yawa. Tunda na sauke komai naje aka zauna dani Omar aka yi sulhu saboda ke da lafiyarki babu abinda bazan iya yi domin ki ba. In Allah ya amince babu abinda zai sake faruwa da zai saka ki yi danasanin aurena Jidda, zan yi ?o?ari na koma yadda ki ke bu?ata."

Nayla a sanyaye ta ce, "nifa bance maka ina danasanin aurenka ba, kawai yadda baka sakewa da familyna ne bana jin daWi."
"Yanzu ki ka ce ?anwarki tace baza ta zo gidan nan ta kwana ba saboda kar a cutar da ita, dole zaki ji haushin wannan maganar a zuciyarki, har zaki Warsa da ace bani kike aure ba da hakan bai faru ba."

"Ita tsoron haWe fuskarka take ji ba wani abun ba." Ya Wan yi murmushi calmly ya ce, "kin faWi abinda tace Win ba tare da kin san kin faWa ba. Wata?ila da bani kike aure ba da bata ce haka ba, kalmar tayi miki zafi shiyasa har kika furta min baki san kin faWa ba."

Nayla ta ce, "nidai ban yi danasanin aure ka ba, gwara ma ka daina faWa. Kawai yadda ka ke da familyna ne bana so, kuma na san haka halinka yake, bana jin daWi ne kawai." Yayi shiru bai ce komai ba, jin shirun sai ta kalle shi suka haWa ido ya Wan girgiza kai ya ce, "shiyasa nace ki yi ha?uri Jidda."

"Ni dai ban ce ina danasani ba."
"Nima ban ce kin ce ba, amma kalamanki da fuskarki sun nuna hakan. Kuma baki yi laifi ba, kin cancanci ki yi danasanin ne jidda. Meye abin alfahari a auren wanda aka yi ?o?arin kashe ki har sau biyu?." Nayla ta rufe masa baki da hannunta ta ce, "nidai ban ce ina danasani ba, ka daina faWar haka bana so." Ya Wan yi murmushi bai ce komai ba.

Ya sake kallonta yana cire hannunta daga bakinsa ya ce, "zanyi ?o?arin sakewa da kowa naki kamar yadda ki ke so, amma sai a hankali saboda bazan canja halittata ba, zan yi saboda na faranta miki rai har a daina cewa ana tsoron zuwa gidanki saboda ni. Tunda na har naje wani waje saboda ke, har naso furta kalma uku waWanda ban taSa faWa a waje ba saboda ke, duk da ban furta Win ba, amma da abin yayi tsamari zan furta Win saboda ke. Na sauke girman kai da zafin kai duk saboda ke da lafiyarki. A wannan gaSar na sake tabbatar ke Win rayuwata ce, bazan iya rayuwa babu ke ba, rayuwata in ba ke tamkar mutuwa ce. Ina jin rauni a raina in na tuna za a iya cutar da Didi ta dalilina, amma ban taSa shiga tashin hankalin da na shiga ba akan abinda ya faru dake...."

Ya ri?e hannunta wanda tabon ciwon da aka ji mata yake yana kallon tabon ya ce, "Ki cigaba da ha?uri dani, in sha Allah wannan danasanin da na gani a kwance a fuskarki zan mayar dashi alfahari a gare ki."

Nayla ta fara kuka ta ce, "ni ban taSa danasanin aurenka ba, ka daina faWa min haka bana so" ta faWa tana zubewa a jikinsa. Bayanta yake shafawa a hankali ya ce, "baza ki so ace ana tsoron zuwa gidan nan saboda ni ba, baza ki so ace ta silar mijinki anyi ?o?arin....." bata bari ya ?arasa ba ta haWe bakinsu waje Waya. Ta fara kissing Winsa slowly tana shafa bayan kansa idanunta a rufe.

Bata Wauki dogon lokaci ba hankali ta zare bakinta ta kalle shi suka haWa ido ta girgiza kai ta ce, "ka daina faWa min haka bana so, abinda yake raina shi na faWa maka ba dan ina danasanin aurenka ba. Wallahi Allah ban taSa danasani ba, alfahari nake yi dakai tun kafin ka kawo wannan matakin. Ka daina faWa min haka bana so, abinda nake so shi na faWa maka."

Ya sauke ajiyar zuciya yana ri?e da fuskarta ya ce, "shima abinda yake ran naki zan yi ?o?ari dan kawar miki dashi in Allah ya yarda."
"ni a yanzu ma kayi min komai, kawai naji haushi ne daka dinga fushi dan na fito na raka Yaya J" ta faWa da shagwaSa tana wasa da mallaSan gaban rigarsa. Ya Wan yi murmushi ya ce, "ba iya ganin ki a waje ba, ki ?ara harda rungume shi da kika yi, wallahi naji ciwo a nan" ya faWa yana Waukar hannunta ya Wora a side Win zuciyarsa.

Tayi dariya ta ce, "Rouhii ban taSa ganin mutum mai kishinka ba, yanzu harda Yaya J Win ma kishi ka ke yi?." Ya wrapping ?ugunta yana kallon ta ya ce, "sosai ma kuwa, dan kawai babu yadda zan yi ne Jidda, amma da babu wanda zai sake ri?e hannunki daga ni sai Abiy." Ta yi dariya sosai tana jan gashin fuskarsa ta ce, "na Wauka harda Abiy a cikin wanda ka ke kishin?." Ya wara idanu ya ce, "wane mutum." Kiss ta yiwa idanunsa ta ce, "to ka yi ha?uri." Ya Wan taSe baki ya ce, "ya zanyi miki? Nayi ha?urin."

"Nima bana so kowa ya ri?e hannunka Rouhii."
"shiyasa Wazu da Didi take shige min jiki na hanata, nace mata yin hakan kamar naci amanarki ne." Nayla ta ?yal?yale da dariya mai sauti wacce ta saka ya zuba mata idanu yana kallo cikin burgewa, haka yake so


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login